Showing 15001 words to 18000 words out of 180103 words

Chapter 6 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

17 Sep 2025

2443

Miya ne dayaji namomi.


Bansan ya akayi na dauki tukunyar Shinkafar na Dora na miyan akai nayi hanyar dakina dashi ba zubawa nayi niyyar Yi a plate Amma sai na tsinci kaina da daukewa gabadaya na kai d'aki lokacin idona ya rufe da yunwa ballantana nayi tunanin idan aka kamani fa


Ruwan da suka dura a Robobi dake cikin fridge na koma na dauki guda biyu Dan karfinn hali irin nawa har da d'aukar bredi guda biyu dake ajiye a kitchen din.


Ina shiga dakina na kulle d'akin tun kafin na zauna na fara dibar Shinkafar Ina kaiwa bakina ko zafin abincin banaji tsabar yunwar danakeji.


Ina cikin ci naji an fara buga min kofa Muryar Lami Dana Safiyya naji suna ta auna min zagi suna cemin Barauniya wlh idan na Bari suka shigo d'akin sai na lahira yafini Jin dadi ya zaayi su Gama Shan wahalar girki na sace abincin.

Ko kulasu banyi ba na cigaba da cin abincina nasan ban Isa na guje musu ba Dole sai sun dakeni ko naci ko banci ba gwara ma naci abincin.

Koda sun dakeni zasu dakeni da kwarina.

Da hannu bibiyu nake tusa abincin duk uban yajin dake cikin miyar dayasa nayita kwarewa yanda suke jijjiga k'ofar.kamar zasu b'alla ne yasa na dage na cigaba da auna abincin bakina da iya karfina ko taunawar kirki banayi.

Cak na tsayar da cin abincin danaji kukan Zahira muryar Saffiya na tashi cikin balai

"Wlh idan baki bud'e k'ofar Nan ba yau kwana zanyi Ina dukan Zahira da Nadiya sai sunyi kwana uku basu ci abinci ba.

Wani irin mik'ewa nayi cikin tashin hankali Jin Safiyya zata dakarmin yaran da nake tunanin su suka ragemin a rayuwata.

Aguje na nufi kofar na bud'e.

Ban karasa bud'ewa suka banko d'akin suka shiga Safiyya da Lami kuwa suka rufeni da mugun duka suna kaimin naushi ko ta ina nidai durkushewa kawai nayi inata Kare cikin jikina Sabida Kar su kawo min duka sai hakuri nake basu.

Lami da nake tunanin sai ma tafi Umma mugunta idan ta samu waje naji ta harba min kafarta cikina.

Take na saki wani irin ihun azaba na wargaje a kasa.

Nadeeya da Zahira kuwa ihu kawai suke suna kuka suna rike Lami da Safiyya Nadeeya da k'ok'ari har da kankame Lami ta Kai Mata cizo a kafa.

Take Lami ta bar kaimin dukan ta dau Nadeeya tayi cili da ita.

Ihun da Nadeeya ta saki yasani mik'ewa tare da manta azabar danake ciki.

Safiyya dake ta kaimin duka na wawuro na damfara ta da kasa a zuciye

Ko a mafarki akace min xan iya karfin dagata sama karyatawa zanyi


Lami ma dake neman Kara kamoni na wawuro tukunyar Shinkafar da har lokacin da Saura na hau kwada mata akanta Ina ihun kuka.

Sosai idona ya rufe sabida tab'a min 'ya da sukayi.

Sai da Safiyya ta fusge tukunyar nayi wajen Nadeeya aguje da jini ke ta zubar Mata Sabida kanta daya fashe.

Bansan tashin hankali Hawa Hawa bane sai ranar duk dukan da sukamin nemansa nayi na rasa sabida tashin hankali ganin jinin dake zuba a Kan Nadeeya.


Ihu kawai nake Ina sun kashemin 'ya da hannu bibiyu na d'aga Nadeeya nayi waje Ina ihun a taimakamin.

Ina fita Naga wani Dan taxi nace ya taimakamin ya kaini asibiti 'yata zata mutu.

Tun Bai gama tsayawa ba na bud'e k'ofar na afka ciki Nadeeya rungume Dani Ina ta kuka jinin dake zuba Akan ta ba karamin girgiza ni yayi ba.

Asibitin da muke zuwa na Kai Nadeeya Mai taxi kuwa ganin halin da nake ciki yasa Bai tsaya amsar kudinsa ba yayi tafiyarsa.


