Showing 1 words to 3000 words out of 148334 words

Chapter 1 - SO KO ABOTA BOOK COMPLETE BY Maman Nurool-Huda.doc

27 Sep 2025

2855

??ࡱ?>?? ?
????????????? ?
?
? ?
?
?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
? 

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F?
WordDocument????1?0Table?????????Data
???????????????????? P?(?KSKS?1??`
???????rrWWWW';?l? 4W??????????$'??*rWW??WWWW??;?;?;??W; ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJTA`????TDefault Paragraph FontOJPJQJ^Jfi`????f Table Normal :V ?4?
l4?a? OJPJQJ^J(k`????(No List ?`
?x/?U6t??T????v?r?N?&??"ZNt????????2????.?+@?Z:h?{V?.So ko abota[6/23, 1:08 PM] +234 703 129 7709: =?D?=?D?=?D?=?D?=?D?=?D?
*SO KO ABOTA*
=؋?=؋?=؋?=؋?=؋?=؋?
By maman noorul
Hudah

Ina yiwa dukan masoyana barka da sallah Allah ya maimaita Mana,Ina bawa fans dina hakuri Wanda Suka kirani ban samu na d'auka ba,da Wanda Suka min magana ba reply Ina godiya da kaunar ku,Allah ya biya,godiya ga special group Dina Wanda Suka yarda Dani Suka bani kudin su nagode kwarai

Wanan littafi na kudi ne d'ari uku ga Mai bukata zai tura naira d'ari uku ta wanan asusun banki Aisha Mohammed
0092544083
Acess bank
Ko katin mtn,domin niman Karin bayanin a min magana ta wanan number via watsaap 09090112817 sai na ji ku


Bismillahir Rahmanir Rahim


Gidan alhaji zubairu

Misalin karfe 7:30 na dare

Zaune suke a saman taburma a tsakar gida kallo d'aya zaka musu kasan suna cikin farin ciki da kaunar juna,ga su dayawa domin Yan matan da samarin kawai sun Kai su ashirin Banda Yara kanana ga Kuma su anties matar su Yaya jafar su uku babban gida ne da ake zaman lafiya da kaunar juna sai dai abinda baza a rasa ba domin kunsan ance zo mu zauna Zo mu sab'a,Haka rayuwar ta gada

Ummi ce ta kalli zeenat tace"ke zeenat je kicin ki d'auko miyar a karawa baba"

Baba yayi murmushi yace"kamar kin San muna niman Kari "

Anty Jamila ta kwace maganar da cewa" ah'ah ummi bari rabi ta je kin San fa halin zeenat Bata da natsuwa yanzu sai ta zubda miyar muyi asara

Turo Baki zeenat tayi tana kunkuni tace"ni kullum sai ayi ta cewa bani da natsuwa toh ya ake son mutum yayi Kuma bada son Raina ai Nike b'arnan ba"

Anty Maryam tace"ai shiyasa ake son ki natsu in Zakiyi abu,

Yaya aminu yace"su zeenat kenan hajiya b'arnata ikon Allah gobe ko ya za ayi a wajen niman aikin oho"

Zaro Ido Yaya Mahmud yayi yace"Wai aiki zata je nima?"

Yaya jafar yace"Kana Ina baka da labari, ai tun last month tayi summiting credentials dinta a nagarta building company Kuma fa anyi shortlisting sunansu Kuma sunan hajiya b'arnata na ciki"

Zaro Ido Yaya Mahmud yayi yace"Kai haba?lallai sun Shiga uku kuwa in suka d'auke zeenat aiki domin ko sati bazatayi ba a company zata rusa building din"

Dariya duk suka kyalkyale dashi harda Yara kanana hakan yasa zeenat fashewa da kuka tana dire kafa

Appa ya daka musu tsawa yace"ku min shiru meyasa ku baku fadin alkhairi ne kuna b'atawa yariya rai a banza"

Inna tace"ka barni dasu wallahi sai na b'ata musu Rai kema takwara ki daina kulasu,in kina Yi musu kuka zasu cigaba da tsokanar ki ne"

Yaya aminu na dariya yace"kowa dai yasan bazata samu aikin Nan ba domin tana Shiga office din interview zata tarwatsar da wurin "duk sai suka kyalkyale da dariya

Appa yace"nidai na yarda da mamana Kuma zata Baku mamaki na bata dukka yarda ta zata samu aikin, mamana ki min alkawari Zaki natsu wanan karon ki basu mamaki,ki min alkawari ko....?"

