Showing 36001 words to 39000 words out of 146065 words
Chapter 13 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
ba, addu'a kawai zaka mata, amma nikam Umma bakya ganin Baba ne yakamata ya d'aukota ta zauna a gunsa, ta yaya za'abar ta ita kadai a gida?"
Magajiya ta kalleta tare da canza fuska tace " kin fadama Hisham din haka?"
Tace " yanzu abin ya fad'omin."
" Tun kafin ya hauki da fada karma kimai wannan zancen, ke dai kije ki dubata gobe."
Khadija zata sake magana Magajiya tace " Khadija bansanki da musu ba."
Shiru tai batace komai ba, sai dai tana ganin hakan bai dace ba, yaza'ayi ace 'yan uwanta da 'ya'yanta duk sun watsar da ita?"
*******
Bayan anyi sallar isha'i ne Jakadiya tazo ta sanarmai da sakon Mai Martaba akan yana san ganinsa.
Shida Garzali suka fito, bayan ya shiga ya zauna ne Mai Martaba ya kalleshi yace " Nayi dogon naxari akan abinda ya faru sannan na sanar ma Sabi'u akan yai bincike akan abinda ya faru, tunda naga shine na hannun damanka."
Abu Turab kansa na kasa yace " Abba!"
Kallansa Mai Martaba yai ba tare da ya amsa ba, dan raban dayaji ya kirashi da Abba tunda ya mallaki hankalin kansa.
Abu Turab ya cigaba " wani hukunci zaka d'auka akan wanda ya aikata hakan?"
Sarki yace " dole ne ya fuskanci hukunci mai karfi."
Murmushi ya saki sannan yace " ko da kuwa Magajiya ce?"
Kallansa yai yace " me kake nufi?"
Abu Turab yace " a matsayin d'a nazo gunka inaso d'a da mahaifinsa suyi magana bawai sarki da d'ansa ba."
Sarki ya kalleshi yace " shine nace mai kake nufi?"
Abu Turab ya d'anyi shiru kafin yace " zaka iya hukunta Matar da take da mukami fiye da kowa?matarda yayanta yake waziri?matar da d'anta yake magajinka?matar da duk yawancin masu mukamin nan suke a kasanta?"
Sarki ya kalleshi ranshi a b'ace yace " Turab!"
Abu Turab ya d'an sunkuyar da kai yace " tuba nake ranka ya dade bawai da wanj abin na fadi hakan ba sannan ba wai nace itad'in ce tai ba sai dai ina tunanin mu binne maganarnan inhar hukunta mai laifin zai iya zama wani abu."
Sosai ran Mai Martaba ya b'aci mai Abu Turab yake nufi?
" bance itace tai ba sannan ban san wanda ya aikata hakan ba, ina tsoron kar ka kasa yanke hukunci ne in laifi ya fada hannun manya."
Sarki ya kalleshi jiki a sanyaye yace " kaima kanasan kacemin baka yarda dani ba? Kaima kana ganin nid'in ragon sarki ne wanda bazai kya hukunta Matarsa ba?"
Kai Abu turab ya girgiza jikinsa shima yai sanyi yace " bawai hakan nake nufi ba sai dai banasan na zama sanadiyar saka cikin tsaka mai wuya."
Murmushin takaici yai yace " na sani ban kula da ku ba kaida mahaifiyarka lokacin kana yaro sannan na sani laifinane da bana shiga duk wani harka data shafeku sai dai na sani bazaka taba gane dalili na nayin hakan ba."
"so kake ka karemu, bakasan a gane damuwarka a kanmu bare a mana illa." jin wannan zance daga bakin Abu Turab yasa ya kuramai ido.
D'agowa Abu Turab yai ya kalleshi, jiyai zuciyarsa ba dadi, ko dai ya dau abin da zafi ne?"
Ga mamakinsa gani yai Sarki ya saki wani sansanyan murmushi sannan yace " Alhamdulila d'ana ya girma."
Baisan sanda ya kalleshi ba cikin mamaki.
Sarki yamai alama da hannu akan ya matso.
