Showing 9001 words to 12000 words out of 180103 words

Chapter 4 - NAGA TAKAINA COMPLET BOOK by Sadnaf.txt

Sadnaf   

18 Sep 2025

702



"Abba bazai min karya ba duk da ban tashi nasan wacece mahaifiyata ba ni akaran kaina nasan itace mahaifiyata Amma wane irin Abubuwa nake gani haka ta yaya Mahaifina da yake Shahararren mallami zai auri wacce ake zargin matsafiyya ce ko Mayya Astagafurullah Mahaifiyata ba Mayya bace ba matsafiyya bace insha Allahu Ina dai tunanin tana da fad'a.

Naseer duk ke maganar a zuciyarsa.

"Karka manta Naseer Allah Kan fitar da matacce a cikin Rayyaye ya fitar da Rayayye a cikin matacce Ka yarda da zancen Mahaifinka ka dage da Addu'a.

Maganar Hajara ne ya dawo dashi tunaninsa

"A Ina zaku Zauna Kai da matar taka"?


"Zamu zauna a garin Jos ne Umma anan na siyi fili har na Gama gini"

"Toh ban yarda ka zauna a Jos ba kaji ko ban yarda ka zauna da Dan iskan abokin babanka da ya d'aukemin Kai ko fuskarka ba'a Bari nagani ba ka Kara ma mu'ammalla dashi Naseer sai na tsine maka daga Yau ba Kai babu shi Dan babu yanda zanyi ne Dana ce har mahaifinka ban yarda ka cigaba da mu'ammalla dashi ba
Ban yarda ka ringa b'oyemin komai ba da yanzu a gabana ka girma da duk bazaka zama wani susu su haka ba"

Naseer rusunawa yayi a gabanta cikin tashin hankali Yana "Umma Abba fa shi ya Raine ni ya rik'eni tamkar Dan daya Haifa a cikinsa Dan Allah Mai yasa kike so ki rabamu Dan Allah kiyi hakuri nasan anyi Miki laifi Bai Dace a rabamu ba tun Ina jariri Dole zakiji ba dadi Amma Dan Allah kiyi hakuri Umma wannan matakin da kike San d'auka a kaina yayi tsauri Umma"


"Toh sai dai ka zab'a ko Ni ko shi Naseer idan Kuma ka zabe shi Banga abinda zai Hana nayita tsine maka ba daga yau babu Kai babu shi ko Jos d'in ma bana so ka Kara zuwa zamanka a wajensa ba alheri bane a gareni sai Sharri"


Sosai Hajara ta ringa bambamin fad'a har tana neman yiwa Naseer baki.

Shi kuwa Naseer sosai hankalinsa ya tashi Sosai da rabashi da Hajaran ke neman Yi da Mallam Hassan Wanda ya Masa abinda ko Mahaifinsa Bai Masa ba tun daya taso ya fara wayo ya fuskanci irin Kaunar da Mallam Hassan ke Masa ba k'aramin jajircewa Mallam Hassan yayi a kansa ba ko Sana'ar da ya farayi da kudin Mallam Hassan ya fara kafin Mallam Ibrahim ya turo Masa kudi ya Kara Jari Taya Sama ta Ka shekara da shekaru da suke tare ace lokaci guda mahaifiyarsa tace su rabu har tana barazanar tsine Masa.

Tunda ya taso Abu bai tab'a d'aga Masa hankali kamar yanda rabuwa da Mallam Hassan ya d'aga Masa hankali ba hakane yasa ya dage ya cigaba da rokar Hajara ita kuwa ta cigaba da Shan alwashin tsine Masa matsawar Bai bi umarninta ba.

Kiran Sallah ne yasa Shi mik'ewa ya fita waje ya d'aura alwala ya nufi Massallaci yayi Sallah azahar.

Yanda zuciyarsa ta cunkushe da tashin hankali yasa ya d'auki Qurani daya gani a Massallacin ya fara karatu ahankali yaji ya fara samun nutsuwa a Massallacin yayi zamansa har akayi Sallar ishai Dan Bai San Mai yasa yaji yafi samun nutsuwa da iska Mai dadi a Massallacin akan gidan Hajara ba.