Zeenat ta Kura me Ido Amma Bata amsa ba tana gudun d'aukan alkawari abubuwa su tab'arb'are a musu dariya

Baba yace"Sha Shasha ai bazata d'au alkawarin ba Dan tasan baza ta tsinana abin kirki ba shashasha mutum bazai natsu yayi abin kirki ba"

Inna tace"nagode da cin fuska bukar a gabana kake zaginta

Zeenat tace"Abba nayi maka alkawari wanan karon bazan baka kunya ba ta Kare da Shan ruwa

Mama tayi murmushi ta mike zata d'au tray sai anty Maryam ta had'an da nasu sai ta kwashi nasu jafar ta Kai ciki

Mama tace"Allah ya taimaka ya'ta

Duk suka kyalkyale da dariya anty Jamila harda shakewa sai Kuma aka cigaba da Hira har aka Kira sallah isha'i da yike a yanayin sai 8 tayi ake Kiran isha'i mazan suka tafi massalaci matan Kuma sukayi a gida suna idarwa aka had'an hannu wajen yin aiki gidan, Yan matan gidan suna gyran gida su anty Jamila na wanke-wanke cikin kankanin lokaci aka gyra gidan saf,domin Basu Bari wuri da dirty

Inna ta shige cikin d'ankinta

Zeenat ta zauna a babban falo tana kallon film,anty Maryam tace"zeenat ki tashi ki Shiga ciki ki kwanta saboda gobe ki tashi da wuri "

idon zeenat na Kan tv tace"ai yanzu Zan tashi ai "

Tace"babu wani tashin da zakiyi ni nasan halinki sai kikai 12 anan"

Su anty Jamila suka ce Wai meyasa kike b'ata lokacin ki a kanta bafa tashin zatayi ba kin sani "

Zeenat ta gyra kwanciya tace"ai na kusan tashi da an Gama film din nan Zan shige ciki

Anty Maryam tace"karma ki tashi Yar rainin wayau,

Kallon ko ta tsaya Yi a Bollywood har karfe d'anya bacci ya d'auketa a falo

Washe gari da misalin 6:40,Marin da anty Jamila ta Kai Mata a cinya shi ya tada daga bacci ta saki ihu

Cikin matsifa domin ita anty Jamila Bata da hakuri ko kad'an tace"Wai bazaki tashi mu had'an breakfast ba ko ba zaki je interview din ba"

Cikin magagin bacci tace"Dan Allah ki Bari in samu bacci jiya har 1am banyi bacci ba"

Anty farida tace"Kuna damun kanku ku kyaleta tayi baccin ai duk mu san ba aikin zata samu ba"

Aiko baccin ta koma sai 8:03 ta tashi,kallon agogon bango falon tayi ta zaro Ido ta mike

Haurawa tayi part dinsu ta tarar da har su halima sun tafi school wasu na barci tace"Yan gidan ban akwai mugunta maimakon su tashe ni shine suka barni nayi ta barcin asara salon in rasa aikin su min dariya Allah ya fisu wallahi

Tana Shiga ta watsa ruwa a gurguje ta fito ta zaro dogon riga ta saka sab'an rudewa maimakon ta d'au gyalen dogon riga sai kawai ta d'au d'ankwalim atamfa ba tare da ta lura ba,wata jakar ta d'auka ba Wanda ta saka credentials dinta jiya ba ta fita tana gudu su anty Maryam dake falo Suka kyalkyale da dariya Suna kiranta taki kulasu


Kallon juna sukayi anty Jamila tace"ko dai kanta be cika bane anyi yariya ba natsuwa ni Banga laifin Aliyu ba daya fasa aurenta"

Duk sukayi dariya anty Maryam tace"iskancine da kiwuyar matsifa yariya ba natsuwa"

Hmmmmm Mai karatu gidan alhaji zubairu kenan Mai kanti

(Wacece zeenat)

Maman nur
[6/23, 1:08 PM] +234 703 129 7709: =?D?=?D?=?D?=?D?=?D?=?D?
*SO KO ABOTA*
=؋?=؋?=؋?=؋?=؋?=؋?
By maman noorul
Hudah

Wanan littafi na kudi ne d'ari uku ga Mai bukata zai tura naira d'ari uku ta wanan asusun banki Aisha Mohammed
0092544083
Acess bank
Ko katin mtn,domin niman Karin bayanin a min magana ta wanan number via watsaap 09090112817


Bismillahir Rahmanir Rahim

Malam zubairu ya kasance mutumin kirki da sanin ya kamata. matar shi d'anya zeenatu da yaransu maza 3 Mata biyu ,appa shine babba watoh malam musa, sai Abba shine na biyu sunanshi Dauda, sai baba shine auta sunanshi Abubakar amma suna kiranshi bukar,shine mahaifin zeenat,sai matan akwai Fatima,sai autarsu bintu Wanda duk suna gidanjen mazajensu da ya'ya Duk sun manyata

A shekarun baya da Suka wuce Malam zubairu Yana da babban shago na provision shiyasa ake ce me mai kanti domin babban shago ne duk layin babu irin ta