Da sauri yad'auke idanunsa, Mai Martaba ya kara mai alama da hannu sannan yace " na sank kana gani Turab."
Idanu Abu Turab ya zaro Sarki ya mike da kansa yazo inda yake, kansa ya d'ago saitin sa yace " na sani da dadewa, na janye idona ne daga nuna maka saboda banasan ruguza abinda mahaifiyarka ta shirya ya ruguje."
Idanunsa ne suka ciciko, kai ya girgiza mai yace " ka manta mai kace? A matsayin Uba kakeso muyi magana? Yau a matsayin uba nake, daga kabar nan zan koma sarki in kuma manta da abinda ya faru tsakanin mu."
Idanu ya runtse yama kasa magana sam, Sarki yad'an had'e fuska kadan yace " ina Abu Turab dina wanda baya shakka ta? Jarumin da nake farincikin samun d'a kamar sa?"
Baisan sanda yad'an murmusa ba.
Sarki ya kalleshi yace " me ka shirga game da abinda Magajiya ta maka?"
Abu Turab ya kalleshi yace " bazan iya fadama Sarki ba, sai dai ina neman alfarma akan kaba Abdulmajid umarnin yin binciken abinda ya faru."
Bai kara tambayarsa va yace " shikenan, sai me kuma?"
Yace "inaso ka taimaka ka cigaba da nuna rashin damuwa dani da kuma hukuntani sosai in nai ba daidai ba."
Yace "shikenan, sai kuma me?"
Kai ya girgiza yace " su kenan."
Murmushi sukama junansu.
Abu Turab ya mike zai tafi, jiyai mahaifinsa yace " yanzu mun zama d'aya kenan ko?"
Ba tare da ya juyo ba yace " dama can d'aya muke."
Yana kaiwa nan ya bud'e kofa.
Yana fita ya had'e fuska sannan ya tsaya a waje kamar irin an mai fadan nan sosai, ya dade a tsaye kafin jiki a sanyaye ya fara tafiya, tuntube yai saura kiris ya fadi da sauri Garzali ya taimaka mai sukai gaba.
Jakadiya ta tabe baki sannan tace " da alama ansha fada, ai naso a nan akai ba a kuryar d'aki ba."
Nace hmmmm
*ABU TURAB TEAM 🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*24*
Abu Turab yana shiga d'akinsa ya rufe tare da jingina a jikin kofar, tausayin Mahaifinsa ne yake ratsa jikinsa ace kana san abu amma saboda kana mulki baka isa ka nuna ba? Lalai shikam wannan mulkin sam baya kansa.
Haka ya kwanta bacci zuciyarsa fal da tunani kala kala.
********
Washegari a fada Mai Martaba ya umarci Abdulmajid akan ya d'aurashi akan aikin binciken abinda ya samu kaninsa.
Ba Abdulmajid ba kowa na fadar sai da yai mamakin wannan al'amari, ai ko ba'a fada ba kowa yasan ba wata soyayya ko mutunci a tsakaninsu, amma ace shine zaiyi binciken?
Andulmajid ya kalli Mai Martaba cikin tsananin mamaki, kafin ya daure yace " insha Allah zanyi binciken abin in sanar maka."
Yana fitowa Hisham ya biyoshi, Hisham ya kalleshi yace " me ke faruwa?"
Abdulmajid ya dan kurama kasa ido sannan yace " abinda ke faruwa?" Umm yad'anyi ajiyar zuciya yace " wannan shine tambayar da zan fara nemanma amsa."
Hisham yace " muje gun Magajiya nikaina inasan ganinta."
Bayan sun isa gunta ne sun gaisheta, Abdulmajid ya sanar da ita abinda ke faruwa, murmushi ne mai sanyi ya bayyana a fuskarta ta kalli d'an nata tace " hmm lalai Turab ya girma sai dai Tsohon doki yafi sabon takalmi."
Abdulmajid ya mata kallan rashin fahimta, "Tsi tsi tsi tsi" abinda tai da bakinta kenan tana jijiga kai tace " karka badani mana Abdulmajid, ba shakka Turab abinda ya nema mahaifinsa yamai kenan jiya.
