Showing 27001 words to 30000 words out of 146065 words
Chapter 10 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
ya tambayi Barde abinda ke faruwa.
Barde ya nisa yace " bansan nikaina takamaimai menene ba sai dai naganshi ya taho gunka sai kuma ya juya."
Cikin mamaki Mai Martaba yace " ban gane ba?"
Nan Barde ya sanar dashi abinda ya gani.
Hankalin Mai Martaba ne ya tashi sosai nan ya juya afusace yai bangaren d'an nasa.
Bai jira Zagi ya isar da zuwansa ba ya fada ciki da sauri.
D'akinsa ya nufa ya bud'e, a dukunkune ya ganshi cikin bargo, da sauri ya karasa gunsa ya d'agoshi.
Jikinsa zafi rau wanda hakan ya kara tadamai hankali, ya kalli Abu Turab wanda idanunsa sai lumshewa suke, yace " Menene? Waye ya tabaminkai? Har yajama zazzabi?"
Kai Abu turab ya girgiza alamar bakowa.
Fuskarsa yace " bayin dana aiko da kayanka sune suka baka yagagge ko akwai wani abun?"
Abu Turab jiyai wani kuka yazo mai, baisan sanda yasa kuka ba, kuka ya shigayi sosai.
Mai Martaba ya rungumeshi tsam a jikinsa hankalinsa a tashe.
Abu Turab ya dade yana kukan sannan ya share hawayensa cikin murya mai raunin gaske yace " kayi hakuri na tadama hankali daga zuwana."
D'ago dashi yai ya kalleshi yace " ni zan baka hakuri na rashin kula da abinda ke faruwa dakai."
Abu Turab ya share kwalla baice komai ba.
Yana zaune kusa dashi har bacci ya dauke d'an nasa sannan ya mike ya fito.
Bangaren Basira ya shiga, zaune ya ganta tana cin abinci.
Sai daya zauna sannan ya kalleta yace " Abu Turab yaci abinci ne?"
Murmushi tai tace "in bashida lafiya bayacin abinci dan ko yaci zai dawo dashi."
Ya kalleta ya kalli yanda takecin abinci yace " Basira mai ya sameshi? Ance ya sa kaya bayan rigar a yage."
Abincin hannunta ta ajiye dan dama ci kawai takeyi, ta kalleshi tace " bansan me ya faru ba nima na dai san bashida lafiya."
Ido ya kura mata, tai saurin kauda kanta gefe, yace " wanene yamai haka? Na tabbata kinsani."
Ta dan kalleshi kadan tace " shi bai fadama ba?"
Yace "yace bakowa."
Murmushi tai najin dadin yanda dan nata yace bakowa, tace " tunda yacema bakowa hakan ne, koma ba hakan bane alama ce ta bayasan kasani."
Shiru yai, sannan ya kalleta yace " komai yayi daidai? Na gida nake nufi."
Kai ta d'aga tace " komai yayi daidai sai dai inaso ka bani dama na wani abu."
. Ya kalleta bai ce komai ba.
Tacigaba da cewa " so nake Lantana ta koma gun Abu Turab sannan inaso ka taimaken akan barinta ita kadai ta kula dashi banasan abashi bayi dayawa."
Mamaki ya kamashi yace " me kike fada haka! D'an nawa da bashida lafiya kikeso invar lantana kadai ta kula dashi?"
Tace" rokon ka nake akan hakan inya tasa lokacin sai ta dawo nan, ya saba da ita da ita kadai yakejin dadin zama."
Shiru yai baice komai ba, ita kuwa tana tsoron kar a turamai mutane ya zama harda mutanen Magajiya kada kuma tsautsayi yasa ya nuna yana gani tunda dai yaro ne.
Ta kalleshi tace " sannan yana san karatun boko."
Mai Martaba yai murmushi yace " akwai mai koyama Abdulmajid da 'ya'yan kanina da na galadima karatu a cikin gida, inyaso sai ya dinga zuwa."
Tai murmushi tace " nagode Takawa."
Kallanta ya sakeyi yace "amma kina ganin zai iya karatu cikin yara masu gani shida yake makaho?"
Tace " zai iya, kuma hakan zaisa su fuskanci juna da 'yan uwansa."