Yayi kokarin ganin yaranshi sunyi karatu addini dana boko domin mutum ne Mai bawa karatu muhimmanci bashi da burin daya wuce ya gan ya'yansa sun had'an kansu shiyasa tun suna kanana yake nuna musu su kaunace juna haka ko suka taso cikin aminci da kaunar juna Basu da burin da ya wuce kamar su farantawa iyayensu

Inna ta kasance mace Mai yawan fad'an sai dai fa tana da kirki in ka fahimce ta zaku zauna lafiya

Dukkaninsu kasuwanci sukeyi appa Yana da Mata d'aya da Yara goma maza bakwai matar duk kanana ne domin su daga baya aka haifesu,jafar shine babba a gidan Yana da Mata da Yara hud'u sai Yusuf shi a Abuja yake aiki sai Kuma aminu,Jamil harun,abubukar, Abdulrazaq,sai azima Wanda Abdul ya Bata shekara goma Sha biyu sai bintu sai Maryam

Abba Kuma yaranshi tara duk maza ne guda biyar suna da Mata sauran biyun suna jami'a University of maiduguri

Baba Kuma yaranshi biyar zeenat itace babba Kuma duk gidan itace babba a Mata daga kanta aka fara haihuwa yara mata Khadija ke binta sai hafsat sai maza biyu, Kuma duk a gidan suke zaune da ya'ya da jikoki Yusuf ne kadai baya Zama suna Zama da matarshi a Abuja Amma duk su Yaya aminu da jafar da sauran yayunta a gidan suke Zama da matar su,abinda zai baka mamaki had'a girki ake a babban tukunya Kuma in za a ci shimfid'a za ayi su Abba had'an musu ake a tray d'aya,su ummi ma da mama da Kuma umma Suma a tray d'aya,Yara Mata a tray d'anya sai mazan ma haka matan su Yaya jafar Suma a tray d'aya ana ci ana raha ana Hira matan tsanye da hijabi,su anty Maryam da anty Jamila da anty hauwa duk suna Jin dadin zaman gidan domin gidan dadi ne dashi,dukda shimfid'a su abba Yana da dan nisa da su amma sai a had'e baki ana Hira cikin mutunta juna da girmamawa,Yan unguwan ma suna kwatance da gidan malam Mai kanti domin ya saita gidan kafin ya b'ata,domin yanzu baya gidan ya b'atta babu Wanda yasan inda yake shekaru ashirin da biyu da suka wuce randa aka haifi zeenat daga zuwa shago be Kara dawowa ba har yau ba labarin shi, tun suna jimami da Jin d'acin rashin sa har suka Fara bawa zuciyarsu hakuri,Inna ko har hawan jini ya kamata

Zeenatu ta samu gata ta ko Ina kasancewar su mama sun dade suna niman haihuwa ya' mace Amma Allah be basu ba sai ummi da aka auro daga baya ita ta haifeta,hakan yasa suka sarganta ta an mugun b'ata ta da shagwab'a Kar ma Inna ta ji labari ta mugun shagwab'a zeenat to the extend that ta taso Bata da confidence komai yi Mata akeyi,har jami'a da kowa ke Kai kanshi ita kaita akayi kamar dai tata,su baba Basu tab'a tunanin hakan Yana affecting dinta negatively ba kwata kwata Bata da natsuwa komai aka ce tayi sai ta b'ata shi domin da an sata aiki jikinta zai Fara rawa,bata maida hankali in zatayi abu ga shegen b'arnan tsiya shiyasa ma su Yaya jafar ke kiranta b'arnata so biyu ana sa bikinta ana fasawa domin samarin cewa suke bata da natsuwa,sai Nan gaba zaku gane wanene zeenatu da halayenta if you are meeting her for the first time zaka d'au irin half done din Nan ne>?#?but she is extremely beautiful and lovely in ka gane ta zaka San confidence ne kawai bata dash,sai dai fa akwai rashin kunya da rashin ji a b'oye,irin slow motion din Nan ne Wanda in sukayi abu zaka rantse ka ce Basu bane

Shekarunta ashirin da biyu,graduate ce,zeenat Fara ce sol son kowa kin Wanda ya rasa

_______________

Fita tayi tana gudu a titi kamar mahaukaciya sabon kamu, sai da tayi nisa ta fahimci ashe slippers ne a kafarta tace"oh no"sai dai fa babu halin komawa ta rigada tayi nisa

Keke ta tare tace me kamfanin nagarta zaka kaini na nan cikin gari

Yace"naira d'ari"

Tace"babu damuwa"Shiga tayi ya ja keke sai kamfanin,zeenatu ta fita tana kokarin bude zip din Jakarta kawai sai ta gan ashe ba jakar da ya kamata ta d'auko bashi ta d'auko ba,rike Kai tayi tace"na Shiga uku na lalace ni zeenat,me Keke yace"ke sallame ni intafi sauri Nike "

Zeenat tace"kayi hakuri malam wallahi Ashe ban taho da kudi....."