Da yake nurses da likitocin sun sani sosai Sabida haihuwar Nadeeya Dana Zahira duk a asibitin nayi Kuma Naseer na musu alheri sosai Sabida bashida rowa har gida suna zuwa dubamu idan Wani bashida lafiya.

Da Sauri suka karbi Nadeeya suna tambayata Mai ya sameta.

Ko magana ban iya Yi ba in Banda ku taimaka.min danake ta cewa.

Wani daki aka Kai Nadeeya suka hanani shiga.

Minti talatin din danayi Ina jiran fitowarsu sai Dana ga kamar awa talatin ne duk na matsu su fito Naga lafiyar 'yata.

Fitowar Likitan yasa nufeshi da Sauri Ina tambayarsa jikin 'yata

Sai Dana ga yana ta k'ok'arin fusge hannunsa daga ruk'on danayi Masa nasan Ashe ma hannunsa na ruk'o sabida tashin hankali.

K'ofar d'akin ya bud'e min ya Nuno min Nadeeya da sukayi wa dinki akai da ke ta sharar bacci ya bani hakuri akan Kar nashiga sabida Kar na tasheta.

Sai sannu yakemin sabida cikina dayayi turtsetse a gaba yace na samu waje na huta.

Ban iya zama ba Haka nake ta Kai kawo ko nauyin cikina banaji har sai Dana tuna Ashe banyi Sallah Laasar ba kafin na nemi buta na daura alwala Allah daya taimakeni da hijabi a jikina Dama ban cire ba.


Kebabben waje na samu nayi Sallah duk ba nutse ba sai Dana iddar da sallahn na fashe da wani irin kuka danake taso nayi tun dazu yak'i zuwa Sosai na jika gaban hijab Dina da hawaye Ina tunanin halin Danake ciki Sabida kawai abinci kannen mijina suka rufeni da duka Haka har abin ya shafi 'yata su fasa mata Kai.

Sosai nake kudirtawa Raina guduwa daga asibitin Amma Zahira Dana tuno yasa na Kara fashewa da Kukan Dan bazan iya guduwa na barta ba da da ita na fito da wlh babu abinda zai maidani gidan.

Gani nake babu Wanda ya Kai Su Umma rashin Imani gani nake babu Wanda ya Kai Su mugunta da rashin tausayi.

Bansan Magriba tayi ba sai da naji wata nurse ta tsugunna a gabana Tana bani hakuri akan na bar kukan Haka komai yayi tsanani maganinsa Allah.

Bansan ya akayi na kwanta a Jikinta na riketa Gam Ina cigaba da kuka ba so nake na fada Mata halin da nake ciki ko Yaya ne Amma tsabar kukan danayi maganar tawa taki fitowa sai sheshek'a nake.

Dak'yar ta kwace jikinta daga nawa idonta itama da hawaye tacemin nayi hakuri ga mijinta can yazo daukarta ta Gama duty dinta.

Ji nake kamar na bita aguje Dana hango tausayina a idonta kamar na riketa Gam na hanata tafiya sabida kawai ta taimaka min.

Nadeeya data fad'omin yasa na mik'e da Sauri nayi wajen d'akin da aka kwantar da ita.

Ina bud'e k'ofar tana bud'e idonta.

Da Sauri na ka rasa gadon na jawota jikina na rungume Ina fashewa da wani sabon kukan

Sosai nake tausayin kaina Dana yayana.

Ummata kawai nake kira da Abbana.

Wata nurse ce ta shigo ta bani hakuri tace zamu iya tafiya Dan Naseer ke biyan kudin asibitin ta bani ledar magani.

Kalmar xamu iya tafiya data ce ne yasa na Kara fashewa da kuka na tsani gidan Nan inama da Zahira na fito wlh Tallahi babu abinda zai maidani gidanan na gwammace na gudu da yayana.

Nurse din kuwa Tsaki tayimin tayi tafiyar ta Tana Jin Haushin yanda nake ta kuka akan 'yata taji ciwo ita Kam batasan kukan da nake ba.

Duk da nauyin cikina ahaka na kunce dankwalina na goya Nadeeya muka d'au hanya a lokacin dare yayi.

Ba fita nake ba ballantana nasan ko ina a yanzu ma bansan hanyar komawa gida ba.