Hajara kuwa sosai hankalin ta ya tashi da yanda taga Naseer nada ruk'o da addini Dan taga alamar bazata iya mallake shi yanda take so ba duk da wani Abun zai iya tasiri akansa Amma zai na sakin shi nan da Nan sosai tayi ta tsinewa Mallam Hassan da Ibrahim Dan har yan kungiyar sun so tab'a Mallam Hassan Wacce taje Masa a Siffar Mujiya ya watso Mata ruwan rubutu Wanda ya k'ona Mata Rabin Fuskarta Sosai shugubarsu ta fusata suka Kara d'aura damaran ganin Bayan Mallam Hassan da suka lura idan basuyi da gaske ba zai iya cin Galaba Akansu Dan a tsaye yake sosai duk jifan da suka masa baya kama shi da alamar shima Naseer din kusan hakan ne


Hakane yasa Shugabarsu Hajaran ta cewa Hajara lailai ta raba Naseer da Mallam Hassan.

Wani Abu suka bawa Hajaran akan ta dafawa Naseer abinci dashi indai yaci zasu Dan ci Galaba akansa wajen Mallakeshi.

Sai dai har ta Gama girkin Bai shigo ba har dare yayi.

Naseer kuwa har Sha biyun dare Yana Massallacin har zai bar Massallacin Kuma ya koma ya zauna daya ga wasu su biyu sun shigo da alamar kwana zasuyi suna karatu aikuwa tuni ya koma ya zauna ya shiga cikinsu suka kwana suna Karatu Sabida biyan bukatar gabansa yasa ya tashi da azumi.


Sai washegari ya koma gidan Hajaran data cika tayi Fam Dan duk yanda taso ganin Inda yake ta cikin mudubi,Bata samu ganinsa ba illa haske kawai data ke gani anan ta Kara sanin Naseer ya karantu akwai Kuma dafai a jikinsa.

Dak'yar ta amsa gaisuwar sa ta hau surfa Masa Balai shi kuwa yayi ta Bata hakuri sai data Gama Dan kanta tace ga abincinsa Nan ya tashi ci.

Wani irin kallo ta watsa masa lokacin da yace
Mata azumi yake.

A takaice duk yanda Naseer yaso shawo Kan Hajara abin yaci tura ahaka ya Mata Sallama ya taho Modobi zuciyarsa a cunkushe Dan ta rantse Masa idan Bai rabu da Mallam Hassan ba sai ta tsine Masa ta Kuma ranste bazai zauna a Jos ba yaje ya siyar da gidan ya dawo Calabar yayi gini su zauna.


Allah yayi wa Mallam Hassan baiwa sosai na gane Abubuwa Wanda har idan wani mummunan Abu na neman far'uwa dashi Allah Kan nuna Masa a mafarki shi Kuma sai ya dage da Addu'a idan ma abin zai faru zai zo Masa cikin sauki ya Dade da sanin irin harin da Hajara take kawo masa hakane yasa yaci damarar Kare kansa ko tafiyar da Naseer yayi da mahaifiyarsa sai daya dage da Addu'a cikin Mafarki Allah ya nuna Masa komai ya Kuma Godewa Allah.

Hakan yasa yak'i komawa Jos ya zauna zaman Jiran dawowar Naseer Dan ya Kara Masa wasu adduoi.

Naseer kuwa a lokacin daya iso kasa magana yayi da Mallam Hassan Yana Jin kamar lokacin Hajara ke rantsuwar Yi Masa baki indai ya Kara kulashi sosai kirjinsa ya Masa wani irin Nauyi ya hau zubar da hawaye Bai San maanar tashin hankali ba sai daya ga Hajara na neman rabashi da Wani b'ari na jikinsa.

Murmushi Mallam Hassan yayi a lokacin da yaga idon Naseer ya kad'a yayi Ja ya sunkuyar da kansa ya kasa Bari su had'a ido.


Mallam Ibrahim kuwa wani irin ajiyar zuciya ya sauke da yaga Naseer ya dawo ba abinda ya same shi.