"Dakata malama Daman kin San baki da kudi Kika Shiga min Keke toh maza ki San inda zakiyi ki biya ni domin bazan d'auka wanan iskanci ba,daman ai irin ku ne masu Shiga Keke baku da kudi toh in kin Saba yiwa wasu ni bazaki min in kyale ki ba"
Idon zeenat yayi wuri-wuri jikinta har rawa yake tana kallon opposite dinta can tsallaken titi a wani karamin shago rike yake da table water me shagon ya mika me wani abu a karamin kwali Wanda Bata san ko miye ba "

Maganar su Yaya aminu ya fara mata kuwa a kwakwalwa na cewa"she is useless bazata iya aikata komai ba balle ta samu aiki"wani karfin guiwa ne ya Zo Mata ta kalli me Keke dake zuba matsifa tace"malam bari in shiga ka juya dani ta can lane din gaban shagon can "Bata jira cewar shi ba ta shige shiko sai zuba ruwan matsifa yake


Shiga uturn yayi domin Daman Bata da nisa da inda ya sauke ya samu wuri ya paka gaban shagon

Jikin zeenat na d'an b'ari ta karasa shagon dai-dai lokacin da Mai shagon ya miko me canji zeenat tayi saurin kwace kudin da Bata San ko nawa ba ta juya da gudu ta cire d'ari ta mikawa me adaidaita kudinshi

Me shagon ne ya fito Yana keeee b'arauniya Amma zeenat Bata tsaya ba saima Shiga titi da tayi da gudu sauran kad'an wani Mai Bajaj ya bigeta

Binta yayi da kallo tsana a ranshi yace"b'arauniya b'allagaza mace babu class sai gudu take a titi

Tana gama tsallakewa ta juya ta kalli shagon sukayi Ido hud'u dashi gwalo tame ta shige kamfanin tana addu'a a ranta na Allah ya Bata nasara gashi har 9 ya wuci


Tana Shiga hall din ta Gan mutane dayawa da alamu ma ba a Fara gudanar da interview din ba jikinta ne yayi sanyi ganin suna dayawa sosai tace"su Yaya zasu samu abin yimin tsiya in ban samu aiki nan ba dole ne ma in Samu aikin Nan by all means bana son Abba ya ji kunya

Wata budurwa dake kusa da ita tace"baiwar Allah ya kikayi dressing haka ne?Kuma aiki Kika zo nima ai sun fi son su gan mutum yayi looking smart

Zeenat ta sauke ajiyar zuciya tace"hmmm bazaki gane ba Yar uwa ni kadai nasan inda akayi na iso nan,har Yar fashin wucin gadi na zama"labarin komai zeenatu ta Bata tace"wallahi in har ban samu aiki nan ba toh fa bani da maraba da akuya a gidan mu domin dama Basu d'aukeni da muhimmanci ba balle kafin in zo har sun yanke bazan samu ba"

Sosai tasleem ke dariya wai hajiya b'arnata shima fa Wanda ke zaune kusa dasu sanda ya dara harda tafawa

Tasleem tace"toh Bari dai in gyra Miki d'ankwalin ya bada style amma fa da slippers Kika zo "
Ji sukayi yace"Wai toh ku miye tunanin ku na zuwa niman aiki Kuna Mata ku da komai yi muku za ayi ku bar maza mu samu"

Hararanshi taslem tayi tace"Dan muna Mata sai mu zauna mu shimfid'a kafa bazamu nimi na kanmu ba,ai duk macen da bata son namiji ya rainata wajibi ne ta tashi ta nimi na kanta domin yawan bani bani yana jawo sab'anin tsakanin ma'aurata

Yace"kenan Kuna nufin zaku bawa company Nan gudumawa kamar inda maza zasuyi?

Tasleem tace"ai ita Amana d'aya ce Wanda ya baka aiki tamkar Amana ya baka Kuma ya rufa maka asiri babu abinda zakayi ka biyashi illah ka rike me Amana da sirrin sa ka yime aiki iya karfin iyawar ka,ka barwa allah saura

Yace"hakane kefa?"

Lumshe Ido zeenat tayi ta bude,Wanda hakan dabi'ar ta ce tace"honestly ban San me zance ba amma nasan duk Wanda ya baka aiki ya baka hanyar cin abinci amma nasan zanyi komai iya karfina dan ganin nayi taking wanan kamfanin to great height zan zamanto bani da wani buri daya wuce in farantawa kamfani nan"

Murmushi yayi sai Suka gan yayi wurgi da file din hanunshi, ya mike,sai Suka gan wani daga bayanshi ya taso da wuri ya Fara saka me

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login