Hisham yace " nima naji labarin zuwansa sai dai naji ance fada aka mai?"
Baki ta tabe tace " ko da wasa ni nasan ba fada aka mai ba in har fada ne mezaisa ya shiga kuryar d'aki? Sannan da yamma ya riga ya umarci Sabi'u akan yai bincike sannan yau da safe ya maidashi kan Turab ne hakan yake nufi?"
Hisham ya kalleta yace "amma hauka yake da zai umarci Abdulmajid? Bayan yasan ba sanshi yake ba."
Abdulmajid ya kalli Magajiya yace " Umma kina nufin yayi hakan ne saboda karmu d'aurama mahaifiyarsa laifi? Tunda yasan ai ni ban isa ince mahaifiyarsa bace hakan zaisa a zargeni."
Magajiya ta mai alamar jinjina da hannu tace " kwarai kuwa Yarima na ashe ka harbo jirgin."
Dariya Abdulmajid yai yace " lalai yaran nan, yana makaho har......"
Katseshi tai tace " munyi sakaci da muka ragamai muna tunanin makaho ai baya ganin komai, masarauta fa muke?sannan jinin mahaifinsa da kakansa suna yawo fa ajikinsa."
Hisham ya kalleta yace " yanzu meye abinyi?"
"Hmm farko dai tunda ya maida wasan kanmu dole ne mu buga wasan, ai hakorin dariya shi yakanyi cizo."
Kallan mamaki suka mata, tai kalli Abdulmajid tace " ka nutsu sosai kaga yanda zan buga wasan."
Shiru yad'an biyo baya kafin Hisham yace " ni kuma wani abu d'aya ne yake damuna, me yasa haryanzu sarki ya kasa neman ma Abu Turab magani?tunfarkon zuwan sa da yadanyi na shekaru kad'an yanzu sam baya turo masu magani, ko ya hakura ne da makantar yaron....."
Magajiya ta d'an kankance ido tace "ko kuma ya warke ba."
Idanu suka zaro suka kalleta, shiru tai tana tunani kafin ta mike da sauri tace " me yasa hakan baizo min ba?"
Da sauri ta kalli Hisham tace " Hisham aika a kiramin yaron nan."
Abdulmajid shima ya mike hankalinsa a tashe yace "Ya zamuyi in har yana gani? Kenan za'a iya bashi mulkina!"
Magajiya ta bugamai wani kallo tace " so kake ka zama rago akan wani makahon daya warke?"
Hisham ne yai waje da sauri ya tura baiwar Magajiya akan ta aika a kira Abu Turab.
Shiru tai tana tunani kafin tace " aika a dafomin ruwa mai zafi sannan a zubo a roba, a kuma zubo ruwa mai sanyi shima a roba."
Shiru tai tana tunani kafin ta fita da kanta, ba shakka hankalinta ya tashi, ya zatai in har yana gani? Kenan tunda raina musu hankali yakeyi kenan.
********
Zaune yake yanashan ruwan zafi wanda yasa aka dafa mai da kayan kamshi, zafin cittar yasa yake d'an lumshe idanunsa, shigowar Garzali ce tasa ya bud'e idanunsa.
Zubewa yai a kasa ya sanar dashi sakon nemansa da Magajiya takeyi yanzu.
Bai amsa ba ya cigaba da shan shayinsa.
Sai daya gama sannan ya mike ya shirya ya fito, Garzali ya taso da sauri yazo kusa dashi.
Tafe suke yana rike da sandarsa, idanunsa ne suka kai gun jiya inda yarinyarnan ta b'uya, ya rasa me yasa yakeji kamar ana kallansa.
Yana kallan gun kuwa suka had'a ido.
Da sauri ta b'oye tare da dafa kirjinta dayake bugawa da sauri, a tsorace tace " ya ganni?"
Kai ta girgiza tace " ta ina zai ganni?"
Shikansa jikinsa ne yai sanyi yana tunanin abinda ya gani, kawar da abin yai a ransa har suka karasa b'angaren Magajiya.
Tana zaune a kilisarta, Abdulmajid na gefenta, Hisham ma na d'aya gefen nata ya shigo.