Tafiya kawai nakeyi Ina tunanin inama mota tazo ta bi ta Kaina da Nadeeya mu mutu itama Zahiran ta mutu mu huta.

Sai danayi ta zagaye kafin na gane hanyar gidan da sai Dana balain gajiya.

Ina zuwa kofar gidan na kunto Nadeeya dake bacci na kwantar da ita a kasa Ina fargabar kwankwasa k'ofar Gidan

Ciki kuwa Umma ta cika tayi fam tana jiran dawowata Dan Bata Nan mukayi fada da su Saffiya tana dawowa suka Gaya Mata Kan lami data gani a kumbure ne kawai ke tafasa zuciyarta sosai takeji lokaci yayi da zata saka Yaya matanta a kungiya ko Dan irin abinda ya faru Allah Allah kawai take taga ta Inda zan shigo Dama idan ranta ya b'ace yake shigar bak'akken Kaya takeyi.

Naseer kansa daya dawo gidan sai daya San yau Mahaifiyarsa ba daidai take ba hakane yasa daya shiga dakinsa ya kulle Dan Haka kawai yau bayajin dadin Jikinsa Yana so ya tambayi Zahira da Nadeeya Yana Jin tsoron tambaya Kar yayi laifi.


K'ofar kawai Hajara ta zubawa Ido tana kallon Naeema datayi zaman dirshen a k'ofar Gidan tana tsoron kwankwasa wa.

Hajara kallonta kawai take Tana tunanin matakin daya Dace ta d'auka akanta Wata biyu ya rage wa Naeema Dan sun Gama tsara abinsu kamar idan tazo haihuwane ta mutu Amma mutuwar tata sune sila a da batayi niyyar kashe Naeema ba taso su rabu Salin Alin data haifi Zahira Amma sabida taurin Kan Naeema shine tayi mata gardama, taki tafiye tana ta Mata haife haife ita Nan Mai wayo baa ja da ita Amma Naeema ta ja da ita gani take Dole Naeema akwai abinda ta dogara dashi shiyasa take tsallake duk abinda tayi Mata.

A yau Naeema ta Mata abinda takejin kamar tun a daren yau ta rabata da ranta.


Ahaka ta zubawa kofar ido Bata motsa ba.

Naeema itama Bata kwankwansa ba sabida tsoro har karfe dayan dare Naeema na waje ta kasa kwankwasawa Sabida masifar tsoro.

Haushin karnuka ne yasa na jawo Nadeeya jikina na fara kwankwasa k'ofar a hankali tun inayi a hankali da Sauri na fara bubugawa Sabida tsananin tsoro ga wani irin Kara da nakeji.

Da iya karfina na fara buga gidan Ina waige waige ai kuwa waigawar da zanyi Naga wani irin bakin mage ya zuromin ido.

Wani irin razanann Kara na saki na fara kwalawa Umma Kira Dasu Safiyya tsabar tsoro har da Naseer na hau Kira.

Ina jijjiga k'ofar.

Karar buga k'ofar ne yasa Naseer da bacci ya fara dauka akan Sallaya mikewa da Sauri tare da yin waje.

Wani irin fad'uwa gabansa yayi a lokacin dayaji muryar da yaso tuna na waye Amma ya kasa tuna Mai muryar sai kiransa take Tana yazo ya taimaka Mata.

Gadan gadan ya nufi kofa.

Hajara ta Dago manyan idonta ta watsa Masa shi kuwa Naseer ya tsaya cak Yana Dan addua a Ransa a idonsa sai yaga kamar ba Hajaran ba wata hallita ce zaune Mai ban tsoro.

Da hannu ta nuna Masa d'akin shi kuwa ya juya da Sauri ya koma d'akinsa.

Hajara kuwa ta mik'e ta nufi kofar tana bud'ewa Naeema ta fado jikinta sabida tsananin tsoron Magen daya nufota Yana Dab da Isa wajenta taji an bud'e k'ofar.

Wani irin kallo Hajara ta hau Mata Naeema kuwa ta sunkuyar dakai ta na bata hakuri idonta a rufe Gam Sabida tsoron Hajaran


Ji nayi kawai ta finciki hannuna tayi dakina Dani.

Muna shiga ta watsar Dani tana hucci ni kuwa na rungume Nadiya gam jikina na rawa addua kawai nake a raina.

Umma ta Dade tana kallona kafin naji ta juya ta fita tare da bankomin k'ofar.

