Showing 75001 words to 78000 words out of 146065 words
Chapter 26 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
ji? Idan har ba so kakeyi rayuwarta ta shiga cikin kunci ba kai gaggawar janye maganar nan."
Yace " indai har a kusa dani zatai kuncin nikam banajin zai damen."
Kallansa tai cikin tsananin mamaki tace " Abdulmajid."
Kasa yai da kansa kawai baice komai ba.
Khadija ce tai sallama bata jira ba ta shigo da sauri ciki.
Magajiya ta kalleta, gaban Abdulmajid tazo ta tsuguna tace " yaya yanzun nan Umma ta aikoni in kawo sako naji ana zancen kana san auran Mairo, Yaya Meke faruwa?"
Kansa ya kawar gefe, hawaye ne ya fara zubo mata ta shiga girgiza kai tana cewa " yaya please kabar maganarnan, Mairo itace Ya Turab yake so ta yaya zaku zama kune sanadiyyar kuntata masa rayuwa, na sani ba santa kakeyi ba, in har ni bazan zauna kusa dashi ba dan Allah yaya kabar ta ta zauna gun Ya Turab......."
Kuka ne yaci karfin ta mamaki ne karara ya bayyana a idanun su duka su biyun, Magajiya ta juyo tace " Turab ne yake san wa? Mairo?"
Khadija kuka kawai takeyi tanacewa "Dan Allah yaya ka janye maganarnan."
Abdulmajid ya buga mata wani harara yace " Khadija kina nufin saboda farincikin Turab kinaso ni in kuntata? Farincikinsa ya fiye miki?"
Kallansa tai tana girgiza kai tace " ba haka bane yaya, inka duba rayuwarsa zakaga abin tausayi ne shi, yaushe ya fara gani? Sannan waye gareshi a kusa dashi?"
Jitai an fincikota a tsorace ta d'ago Mahaifinta ta gani, Magajiya na tsaya tana mamakin abinda takeji.
Hisham yace " Akan wa kike kuka?"
Kallansa tai sai dai batace komai ba, cikin fad'a ya kara cewa " Waccan karan ma akansa kike kuka? Akansa kika daina magana? Akansa ne kike neman ture auran Saifullahi?"
Hawaye ne kawai ke zubo mata sai kai kawai da take girgizawa.
Hannu ya d'aga kamar zai daketa sai kuma ya fasa, ya kalleta cikin takaici yace " Kin bani kunya Khadija......"
"Ya isa hakanan, Khadija wuce ki shiga cikin d'akina maganar ta isa haka." Magajiya tai maganar cikin kakkausar murya.
Khadija a hankali ta shiga ciki jikinta duk yai sanyi, Hisham kam bakin ciki yasa ko motsi ya kasa, yana bala'in san yarinyar.
Magajiya ta kalli Hisham da Abdulmajid tace " ku bani guri zan nemeku anjima."
Nan kowa ya mike.
Zama tai tare da had'e hannayenta guri d'aya ta matse su tai shiru.
" Turab nasan Mairo?
Abdulmajid na san Mairo?
Sannan Khadija nasan Turab?" Dolene ta fito da hanyar dazaisa komai ya warwarw mata.
***********
Mairo ta fito daga wanka tana shafa mai, mahaifiyarta ta shigo tace " kiyi sauri kisa kaya mahaifinki na nemanki."
Nan ta zura bakar doguwar riga bayan ta gama kintsawa.
Mayafin rigar ta yana a kanta ta fito zuwa falonsa.
A zaune ta ganshi yayi shiru, jin sallamarta ne yasa ya dawo daga tunanin dayake yi.
Zama tai sannan ta kara gaidashi.
Kallanta yai, idanunsa duk sun canza yace " Mairo, Abdulmajid ya sanar ma Sarki yana san auranki."
Idanunta ta zaro cikin tsananin tashin hankali tace " aure? Ni da shi?"
Barde ya kakaro murmushi yace " Kinfi kowa sanin kuma ban isa bijirewa umarnin sarki ba."
Ya mike yai cikin d'aki, da alama ya shiga ne dan kar yaji tausayin 'yar tasa.
Mairo tai shiru a zaune dan tama rasa ta inda zata fara.
Mikewa naga tayi da sauri ta zura takalminta tayi waje.