"Karka damu na Riga da nasan Komai D'ana Ni nasan zatayi haka Dan Bata da makiyin daya wuceni Uwa ba Wasa bace kabi Umarninta Dan Allah sai dayace kabi Uwa sau uku kafin a ambaci Uba Abu daya zan Gaya maka karka sake da Addu'a ka dage da Addu'a dan Mahaifiyarka shu'uma ce ta gaske ta wuce tunaninka Sabida Kai yasa nak'i bud'e Mata wuta Amma da yanzu an shafe labarinta ita a tunanin ta idan ta rabamu shine zata iya cin Galaba a kanka tun kana jariri ban barka haka ba Naseer sai Dana Dage maka da Addu'a Kuma Alhamdulillah gashi ka girma cikin kariyar Allah a yanzu ne zaka fara fuskantar kalubale a rayuwarka domin Mahaifiyarka itace kaddararka duk lalacewa dai mahaifiyace Amma addu'a na iya canza komai idan rabbi ya sota da Shiriya zata shiryu kafin lokaci ya Kure kayi Mata biyayya ba zan fasa maka adduar dake daga mata hankali ba Kai yanzu ba yaro bane tunda baifi saura makwani ka Rayya Sunnar Ma'aiki ba Naseer ba kanka kawai zaka dagewa da Addu'a ba ka fara saka matar da zaka Aura a addua domin rayuwata itama Tana cikin hatsari karka tab'a kwanciya babu alwala Naseer daga Kai har iyalinka a yau da ba Hajara ce ta haifeka ba ace wani daban ta Haifa wlh Tallahi sai na kawo karshen tsafinsu Allah ya Kan Arawa bawa Dama yayi ta shagalinsa Wala Ala a gaba ko zai gane abinda yake Yi ba daidai bane ya gyara kafin lokaci ya Kure maka Amma Hajara ta Riga da tayi nisa ba Kuma ta Jin Kira Allah ya shiryeta ya ganar da ita gaskiya Bata isa tayimin komai ba sai dai idan Allah ya kaddara ta silarta zan tafi dawowar ka kawai nake jira Dama da tuni na tafi Amma duk da haka a yanzu zan d'au hanya Allah ya kareka da karewarsa ya baka ikon cinye wanan jarrabawa."


Daga haka Mallam Hassan ya mik'e ya jawo jakar kayansa Naseer kuwa duk dauriyarsa a matsayinsa na d'a namiji sai da ya fara zubar da hawaye kamar mace Yana kallon Mallam Hassan ya fice daga d'akin Mallam Ibrahim na rokarsa ya kwana gobe ya dau hanya ya dage sai ya tafi.

Motarsu Bata tashi ba sai wajen karfe biyar na yamma


Yan kungiyarsu Hajara kuwa Suna kallon komai ta cikin Mudubi hakane yasa Motarsu na d'aukar hanya duk suka rikid'e suka koma siffar Mujiya suka tashi lokaci guda kusan su dari.

Mallam Hassan kuwa tunda ya hau motar ya rufe Ido Yana tayiwa Annabi Sallati Bai ankara ba yaji an driver yataka wani irin birki Sakamakon Mujiyoyin da suka cike gaban glass din motar Wanda hakan yasa driver ya daina ganin gabansa har ya Kai shi da buga wani katon dutse dake Gefen hanya Motar ta kife.


A takaice mutane biyu ne suka Rayu a Hatsarin Motar ahaka Mallam Hassan ya amsa Kiran Allah Inda sai da Mallam Ibrahim da Naseer suka yi kwana uku a asibiti Sabida yanda mutuwar Mallam Hassan ya gigitasu.


(Allah ya jikanka Baba Ibrahim Allah yasa Aljanna ce makomarka a gaske akayi hatsari ya Kuma rasun Inda da yawa ake zargin yan kungiya ne suka haddasa Hatsarin Sabida biyu daga wayanda basu mutu ba suka bada labarin yanda Mujiyoyi suka rufe gaban motarsu Allah ya tsare Mana imaninmu Ameen)


Har Mallam Hassan ya samu sati biyu da rasuwa Naseer bai dawo daidai ba haka Mallam Ibrahim Dan tunda akayi rasuwar yake kwance ya Kuma daina magana.

Dak'yar Yan uwa da abokanan arzkiki suka samu rarrashi Naseer ya fara dawowa daidai Yana yiwa Mallam Hassan addua da yake ganin kamar zaa tashe shi ace mafarki yake ba mutuwa yayi ba Ashe duk maganar da yake Masa a ranar na bankwana ne daya sani ya rakashi daya Sani ya tashi ya rungumeshi kafin ya tafi.


Hajara kuwa sosai sukayi kwana bakwai a daji suna abubuwa na murnar Mutuwar Hassan Dan Dama shine ya zame musu karfen k'afa.


A takaice bayan Sati uku da rasuwar Mallam Hassan aka daura Auren Naeema da Naseer ba'ayi komai ba bayan daurin Auren Dan har a lokacin Naseer ba wani dawowa daidai yayi ba San ma dayake yiwa Naeema da San mallakarta ne yasa ma yake Dan samun relief.