Dan yanda ranta ya b'aci ba a iya duka zata tsaya ba sai ta raba Naeema da ranta sai dai lokacin yin hakan baiyi ba.

Ni kuwa Tana fita na shige bandakina da Sauri na daura alwala Nazo na tada sallah Dan nasan bazan iya bacci ba har yanzu Ina hango katon bakin magen Nan a idona.

Ina Kan Sallaya bacci ya daukeni bansani ba.


Naseer kuwa Yana shiga d'akin ya rik'e kansa Gam Sabida mugun ciwon da yake masa muryar Naeema kawai yake ji a kansa tana kwalla Masa Kira sosai yake so ya tuno Mai muryar matsawa.kansa da yayi da San tunawa ya haddasa Masa mugun ciwon kai.

Shi kansa yasan ba daidai yake ba ya rasa Mai ke damunsa ya Dade a Haka kafin bacci ya d'auke shi batare da.yasani ba



*Mafarki*

Naseer akwai aiki a gabanka idan baka dage da Addu'a ba
bacci Bai ganka ba Naseer ka tashi ka gana da mahallicinka ka ware murya ka fara karatun Qurani a gidanan matarka na bukatar taimakon ka.

Murya kawai Naseer Yaji Bai San Wanda ke Masa magana ba da sallati ya tashi mafarkin na sake dawo Masa kamar a gaske.

Da Sauri ya mik'e ya shiga bandaki ya d'aura alwala yazo yayi kyakyawan Sallah raka'a biyu Yana iddarwa ya jawo Qurani ya Ware muryarsa ya fara karanta Ali Imran dayake dare ne take muryar sa ta karade ko'ina.

Hajara dake zaune a d'akinta tana ayyana mugayen abubuwa kuwa ta mik'e zumbur tayi waje da saurin ta jikinta na d'aukar zafi..........
8/19/21, 10:30 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*



*Page 7*



Salon da Naseer ya b'ullo dashi na karatun dare ba karamin dagawa Hajara hankali yayi ba Dan Naseer tunda yayi wanan mafarkin ya zage damtse wajen kusantar Allah.

Sosai ya fara Dan jin canji a jikinsa duk da har lokacin ya kasa tuna Naeema Sabida ba karamin aiki sukayi a kansa ba.

Koda aikin da sukayi Masa ya dauko hanyar warwarewa daya ci abincin da Hajara ke tilasta Masa yaci daya Sha barbaden magani sai aikin ya cigaba da tasiri akansa

Hajara da Yan kungiyanta sosai hankalinsu ya tashi da yanda Naseer ke neman zame musu barazana Dan Ta Kai Hajara Bata iya kwanan gidan Sabida kwana da yake Yana karatu Wanda idan tsautsayi yasa ta kwana a gidan komai na iya faruwa babann tashin hankalinta Bai wuce Kar aikin data Masa na manta Naeema ya wargaje ba.

Bata da burin daya wuce har ta Gama da Naeema Kar Naseer ya dawo hankalinsa.

Sanin idan Hajara ta b'ata Rai Naseer Kan shiga tashin hankali Dan sosai yake Mata biyayya Kuma bai San b'acin ranta.

Magani Shugabarsu ta Bata Wanda zata na zubawa Naseer abinci a ciki da indai ya Kai abincin bakinsa toh duk jikinsa zai mutu bazai iya aiwatar da komai ba Daga Nan ma bacci Mai nauyine zaiyi awon gaba dashi.

Da Wanan salon suka samu Naseer ya daina karatun daren Dan Da farko da Hajara ta bashi abincin dage mata yayi da ya koshi duk da yana tunanin Hajara bazata iya cutar dashi ba Amma abincin da take bashi zuciyarsa Bai kwanta da abincin ba shi ba yaro bane Dan abinda yake gani a abincin da taste din abincin na nunawa Abu aka saka a abincin.


Har a lokacin ya kasa tuna Naeema Amma idan zai kalli Zahira da ba Inda ta baro Mahaifiyarta sai yaji Yana San tuno Naeema Inda Yana matsawa kansa da tunanin kansa zai hau ciwo.


Naeema


Tun da mukayi rigama dasu Safiyya babu Wanda ya Kara kallon Inda nake da Umma Wanda hakan ya balain bani mamaki Dan na d'auka washegari Umma zata sakosu a gaba su nada min duka ga mamakina babu Wanda ya kalli ma d'akin da nake da farko a tsorace nake Ina tunanin bazasu shareni a banza ba kila akwai wani mugun abinda suke San kulla min.