Tafiya take zuwa gidan Sarki, tana tafe tana cewa " Ya Turab ya zanyi? Menene mafita?"
Tunda ta shigo gidan ake gulmarta.
B'angarensa ta nufa a waje taga Garzali, da sauri tace " Ya Turab fa?"
Garzali yace " Yana kano."
Taku biyu tai zuwa baya dan ji tai kamar an kwad'a mata abu, cikin rikicewa ta nufi b'angaren Basira.
A zaune ta ganta tana shan fura ita kanta yau bata samu cin abinciba sai yanzu da yamman nan.
Basira tana ganinta tausayinta ya kamata, Mairo ta karaso da sauri ta zube gabanta tace " Umma ki taimaken."
Basira ta kalleta cikin tsananin kulawa tace " Mairo."
Mairo idanunta suka ciciko tace " ba sona yake ba, Umma haka ake so? Ta karfi? Umma kinsan halayen mutumin nan, ni na hakura da Ya Turab dan da alama dama naso kaina dayawa ne, Umma amma ba Abdulmajid ba, dan Allah Umma ki tai......."
Idanu ta runtse dan ji take kamar ta kwalla kara na bakin ciki.
Basira ta matso da ita ta rungumeta tana lallashinta, kuka sosai Mairo takeyi tana cewa " Umma ba Abdulmajid dan Allah, naji aban kowanenen amma bandashi."
***************
A can garin kano kuwa bayan sun dawo a kofar shiga Mai Martaba ya kalli Turab yace " Inka koma wannan karan kasa a turo domin sa rana dan ba'asan masarauta da jan magana ba."
Turab yace " Godiya nake Mai Martaba."
Bayan mai tuka motar yai parking, wani bafade ne yazo da gudu ya bud'e sannan ya rad'a mai magana a kunne."
Murmushi naga yayi sannan ya kalli Abu Turab yace " Turab muje kaima kwa gaisa da Minister."
Abu Turab ya kalleshi sai dai baiyi magana ba yabi bayansa.
Wani bangare aka kaisu, bangaren ya tsaru sosai wasu maza ne guda biyu a zaune kana ganinsu kaga uba da d'a duba da yanayin kamar su.
Suna ganin Mai Martaba suka mike, uban na ta murmushin jin dadi.
Sarki ma cikin fara'a ya kalleshi yace "Malam Haruna yau kaine da kanka?"
Wanda ya kira da Haruna ya karaso suka gaisa, yace " Tuba nake Ranka ya dade da alama fishi ake dani."
Zama Sarki yai sannan suka kara gaisawa.
Yaran nasa ne ya matso ya gaisheshi.
Shima Abu Turab ya gaida mutum.
Haruna ya kalli Sarki yace " Ga d'ana Saifullahi, kullum ina cewa zan kawoshi ya gaidakai sai yau Allah yai."
Saifullahi ya kara gaidashi.
Sarki yace " naji dadi, ni kuma wannan sirikina ne."
Mamaki ya kama Haruna ya kara kallan Turab.
Sarki yace " d'an Sarkin Zazzau ne, Abu Turab."
Fara'a ce ta kara bayana a fuskar Haruna, Saifullahi ya kalli Abu Turab."
Haruna ya kalli Turab yace " Kace na ganka kai tun yanzu kafin mu had'a zuri'a."
Turab yamai kallan mamaki da rashin fahimta.
Haruna ya kalli sarki yace " ai Saifullahi shine zai auri yar gidan Waziri sunanta Khadija."
Wani mugun fad'uwa gabasa yai da sauri ya d'ago ya kalli Saifullahi, wanda shima kallansa yakeyi.
Idanu suka kafema juna.
Sarki shikam bai kula dasu ba ya kalli Haruna yace " lalai Minister na tayaka murna Allah ya sanya alkairi."
Yanayin kallan da Abu Turab yakema Saif yasa Saifullahi yace " Lafiya?"
Turab yai saurin kauda kai yace " ba komai."
Kallan mamaki Saif ya bishi dashi, dan ya kasa fahimtar ma'anar kallan da yake mai.
🤝🏻 *TEAM ABU TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*50*
Mikewa Turab yai ya kalli Mai Martaba sannan yai kasa da Kansas yace " bari na baku guri." Ya fad'a kansa na kasa.
Sarki ya jinjina kai yana murmusawa yace " To Turab kaje ka huta."