Kai ya jinjina alamar gamsuwa.
********
Washegari.
Da gudu ta shigo bangaren Magajiya, tana zuwa cikin zumudi tace " Umma ina kanin Ya Abdulmajid d'in?"
Abdulmajid ya maka mata harara yace " khadija me yasa bakida hankali ne? Ba na hanaki yima mutane gudu ba? Kina mace?"
Baki ta murguda kadan sannan ta kalli Magajiya ta shagwabe fuska tana neman yin kuka.
Tace "Umma kinga Ya Abdulmajid ko?"
Abdulmajid haushi ya kara kamashi, yace "banace karki kara cemin Ya Abdulmajid ba?"
Kuka ta saka sosai, Magajiya ta janyota jikinta tana lalashi.
Abdulmajid ya kalli Magajiya yace "Umma duk ke kika b'ata yarinyarnan."
Khadija ta d'ago daga jikin magajiya tace "Umma ina kanin ya....."
Sai kuma tai shiru.
Magajiya tai dariya yace "Abdulmajid kadaina zafafa mata."
Itakam ganin anki fada mata yasa tai waje da sauri.
Baiwar bangaren Magajiya ta samu tace "kaini gun yaron dayazo jiya."
Nan ta dauketa tai bangaren Basira da ita.
Ta nuna mata bangaren yaron.
Da sauri tai ciki, Lantana ta gani a zaune tana ninke kaya, cikin zumudi tace " sannu, ina yayan da aka kawo jiya?"
Lantana ta mata kallan mamaki ganin bata santa ba.
Abu Turab ne ya fito daga d'aki bai kula da wani a gun ba yace " Lantana dan bani ruwa."
Jiyai anzo an rungumeshi kam.
A tsorace ya kalli kasansa.
Yarinya ce karama ya gani, cikin mamaki ya tureta yace " waye hakan?" ya fada kamar bai ganta ba.
Khadija tai dariya tace " nice nan 'yar gidan waziri, kaine yayan dayazo jiya ko?"
Kallanta yai kadan ya kauda kai yace " ni bansanki ba."
Dariya tai batace komai ba, itakam tun jiya ta matso ta ganshi.
Hannunsa ta kama tace "ai kai zaka dinga wasa dani ko? Bakaman ya Abdulmajid ba ko?"
Shiru yai baice mata komai ba, ta kara rike hannunsa tace " sunan ka Ya Turab ko?"
A hankali yace eh.
Dadi ya kamata tace " zanje gun karatu sai nazo gobe.
Nan tai waje da sauri.
Baisan sanda yadanyi murmushi ba.
Lantana ta kalleshi tana dariya tace " tunda kazo gidan nan sai yanzu naga fara'arka."
Ya kalleta yace " bani ruwa kishi nakeji."
Tai dariya ta mike, jikinsa ba karfi hakan yasa ya zauna.
**********
Jin labarin fara karatunsa agun Mai Martaba yasa Barde shima ya gurfana gaban Mai Martaba yace " Takawa nima inasan abani izini in dawo da yarinyata cikin gida dan daukar darasi."
Mai Martaba yace "ba da kace tanayi a waje ba?"
Barde yace " wlh Takawa yarinyar tawa ce kasan na fadama bataji sam, kullum ta fita makaranta sai an kawo kararta, ina ganin in anan take zatafi samun nutsuwa tunda ba wanda ta isa tsokana ganin darajar mutanen da zatai karatun dasu."
Mai Martaba yadan murmusa yace " shikenan ka kawota, Mairo sunanta ko?"
Barde yace "eh Takawa, ina godiya Allah yaja kwana."
*********
*ⓐⓑⓤ ⓣⓤⓡⓐⓑ ⓣⓔⓐⓜ*🤝🏼
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🤸🏼*
*19*
Da yamma suka shirya ita da d'anta dan zuwa gaida Magajiya.
Duk inda sukai kallansu ake ana 'yan gulmace gulmace har suka isa b'angaren Magajiya.
Tana kilisarta itada d'anta, bayan an neman musu izini nan suka shiga,ta kama hannun Abu Turab sakamakon sakeshi da Lantana tai da zasi shiga.