Hakane yasa na dage da Addu'a Ina gayawa Allah Dan zuwa yanzu da cikina yake neman shiga wata goma Sha daya na balain fara tsorata da haihuwar da banyi ba har yanzu gashi cikin nawa ya Kara tsini ya koma kasan marrata.

Abinda ya Kara bani mamaki Bai wuce yanda Aka bar Zahira da Nadeeya suke zuwa wajena har suke kwana ba.

Kwana biyar da rigimata dasu na fito daga d'akina Sabida yunwar daya koroni dama bredin Dana d'auko daga kitchen nake ta cancanawa Ina ci da ruwa dazu na cinye ragowar yanzu kuma naji Ina Jin yunwa da biyu na fito sabida na ga ko su Umma zasumin masifa kamar yanda suka Saba Dan Ni tun sanina dasu tsawa da hantara ne a tsakaninmu sai rankwashi da duka.

Hannuna rike Dana Nadeeya data mak'alemin tunda Lami ta fasa.mata Kai muka fito Ina Dan Jin fad'uwar gaba.

Duk suna zaune a Palo suna kallon Indian film Nagi

Fitowa ta yasa Umma ta juyo ta zubamin Ido Ni kuwa jikina ya hau rawa Dan tun lokacin Dana dawo ta saka wanan bakar doguwar rigar bamu kara haduwa ba sai yanzu.

Tsintar kaina nayi da nufar wajenta.

Ina zuwa na zub'e a gabanta Akan gwiwata na hau hawaye.

Bata cemin kalla ba in Banda wani irin kallo da take Bina dashi tana jifana da wani irin murmushi daya saukarmin da wani irin tsoro da fad'uwar gaba


Hajara kuwa kallon gawa kawai take wa Naeema Dan a yanda suka tsara Naeema saura Mata sattika biyu ko.uku ta bar duniya abinda basu sani ba shine ran Naeema ba ahannunsu yake ba a hannun Allah yake.

Cikin kukan da bansan d'annewa nake ba na rik'e kafar Umma na fara magana Ina "Umma Dan girman Allah ki Yi hakuri ki yafemin idan laifi na miki Umma banida kowa sai ku ke nake wa kallon iyayena da suka ragemin Umma Mahaifina da Mahaifiyata sun tafi sun barni yayana shima ya tafi ya barni banida kowa sai ke sai Naseer da yarana Umma idan Wani Abu nake yi da bakiso Dan Allah ki gayamin wlh xan daina wlh bazan sake ba Umma duk abinda Kika Sakani zan Miki Umma Dan Allah ki rik'eni tamkar su aunty Safiyya insha Allahu zan bauta Miki na miki biyaya kamar yanda nake yiwa iyayena Umma ki taimakamin Dan girman Allah wlh banida kowa sai Allah sai ku"


Kasa cigaba nayi da Magana sabida kukan dayaci karfina na rik'e kafar Umma Gam Ina cigaba da kuka abinda bansani ba Umma ita Bata San wani Abu tausayi ba ballantana tasan yanda yake tsugunnawan da nayi agabanta Ina rokonta ita hararo gawata take a kwance Sabida tsananin Tsanar da tamin.

Irin ruk'on dana yiwa kafarta Yasa ta janye kafarta ta Dago hab'ata ta zuramin Ido cikin wani irin murmushi da idan tamin gabana ke tsinkewa banga alamar alheri a Fuskarta ba sai Sharri.

"Bakimin komai ba Naeema bana sanki ne kawai Sabida San danaga d'ana na miki da har ya kasa b'oyuwa Naeema tun Kafin ki haifo wanan er Taki Mai zubin Aljannu na baki shawara da idan kin haihu ki saka Naseer ya sakeki wata itama tazo taci rabonta Kika k'i Naeema Kika min taurin Kai Kika ja Dani
ba abinda ban miki ba Dan ki rabu dashi Kika k'i Kika sake haihuwa alamar akwai abinda kika tak'a Dan Haka nayi abinda zanyi ke gaki D'ana tare aka haifoku duniya bazaki iya rayuwa idan babu shi ba nayi abinda zanyi to nayi abinda zanyi Naeema ki haihu nagani ki tashi ki bani guri yanzu Zaki iya duk abinda ranki keso bazan hanaki ba Dan na d'an

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login