Gaida Mahaifin Saif yai sannan ya musu sallama yai waje.
Jiyai ance Ina magana.
Tsayawa yai tare da juyowa dan duba mai magana.
Saif ya gani ya ya tsaye daga kan baranda, saukwa yai ya nufoshi.
Tunda ya taho Turab yake binsa da kallo ni kaina bansan me yake aiyanawa a ransa na.
Saif ya karaso sannan ya saki fuska yace " Naga kamar bai dace mu rabuba ba tare da sanin junan mu ba, duba da yanayin nan gaba zamu zama dangin juna?"
"Dangi?" Abu Turab yai fad'a sannan ya murmusa yace " Yama kace sunan?"
Saif.
Turab ya jinjina kai yace "Saifullahi, am sai dai kayi mantuwa Abdulmajid zaka fadawa haka bani ba."
Saif ya kalli Turab tabbas yaji haushin maganarsa yace " Amma na d'auka......"
Turab ya katseshi yace "Allah ya sanya alkairi."
ya juya ya tafi, dangin juna? Ya kara maimaita Kalmar tare da jan tsaki yace " kama rainamin hankali."
Yana shiga masaukinsu Sabi'u ya taso saga zaunen da yake yace " Ka dawu? Sirikin mu."
Turab ya bugamai wani kallo yace " wai ni har wani d'an rainin hankali zai kalla yace wai mun kusa zama dangin juna? Ha ha amma ya gama rainamin hankali ya karasa maganar tare da zama.
Sabi'u cikin mamaki ya kalleshi yace " Nikam kai da waye?"
Turab yaja tsaki yace " wai wani Saif, ko Khadija yakeso ko Khadija zai aura ni ban ma sani ba."
Sabi'u ya tuntsure da dariya yace " Turab? Kaine?"
Kallansa Turab yai baice komai ba sai dai takaicin dariyar yakeyi.
Sabi'u ya matso kusa dashi yace " Khadijan ka?"
"Eh ma......."
Sai kuma yai shiru sannan yai saurin mikewa tsaye yace " wace irin banzar tambaya ce wannan, ban gane Khadija ta ba? Wai kai Sabi'u me yasa ka iya abin haushi ne?"
Sabi'u yace "ohhh abin haushi? Sai naga kamar kishi ne ya ciwoka kake bukatar tausa."
Turab ya bugamai wani banzan kallo yace " kishi?" Mtsw kai fa sai a hankali wlh.
Ya fad'a tare da shigewa d'aki yanaji Sabi'u na cewa " karka manta anjima zakaje gaida Fulani mijin Gimbiya
"
Yana shiga d'aki ya zauna a bakin gado yace " me ya sameni? Why am i acting like this?"
Sai kuma ya nuna kansa cikin mamaki yace " don't tell me kishi nake?" Kai ya girgiza da sauri yace " inaa tayaya ma zanyi kishi akan wacce take zuri'ar makiyana?"
Yin baya yai ya kwanta akan gado, yana takaicin wannan abu, inama shikam baisan Khadija ba a rayuwarsa?"
*********
A can Zariya kuwa Magajiya ta rasa abinda ya kamata tai ta dade tana tunani kafin daga baya ta wuce cikin d'akinta.
A zaune a kasa ta taradda Khadija kana ganinta kasan tana cikin wani hali.
Magajiya ta karaso kusa da ita tace "Mamana mike." Ta fad'a tare da miko mata hannu.
A hankali Khadija ta tashi sannan ta zaunar da ita a bakin gado itama ta zauna a kusa da ita.
Hannayenta ta riko tace " Khadija san Abu Turab kike?"
D'agowa tai da sauri ta zubama Magajiya idanunta wad'anda suka cika fal da hawaye, sai dai bata iya bata amsa ba.
Magajiya tai murmushi sannan tace " kin san waye Abu Turab?"
Kallan mamaki ta mata dan bata fahimci me take nufi ba.
Magajiya ta d'anyi ajiyar zuciya tace " Khadija baki san waye yaran nan ba, wannan maciji ne wanda dafinsa keda tsananin zafi, kinsan yaron nan idanunsa biyu amma yake nuna makaho ne? Kinsan ya tsaneni da mahaifinki amma yake nuna miki so dan kawai yai amfani da ke? Mune jininke, mu kad'ai ne muka san darajarki bazamu taba cutar dake ba."