Kamar yanda Hajara ta tsara ya nemi gida a Calabar haka ya samu karamin gida ya siya gidansa na Jos kuma ya zuba 'yan haya.


Hajara duk da gidan karami ne daki biyu da Palo sai kitchen da toilet gani take gidan yayi wa Naeema girma ita kadai

Sosai idanta ke Kan komai da Naseer zaiyi naira Hamsin ma da Naseer ya biya Sadaki a wancan lokacin sai data nemi ya rage Dan Naira Ashirin shine highest din kudi a time din dak'yar ya samu ta barshi ya bada naira Hamsin din.

Naseer Sanin darajar uwa da masifar dake tare da Bijirewa uwa yasa yake balain yi Mata biyayya ba Kuma yasan tayi fushi dashi zuwa Lokacin ya fuskanci Rashin ilimn da basudashi gabadaya a Kuma iya saninsa baiga Hajara ta tab'a sallah ba balle Kannensa.

Wani zubin yakan so ya gasgata Abinda ake zarginta dashi Amma kyakyawar zuciyarsa sai ya ringa zata Mata zato Mai kyau.


Sai da akayi Sati da Daurin auren Naeema da Naseer ta tare bayan Mahaifinta Lawan ya damka amanar Naeema a hannunsa ya kuma rok'esa daya riketa Amana Bata da kowa sai shi tunda sunyi nisa da juna zasu ringa aikawa Juna wasika ta Fax suna sanin halin da suke ciki.


Mahaifiyarta da tun b'atan Aliyu Bata Kara samun cikakken lafiya ba itama sai datayi kukan rabuwa da Naeema Dan har ga Allah bataso Naeema tayi Mata Nisa haka ba taso Aurenta tayi a garin ko a kusa da garin Kar abin ya.mata yawa duka yaranta biyu babu Wanda take gani addua kawai tayi musu itama ta roki Naseer daya rike Mata amanar Naeema kamar bazasu rabu ba aka fito da Naeema dake Jin kamar ta hakura da auren Naseer tana fitowa ta fara k'ewan Iyayenta.


Makotan arzikine suka Rakata har Calabar Lawan Kuma yace idan an kwana biyu zai saka shima a rakashi ya gano Inda suke zaune.

Wayanda suka raka Naeema washegari da suka kaita suka juyo bayan ya Naseer ya musu goma sha Tara ta arzki shima a b'oye Sabida Kar Hajara ta gani tayi Magana.

Sosai yake dokin kasancewa da Naeema Sabida tsananin San da yake.


Gida uku ne tsakanin gidan Hajara da gidan Naseer din

Hakane yasa Dan Abubuwan daya siyo ya siya guda biyu ya fara shiga wajen Hajara Dan ya Mata sai da safe.

A palon ya tarar da ita a zaune ta Sha dogon Jar Riga har kasa ta rambada kwalli Tana ta karkada kafa Fuskarta a had'e gefenta Kuma Mijinta ne.tijnani ya sada Kai kasa kamar Mai neman yafiya.

Wani irin tausayinsa ne ya rufe Naseer wanda hakan yasa Naseer danne nauyin Hajaran da yake ji bayan sun gaisa da Hajaran dake Masa wani irin kallo tana mamakin shakkarta da ta ga Naseer ba yayi idan tayi shigar dake saka hantar mutane kad'awa ko had'a ido baa iya Yi da ita intayi Shigar meeting d'insu.

"Umma Miji shugaba ne a wajen matarsa sai mace tabi mijinta take samun Aljanna Umma bana jin dadin yanda nake ganin Baba bana Jin dadin yanda yake neman maidaki shugabarsa Umma Dan Allah banyi magana Dan na b'ata Miki Rai ba bana San ki shiga fushin ubangiji"




"Kaiiiiiii dakata wa'azi zakamin har ka Isa kazo ka tsaya a gabana kana gayamin abinda ya dace da Wanda Bai Dace ba Ni Hajara baayi Wanda zan bishi ba daga yau karka Kara tarata da magana irin wanan wlh ranka zaiyi mumunan b'aci duk abinda zanyi idone naka kawai Kuma daga yau karka Kara tilastawa yayana suyi Sallah ai kowa na da raayinsa ko karka zo ka cusa musu abinda basuyi niyya ba ka dai ji na Gaya maka wanan ledojin daka shigo dasu na menene"?