Abu Turab ya sauke idansa akan hamshakiyar matar dake zaune ta kafe kofar da sazu shigo da ido.
Kallanta yai sannan ya kalli d'an nata dake gefe sai kuma yai kasa dakai.
Magajiya kam ta kafeshi da ido tunda suka shigo har suka isa suka zauna.
Ta rasa me yasa tana ganinshi taji gabanta yayi wani wawan fad'uwa, Basira ta kalla sai dai yanzu taga alamar ba tsoro da gidadanci a idanunta kamar waccan zuwan nata na da.
Zama sukai,Magajiya ta kara kallan yaron a ranta tace " sak Mai Martaba lalai naji dadi da Yakumbo ta taimaka wajen nakasa idan nan."
Gaisheta Basira tai, i
Bata amsa ba ta maida idanta gun yaron, ya d'ago suka hada ido da sauri ya kalli gefe yace "Barka da Yamma."
Tabbas tasan sun hada ido sai dai dayake zuciyarta na farin ciki da kasancewarsa makaho yasa ta kasa dogon nazari akan haka.
Abdulmajid kam ya had'e rai da alama bashida niyyar gaida Basira.
Sai da Magajiya tace "Yarima baka gansu bane?"
"Barka."
Abinda ya fada ma Basira kenan.
Murmushi tai ta kalli Abu Turab tace " Yarima bakaga yayanka bane?"
Wannan kalma ta ba Magajiya da Abdulmajid mamaki, yarima? Haryaushe yazo?kuma ma a gabansu?"
Abi Turab bai kalleshi ba yace "Barkanka dai Yarima."
Magajiya zatai magana, Basira tai saurin cewa " haba Abu Turab sai kace ba yayanka ba? Ai kai basai ka kirashi Yarima ba ko Magajiya?"
Ta karasa maganar tana kallan Magajiya.
Magajiya ta juya ido a ranta tace " lalai wai so kike ki nunamin kin kile ko me?"
Murmushi ta saki sannan tace " hakane abinda kika fada sai dai kinsan tsintaciyar mage bata mage."
Basira cikin mamaki tace "bangane ba?"
Magajiya tai wani nishi na kasaita tace " Dafatan muhallinku an sa komai da komai? Dan ina nan ina fama da al'amuran cikin gida ban samu naje ba."
Basira ta daure tace " komai yayi."
Shiru suka d'anyi Magajiya na kallan yaran, can tace " naji ance ka fita riga a yage jiya? Meke faruwa? Ko dayake laifinki ne kinsan yaran makaho ne bai kamata ki barshi shi kadai ba."
Basira ta kalleta kadan batai magana ba,BU turab yai saurin cewa " Laifinane dan batasan ma nafita ba."
Magajiya a hasale tace " kada ka kuskura in inamagana da mahaifiyarka kasamin baki, ko kaga Abdulmajid na haka? Wannan alama kake nunawa na kataso a wani gun daba Gidan sarauta ba."
Basira ta kalleshi tace " kada ka sake, sannan yi maza ka bata hakuri."
Shiru Abu Turab yai wanda hakan yasa Basira tai dana sanin cewa ya bada hakuri, tasan halin d'anta sarai inhar tace yai abu ya tsuke baki to fa lalai bazaiyi ba.
Magajiya ta kalleshi tana jiran ya bata hakuri sai dai jitai yayi gum.
Abdulmajid ya kalleshi yace "bakaji me aka ceba?cewa akai ka bada hakuri."
Abu Turab aya dan juyar dakai saitin Abdulmajid yace " bansan laifin me nai ba."
Wannan kalma tasa ta basu mamaki sosai, a zuciye Abdulmajid yace "bakasan me kai ba? To me ya damemu? Kayi laifi dan haka bada hakuri ya zama dole."
Kasa ya maida kansa yai shiru, Basira tadan tabo hannunshi nan ma shiru, Magajiya tai wata dariya kadan ta takaici tace " kai? Nice magajiya gimbiyar sarki, sannan nice a matsayin mahaifiyarka babba dole ne kabi abinda nakeso ka kuma guji abinda banaso."
Abu Turab baiyi magana ba, Basira ta kwallama lantana kira tace " Lantana samo bulala."