Ganin Khadija ta zare hannunsa daga cikin nata yasa ta tsaya da maganar tana binta da kallo.
Sai kuma ta mike sannan tai murmushi tace " Umma Babba bazan ce nasan Ya Turab ba tunda ba tare mukai rayuwa dashi ba sai dai namanta ban fad'a miki kalma d'aya ba, nice nakesan Ya Turab ba shine yakeso na ba."
Ta juya tana tafe kamar wacce zata fad'i dan ba shakka kalaman Magajiya sun so kawo mata rud'u cikin kwakwalwarta, maciji?yana gani?amfani da ita? Ba shakka ba dan tayi saurin katseta ba da alama da sai ta canza mata ra'ayi a xuciyarta.
Kallan kofar data rufo ta Magajiya tai a ranta tace " Umma Babba please don't disappoint me anymore."
Abdulmajid ta gani a tsaye a waje da alama ma jiranta yakeyi.
Yi tai kamar bata ganshi ba ta fara tafiya.
Da karfi ya finciko hijab dinta yace " Wato ke Abu Turab ya fi miki ni ko? In taimaka in barma Turab Mairo? Ke meyasa bakida hankali ne?"
Khadija ta kalleshi idanunta sunyi raurau tace " Yaya me ka nema ka rasa a duniyan nan?"
Kallanta yai baice komai ba.
Tace " kanada komai na rayuwa, matsayi,iyaye, lafiya, girmamawa, me ka nema ka rasa?"
Ta share hawayenta tacigaba " Ya Turab na san yarinyar nan, kai ko tausayin sa bakayi?"
Kallanta kawai yake yama kasa magana, ta share hawayenta sannan tace " ku kanku kunki kyale bawan Allahn nan, bakin cikin abinda kuke mai shine na tabbata dalilin dayasa ko ganina baisan yi....."
Hawaye ne suka nemi fin karfinta, da sauri ta juya ta fara tafiya.
Abdulmajid baki kawai ya saki yake kallan mamaki.
Shi Khadija takema wannan banzan sharhin?
*********
Mairo kuwa baya ta gama fad'an kalamanta Baseera ta jawota jikinta tana lalashi.
Tace " Mairo dama kina san Turab? Na dade ina hasashen haka sai dai wani sa'in ina tunanin rad'in kainane yasa nake ganin haka ba wai kece kike sanshi ba, ki kwantar da hankalinki ki koma gida, tunda har nasan abinda ke ranki ni kuma xanyi iya kokarina naga komai ya dawo daidai."
Mairo ta d'ago sai dai batace komai ba.
Hisham na fita ya wuce gida ransa a b'ace a tsakar gida yaga mahaifiyar Khadija a zaune.
Rufeta kawai yai da fad'a.
" Aikin banza ace tarbiya wannan kin kasama 'yarki, inba rashin tsaro ba har yaushe ma kika bari yarinyar nan ta sakankance da wani can sokon yaro, yaron da zuwansa doron kasa shine abu mafi muni da ya taba faruwa a rayuwata, to wlh inma zaki sa Khadija ta cire wannan shirman a ranta kiyi dan wlh in har na sake kamata tana kuka akan yaron can wlh abinda zan miki sai kinsha mamaki."
Bai jira ta tofa komai ba yai gaba fuuuu.......
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*51*
Zaune yake a cikin wani had'ad'an gun hutawa, a hankali yana cin inibin dake gabansa sannan yana duba littafin hannunsa, lumshe ido yake yi saboda yanda yakejin dadin rayuwa, cikinsa ne yaji ya murd'a nan fa wani azababben ciwo mai tada hankali ya rutsashi, baisan sanda ya durkuso kasa ba yana murkususu saboda azaba, idannan nasa yayi jaa kamar garwashi, tsananin tashin hankali da rad'adin da ya ke ciki.
Jiyai an sakar masa wata irin dariya na keta da sauri ya d'ago dan ganin wani mugun ne wannan ba taimako sai dariya?
Magajiya ce cikin wani had'ad'an shiga tayi kwalliya sosai, dariya take sosai.
Abdulmajid ne ya fito daga bayanta shima yana dariya harda kyakya tawa.
D'ayan gefen kuma Hisham ne ya fito shima dariya yakeyi sosai, nuna shi suka shiga yi suna dariya.