Naseer dak'yar ya hadiye yawu sabida b'acin Rai dayaga yanda baba Tijjani jikinsa ke balain rawa da Hajara ke magana


"Kayan marmarine da kaza na siyo shine nace Bari na fara kawo miki kafin na wuce gida"

Karbe ledojin tayi gabadaya ta d'auko iya ledar Ayaba da lemon ta mik'a Masa tana "Zaka iya tafiya Kazar Kuma zan bawa kannenka suci ai Suma suna bukata"

Naseer baice komai ba ya karbi ledar ya mik'e ya Mata sai da safe.


Yana fita ta dakawa Baba Tijjani tsawa Akan ya tashi ya Bata wuri.

Waje yayi a rude Inda ya tarar da Naseer ya zubawa waje daya ido da ledar lemonsa a hannu.

Baba Tijjani baice Masa komai ba ya wuce shi Naseer ya fara binsa a baya.

Sai da suka jere ya fara magana Yana "Ka dage da Addu'a Allah ya kawo maka mafita kayi hakuri da tambayar da zan maka kana Sallah kuwa"


"Ada inayi kafin na aurota sai Dana aurota ta ce Kar na sake Mata sallah a gida.

Wani irin nauyi yaji a kirjinsa ya zubawa baba Tijjani Ido da duk ya firgice

"Ka ringa sallah a boye kana gayawa Allah Yana jinka Yana Kuma sane dakai zai kawo maka mafita"

Sosai.Naseer ya bashi shawarwarin da take baba Tijjani ya fara aiki dashi yayi alwala ya shiga wani Massallacin daya gani a bud'e.


Naseer kuwa Yana Isa gida yajasu sallah shi kadai ya Sha lemonsa da Ayaba Dan mutanen da akwai azabar kunya Tama k'i bari su had'a ido balle ta saki jiki ta Sha lemon.

Shi kuwa ko a jikinsa Dan yasan kunya ke dawainiya da ita.

Daren farko yakan zama Daren tarihi ga maurata karfe goma.sha daya Naseer yayi Shirin kwanciya Yana cikin yiwa Naeema magana yaji an fara buga k'ofar gidan a haukace.


Mamakine ya rufeshi ya zura jallabiyarsa ya fito Yana "waye"?

Tara da bud'e k'ofar sakin baki yayi a lokacin dayaga Safiyya da Lami da uban Kaya

"Lafiya kuwa"?

"Eee Umma ce tace muzo mu Taya Naeema kwana idan an kwana biyu sai mu koma.

Daga haka suka shige gidan suka bar Naseer da sakaken baki a bud'e.


A takaice amarcin da Naseer baiyi cikin dadin Rai ba kenan dan Safiyya da Lami sosai suka sa musu Ido duk abinda akayi idonsu na Kai sai Kuma sun kaiwa Hajara rahota.

Naeema kuwa ko kad'an Bata tab'a damuwa ba Dan tana da balain hakuri idan kuwa Naseer ya fita ya d'an siyowa Naeema Abu tofa an shiga uku Dan sai sun gayawa Hajara ita Kuma sai ta Masa tas kamar ta dakeshi.......
8/19/21, 10:30 PM - My Mtn Number: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸


®? *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_



*Free Novel*


*Page 5*


Naeema sosai take tsoron Safiyya da Lami Dan sun girme Mata indai Naseer baya Nan sai dai tayi ta zaman d'aki.

Ahaka ma bata tsira ba haka zasuyi daidai a Palo suna zuba mulki tunda suka lura Bata da wayyo ga Kuma yarinta ga balain tsoro da take dashi.

Da tsoron da take dashi suke tak'ata yanda sukeso Bata tab'a d'aga Kai ta kallesu ba ballantana ta Kai kararsu wajen Naseer da zamansu Safiyya a gidansa yafi k'ona Masa Rai irin rayuwar daya so Shimfid'awa da Naeema idan ya Aureta ba irinshi yakeyi ba Dan Su Saffiya ma ba wani shak'arsa suke ba idan yaso tsawatar musu ma yasan Ransa sai ya b'aci.

Hajara kuwa ko tari Naeema tayi a gidan sai su Saffiya sun bata labari


Naseer ma in zaiyi kwanciyar Aure da Naeema a b'oye shima hankali ba a kwance ba Sabida fargabar su Saffiya na iya fad'o musu d'aki sosai Naseer ya takura da irin zaman da su Safiyya ke Masa a gida hakane yasa wani dabara ya fad'o Masa ranar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login