Lantana ta kalli Uban gidan nata cikin tausayawa sai dai ya zatayi? Haka ta fita ta samu bulala na bishiyar maina.
Basira ta kalleshi yace mike, Abu Turab ba musu ya mike, ya d'aga kasan wandonsa dan yasa nan zata daka, zata fara dukansa Magajiya tace " Basira meye hakan?
Dan d'ana yamin laifi ai hakkinane in hukuntashi bake ba."
Basira ta tsaya sai dai a ranta tana addu'a Allah yasa kar tace ita zata hukuntashi.
Magajiya ta kalli Abu Turab tace "yi zamanka kaji d'ana." tai maganar fuskarta a sake.
Gani tai Abu Turab yaki komawa ya zauna, kallan mamaki tamai gani tai kansa na kasa kusa da mahaifiyarsa.
Ya saba da hakan inyai laifi sai tace dakanta ya zauna.
Basira ta kalleshi tace " zauna mana." nan ya koma ya zauna, ba shakka wannan abun ya kuna ran Magajiya ya kuma kona ran d'anta, sai dai bata nuna ba har suka tafi, tana tunanin lalai dole ta saita d'an nan.
**********
Yau satinsu biyu a gidan, sam Abu Turab baya fita saboda gudun kar wani abu ya faru a gane idansa na gani, sam bayasan gidan, sai dai jefi jefi Khadija na zuwa gunsa tai tamai zuba, shi mamakinsa ma ko mahaifinsa baya gani dan tun daga wannan ranar bai sake sashi a ido ba.
Yau ce ranar dazai fara zuwa makaranta da safe yai wanka yasa kaya, Lantana ta kawomai abinci yaci sannan suka fita, Basira ta mai fada sosai kafin su wuce makarantar.
Sun kusa isa makarantar sukaji ance Lantana, nan ta juya jin muryar kawarta.
Kallan Abu Turab tai tace " dan Allah bari in mata magana."
Murmushi yai yace " jeki, ba can bane?"
Tace nan ne.
Sandarsa yasa a gaba ya fara tafiya yana d'an kale kale kadan kadan.
Yaje zai shiga yaji an bangajeshi dakarfi wanda sai daya sashi ya fad'i.
Hannunsa ya kalla yaga ya kurje, ya d'ago dan ganin waye, sai dai ga mamakinsa gani yai ta mike tana neman kara mai.
Hannu yasa da karfi ya fizgota.
Mairo ta juyo suka had'a ido, da sauri ya kauda kansa wato yarinyar nan ce ta rannan?
Itama ido ta kuramai tace "la kaine makahon nan ko?"
Abu Turab yace " meyasa bakida hankali? Bakiga bigeni kikai ba? Kike neman gudu baki ban hakuri ba?"
Dariya tazo mata ta toshe baki, jakar buhun dake hannunta wanda ya rike gam ta zare ta rike da hannunta, yana kallanta a ransa yace " wannan ba karamar fitinaniya bace."
Waige waige ta shiga yi nan taga khadija ta nufosu.
Alama ta mata da hannu akan tayi sauri, itakam ganin yayanta ne agun yasa takara sa sauri, tana zuwa kusa dagun zatai magana Mairo ta mata alama datai shiru.
Mamaki ya kamata ta karaso, alama ta mata da hannu akan ta rike mata jakarta, nan khadija ta rike tana san ganin me zatai.
Duk wannan abun da suke Abu Turab na kallansu shi dariya ma abin yake bashi lalai yarinta da ciwo, inba haka ba ko baya gani tana san tacemai bazai fahimci me takeyi ba?
Khadija na amsa ta shige ciki da gudu.
Da kallo ta bita, can tace " Ya Turab haka zamuyi ta zama anan?"
Murmushi yama Khadija yace "cilar da jakar ki shiga muje."
Nan ta yarda jakar sukai ciki.
Suna shiga suka zauna gu d'aya dayake lokacin da ne, akan tabirma suka zauna, can gefe kuma Abdulmajid ne zaune akan wata daduma mai kyau ya hard'e kafafu.
Khadija na zaune kusa da Abu Turab.
Mairo tazo ta baya ta tab'ata tace " jakata fa?"