Sai daya zauna sannan Garzali ya fita.
Gaisheta Abu Turab yai ta amsa tana karema idanunsa kallo kansa na kasa, kallan zargi takema a haka tace " Me ya faru ne sam ka daina zuwa gaisheni."
Murmushi ya d'anyi yace " Da alama Umma Babba san ganina ne yasa kika manta nazo kwanan nan."
Kallansa tai tace "haba? Amma ya akai nakeji kamar na dade banga d'ana ba?"
Yace " zan dinga zuwa akai akai in har kinasan ganina."
Tai dan murmushi sannan tace " bari a kawo ma abinci kaci, yau takanas nasa a ma d'ana abinci, dan na kula bana baka kulawa yanda ya dace."
Ya jita sai dai bai tanka mata ba, nan tasa aka jera mai a binci tace " bismillah."
Hannu ya saka yana shashafa kwanukan alamar baya gani, kwarai yaga ruwan zafin dake daf dashi, tunani ya fara yi me ya kawo ruwa wanda yake turiri kusa dashi? Kana kallan ruwan kasan yanzu aka juyeshi, ba shakka zargin ganinsa takeyi, bazai taba ba mahaifiyarsa kunya ba dan kawai ya faranta ransa ba, hannunsa yakai kan ruwan zafi da saninsa ya sa hannunsa zuciya d'aya.
Azabar dayaji ne yasa ya zare hannun da sauri ya rike hannun cikin jin zafin zugi da radadin da yakemai.
Kallan juna sukayi suka saki murmushi ba shakka baya gani.
Da gudu ta karaso ciki tashin hankali, hannunsa ta kama da sauri ta saka cikin ruwan sanyi.
Kuka kawai takeyi hankalinta yayi tsananin tashi.
Magajiya ta mike itama tace " lafiya Abu Turab?"
Ta fada tare da nunama Abdulmajid ya d'auke ruwan zafin.
Nan ya d'auke ruwan.
Kallansa tai tace " garin yaya? Ina lilahi wa ina ilaihi raji'un, me ya faru? Badai ruwan wanke hannu danace su kawomin bane suka kawo na zafi, inaji sun d'auka kafata zan gasa wacce ma bige jiya."
Ba wanda ya kulata tsakanin Abu Turab da Khadija.
Shikam yama kasa komai zafin hannunsa da kuma ganin Khadija sun sa sam yama kasa cewa komai.
Kuka take sosai ta mike da gudu ta fita, dawowa tai d'auke da zuma a kofi ta shafamai, Magajiya duk ta rikice.
Abu Turab ya daure ya kwace hannunsa sannan ya mike yace " bakomai Umma Babba ba laifinki bane na sani, ke mai zaisa kisa a kawoma d'anki makaho ruwan zafi haka? In har dama ba neman halakashi kike ba, wanda nasan ke kuma ba hakan bane a gunki."
Ta bud'e baki zatai magana yai waje.
Ba shakka ta tabbata magana cikin magana ya fada mata.
Khadija ta kallesu dukansu cikin kunar rai sannan tai waje da gudu.
Binsa tai inda yake ta rike hannun daya kone ta sama tace " yaya muje a baka magani."
Fuska ya d'aure tamau sannan ya kalli Garzali yace " wacece wannan d'in take tabani?"
Garzali ya kalleta, zaiyi magana tai saurin cewa " Yaya Khadija ce, nice kasani ba cutar dakai zanyi ba."
Hannunsa ya fizge yace " ta ina kenan na san ba cutar dani zakiyi ba? Ko na sanki ne da harzan iya miki shaida?"
Sakeshi tai idanunta suka ciciko a hankali tadanyi baya kadan tana mai kallan tsananin mamaki.
Garzali wuce muje.
Tana tsaye anan har suka kule sam tama rasa abinda zatai tunani.
Jiki a sanyaye ta koma b'angaren Magajiya.
Taje shiga taji suna dariya, Hisham yace " da alama dai idannan bam yake baya ganin komai."