Basira ya gani a kasansu a kwance wanda baisan ko tana raye ba ko ta mutu.
Sannan Abdulmajid yana rike da igiya yana jan wata yarinya a kasa, kallan yarinyar yai ga mamakinsa sai yaga Mairo.
Kirjinsa ne ya d'au zafi, Khadija ce ta taho da gudu gunsa tana kuka kamar ranta zai fita, da sauri Hisham yasa hannu ya fizgota.
Jiyai gaba d'aya ya kasa numfashi da sauri ya bud'e idanunsa.
Cikin tashin hankali yake kallan d'akin, ga zufa da yai sharkaf.
Zama yai cikin tashin hankali yana addu'oi, ba shakka wannan mafarkin ya tsoratashi, shi yasa baccin yamma bashida kyau.
Mikewa yai ya sauko daga kan gadon, sai dai jiyai kafafunsa na rawa.
Gado ya dafa tare da runtse idanunsa.
Ya dade a haka kafin ya daure ya shiga ban d'aki.
Bayan ya fito ne ya zauna a bakin gado, ba shakka mafarkin ya bayyana karara kamar gaske.
Ga kansa na mai wani azababben ciwo.
Sabi'u ne ya leko yace " Ranka ya dade ka tashi? Wai daga shigowa sai in tadda kai kana bacci?"
Turab ya kalleshi kawai baice komai ba.
Sabi'u yacigaba " dama aiko wa akai in anyi magrib zakaje ku gaisa da Fulani."
"Gobe da sassafe zamu koma gida."
Abinda Sabi'u yaji ya fad'a kenan.
Mamaki ya kama Sabi'u da sauri ya karaso cikin d'akin yace " Mutumina lafiya?"
Turab ya kalleshi, ganin yanda idanunsa sukai ja ya matso da sauri yace " Yarima Lafiya?"
Turab ya mike yazo kusa dashi kawai ya dafa kafad'arsa sannan ya wuce.
Waje ya fito ya tsaya yana kallan sararin samaniya, me yasa yakejinsa haka?
Bayan Magrib jakadiya tazo ta raja Abu Turab gun Fulani, sosai ta karbeshi sannan itama ta rokeshi akan rikon Bilkisu, irin amsar dayaba Mai Martaba ita ya bata.
Haka ya taso cikin gamsuwa da yanda sukesan 'yar tasu.
Munnira ce ta biyoshi da sauri ta mikamau wata takarda.
Amsar takardar yai ya kalleta yace " ta menene?"
Munnira tai dariya tace " UmmaBilkisu ce tace in baka."
Amsa yai yana cewa
" Yau Umman taki rowar ganinta take min?"
Munnira tace " zaka ganta gobe ai."
Bud'e takardar yai yana cewa "Gobe zan tafi da safe."
Kallan mamaki tamai tace " Amma UmmaBilkisu vata sani ba?"
Kai ya d'aga yace " nima dazun na yanke shawarar haka, amma zan dawo ko zuwa sati biyu ne."
Duba takardar yai, number waya ce ta landline a jiki a kasa tasa, inka samu time ka nemin a layin nan."
Murmushi yai ya kalli Munnira yace "kice mata nagode, dama nayi tunanin tambayarta."
Ya juya yai gaba
***********
Washegari.
A zariya
Basira tayi shiru tana tunanin mafita, ba shakka ko d'anta bazai auri Mairo ba bazata taba bari Abdulmajid ya aureta ba.
Mikewa tai ta kali Lantana tace "Lantana muje in duba Hajiya sannan muje gun Magajiya."
Mamaki ne ya kama Lantana sai dai bata ce komai ba.
Sunje gun Hajiya jikinta kam kamar kullum ba sauki sam, dan ko maganarta dama ba ganewa akeyi ba.
Yau kam jikin ya d'anyi sauki.
Mai kula da ita suka tarar tana bata magani, sai dai tana ganinsu ta daina bada maganin ta mike da sauri ta rufe maganin ta d'auka.
Basira ta kalleta tace " ta gama shan maganin ne?" Dan yanayin yanda yarinyar tai yasa ta kasa fahimtar hakan.
Cikin rawar murya tace " ta gama." Ta karasa magana tare da fita.
Basira ta zauna kusa da ita sannan ta