Tace tana waje.
Waje kuma?yarmin kikai?
Khadija tace eh yayane yace in yar.
Baki ta murgud'ama Abu Turab tace "yayan naki da ba gani yake ba?"
Abu Turab ya kalli inda Khadija take, Mairo ta kalleshi tace " ni anya baka gani kuwa?"
Abu Turab ya juya kansa bai tanka ta ba, ta harareshi tare da murgud'a baki ta mike tai waje.
*********
Sosai yaji dadin yanda yake fahimtar karatun, dan daga anyi tambaya sai yaga yasan amsar, sai dai ba damar ya fada indai ba tambayarsa akai ba, saboda umarnine na mahaifiyarsa.
Abdulmajid in yaji ya bada amsa daidai sai yai dariya a ransa yace duk kokarinka dai baka isa yin rubutu ba saboda rashin ido, yana tsananin jin haushi yanda Khadija ke zama inda yake, sam ma tadaina kulashi iyakacinta dashi gaisuwa.
Wata shakuwa mai karfi ce ta shiga tsakanin Khadija da Abu Turab ko makaranta zata ita take zuwa ta rike hannunsa su tafi, in an tashi kuma sai ta rakashi sannan take tafiya.
Mairo kuwa da Abu Turab banda fada ba abinda ke had'asu, rigimarta tayi yawa da sam ko kusa dashi bayasan tazo, haka kawai indai taganshi azaune sai ta tsokaneshi.
Abdulmajid kam na tsananin kishin Abu Turab ganin yanda ko Mahaifinsu ke nuna mai kulawa da kuma yanda mutane ke sanshi, yasa san ya tsaneshi farincikinsa yaga yamai sharri, sai dai duk sharrin da yakemai cikin ikon Allah sai komai ya warware.
_Wannan kenan_
Haka rayuwa ta kasance musu sosai Abu Turab ke kokarin ganin ba wanda yasan yana gani, sannan baya shiga gun mutane saboda tsaro, Mahaifiyarsa tana kara tarbiyantar dashi da nunamai abinda ya dace da wanda bai dace ba.
Baya zuwa gun Magajiya akai akai, sannan in yaje gaisheta ma yana zuwa yake cewa zai tafi in kuwa ta hanashi tahowa haka zai zauna gum, sosai ya fahimci matar fuska biyu gareta.
Haka ya taso cikin tarbiyya mai tsauri, haka ya taso cikin sanin halayen mutanen gidan, ya kuma fahimci lalai mahaifiyarsa gata tamai, ko daga yanda mutane suke mai kallan tsana sun dauka baya gani, sharrin da ake mai da kuma nuna halin ko in kula akansa.
Mutum d'ayace yake zama da ita yaji dadi, daga mahaifiyarsa da Lantana sai kuwa Khadija.
*TEAM ABU TURAB🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*_Gaisuwa Gareki Fatity, Meela Adeel, Rasheeda, Zaliha, Safeena, wannan shafin sadaukarwace gareku._*
*20*
Ganin irin tsananin shakuwar da ta shiga tsakanin Turab da Khadija yasa hankalin Magajiya ya fara tashi, ga yanda take tsananin san yarinyar, Hisham tasa aka kira ta umarceshi akan ya maida Khadija kano gun 'yan uwan mahaifiyarta, a lokacin Khadija nada shekara 10, sai tazo gidan sau nawa amma ko b'angaren Magajiya wani sa'in harta fita bazata ba, Hisham ma ya aminta da hakan dan kuwa shikansa abin ya fara damunsa jin komai a gida zancenta kenan Ya Turab.
A ranar da za'a tafi da ita ma tazo gun yayan nata tana ta sashi magana, dan dama kaf gidan ita kadai ce mai sashi yai ta magana, suna cikin hirarsu aka turo tazo Mamanta na nemanta, mikewa tai cikin sauri dan ko d'ankwalinta bata d'aura ba kawai ta sa hijab dinta ta fita, hartaje kofa Turab yace " Khadija."
Juyowa tai cikin fara'a, murmushi ya mata ya kalleta yace " karfa kiyi gudu ki tafi a hankali kije ki dawo."
Itama