Dariya Abdulmajid yai yace " tab amma fa ya daure dan ruwan zafi ba wasa bane."
Bud'e kofar tai da karfi cikin tsananin mamaki ta kallesu.
Tace " da saninku?"
Dif sukai kowa ya kura mata ido.
Hawaye ne suka shiga zubo mata ta girgiza kai tace " kuna 'yan uwa, ko ba 'yan uwantaka ai akwai na musulunci, tayaya zaku samu mutum wanda Allah ya d'auke ganinsa ku samai ruwa ya kone? Nazo da niyyar muku magana akan barin Inna Lami a halin da take bayan na dawo daga gunta, sai in tarar da wanda yafi nata?"
Kuka ne yaci karfinta tace " anya akwai tausayin imani a zuciyoy......"
Wani wawan mari Hisham ya mata wanda batai zatan jinsa ba.
Kuncinta ta rike ta kalleshi, kasa magana tai, waje tai da gudu taba kuka.
*#ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
_ina baku hakuri jina da kukai shiru, wayatace tad'an samu matsala nagode kwarai da kulawarku, naga sakwaninku na kuma gode, plz wanda yamin magana baiga namai reply ba yai hakuri whatsapp dina baiyi restoring old messages dina ba, nagode._
*25*
Turab yana shiga ya bud'e kofar d'akinsa yasa kai zai shiga kenan yaji muryar Garzali yace "Ranka ya dade ana nemanka."
Juyowa yai yace " wa?"
Garzali yai kasa dakai, Abu Turab ya kalleshi yace "Umma ce?"
"Tuba nake ranka ya dade."
Idanu Turab ya rufe, Garzali ya tsugunna da sauri yace " Tuba nakeyi."
Abu Turab ya juya har yakai kofa sannan ya tsaya yace " ka fada mata komai?"
Garzali yace " a'a bansan waye ya sanar da ita xuwan mu can ba, ina shigowa ta turo inxo, tambayata tai me ya faru a inda mukaje....."
Katsetshi yai yace " tambayar da maka itace ka fada mata komai?"
Garzali yace " nadai sanar da ita kunan dakai amma bansanar da ita wani abu ba daga wannan."
Takawa yai ya cigaba da tafiyarsa fuskarsa a d'aure.
Xama yai irin zaman daya sabayi a gaban ta, wato lankwashe kafa, kansa na kasa kallansa tai cikin kulawa tace " muga hannun."
D'agowa yai ya mata murmushi yace " Umma karfa ki damu ba wani abu bane nine bansani ba na taba ruwan zafi sannan a lokacin aka samun zuma a gun."
Ido ta kuramai cikin kulawa da tausayi tace " Turab ba sai ka dage ba wajen b'oyemin gaskiya ba dan hankalina ya kwanta, banaji ko yaro ne yaji xancen nan naka zai yarda."
Kallanta yai yace " Umma."
Yanda ya kirata yasa bata amsa ba sai kallesa datai.
Ajiyar zuciya yai yace " Umma ina neman alfarma a gunki."
Idanunta na kansa bata dauke ba haka kuma batace komai ba ya cigaba " abu d'aya nakeso kimin, dan Allah Umma ki rage damuwa dani."
Cikin tsananin mamaki ta kalleshi sai dai yanayin yanda yai maganar yasa ta kasa magana.
Idanunsa yadan rufe kadan sannan yace " gidan sarauta muke, sarautar ma inda makiyanmu sukai yawa, na tabbata a gidan nan kaf daga ciki har waje in har mukace muna neman wanda yake kaunarmu dari bisa dari banaji zamu samu mutane goma cikaku, in muka dauke bayin dake karkashin mu, yanayin yanda muke rayuwarmu ni dake dole ne sai mun sadaukar da rayuwarmu dolene mu sha wahala in har munasan zama cikin kwanciyar hankali, sa damuwata a ranki da kuma shiga wani hali in har abu ya sameni ina ganin babbar matsala ce, saboda dole wani sa'in zan nemi b'oye miki wani abun saboda gudun shiga wani yanayi da kikeyi."
Kallansa tai jikinta yayi mugun sanyi, tanasan