Showing 96001 words to 99000 words out of 146065 words
Chapter 33 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
kauna, inama lokacin da suke yara ya dawo? Lokacin da suke kullum tare, cikin tsananin bege da kulawa.
Kin kafeni da ido bakice komai ba.
Khadija ta kakaro murmushi tace " Ba fara'a yanzu a tsakaninmu."
Kallanta yai sai dai baice komai ba ya maida kansa inda yake kallo da.
Murmushi ta sake yi na tausayin kanta cikin wani yanayi ta fara cewa " sa dayawa ina tunanin ina ma, ina ma ban sanka ba? Ina ma banida had'i da wannan gidan? Inama da naje kano ina karama ban dawo ba."
Tacigaba bayan ta d'an had'a hannayenta gu d'aya.
"Yaya na rasa wace irin mummunan kaddara ce tsakaninmu? Banida abinda xancema na abubuwan da mahaifana suka aikata, bani kuma da bakin baka hakuri akanshi, sai dai zam baka hakuri akan abubuwa gudan biyu."
Hawayene suka zubo mata ta sa hannu ta sharesu tace " Yaya kayi hakuri akan abinda Ya Abdulmajid ya maka, ba wai ina baka hakuri bane dan ka yafemai a'a ina baka ne saboda neman sassauci akansa, ina tsananin tausayinka sai dai ina tausayin Ya Abdulmajid."
Juyowa yai ya kalleta, da alama tasan komai, dama ranad da ta fad'o musu gaban mota tai wannan firucin ya tabbata akwai wani abu da ya sani."
Idanunsa na kanta yace " kin san komai kenan da alama."
Hawayenta ta sake sharewa tace " Yaya wancan sokon yayan nawa baisan komai ba, baisan abinda suka aikata mai ba, tunda yake bai taba keran wacce ta d'au cikinsa na wata tara da sunan uwa ba, bai taba yi mata wani abu ba wanda d'a ya kamata yama uwarsa ba, ko magana tamai gani yake matsayinsa ya wuce a nemi bashi shawara, wancan soko yaya baisan matsayin da yake takama dashiba ba nashi bane, matar da yake kokarin faran tawa rai a koda yaushe baisan amfani take dashi dan cikar burinta bawai dan so ba, Yaya Turab sannan wancan sokon ya gama mutuwa akan san wacce bata sansa, tunda yake a rayuwarsa banaji akwai mutum d'aya wanda ya kasance yana kaunarsa kauna ta yanda yake bawai dan tushensa ba ko dan halayensa ba,yaya wancan sokon d'an uwa nane jini nane wanda ni kaina......."
Kuka ne ya ci karfinta wanta take yinshi daga cikin zuciyarta kuka mai taba zuciyar mai sauraro.
Duk yanda yaso ya jure ya kasa dan kukan sosai yake taba ransa ba shakka shi kansa yana tausayin Abdulmajid, mikewa yai ya nemi hanyar fita.
Cak ya tsaya dan jiyai bazai iya fita ba tana irin wannan kukan.
Handkerchief ya zaro daga cikin aljihunsa na wando ya nufo inda take.
" Ungo." abinda ya fada kenan yana mika mata.
A hankali ta d'ago sannan tasa hannu ta amsa.
Juyawa yai zai fita, da sauri tasa hannu ta riko rigarsa.
Turab ya tsaya sai dai bai juyo ba.
Saukowa tai kasa ba tare da saninsa ba ta sanya gwiwowinta biyu a kasa.
Tace " Ya Turab."
Juyowa yai kallan mamaki ya mata gani gwiwowinta biyu a kasa.
Yace " meye hakan?"
Tace " kasa ama duk wani laifi a cikinsu hukunci sai dai dan Allah yaya ka hakura kaima da abu d'aya, kana da komai a rayuwarnan.
Mulki, uwa ta kwarai, mata, sannan dukiya da ilimi da kuma masoya, dan Allah ka sadaukarwa Ya Abdulmajid da abu d'aya na daga cikin wad'an nan abubuwan da Allah ya azurtaka dashi ka bar masa Mairo kad'ai, ita kadai, in tana tare dashi gani nake ko wani abu ne zai sameshi zai jure sannan ko wani hukunci aka mai zai yi kokarin jureshi."
A hankali ya furzo da wata iska sannan yasa hannayensa biyu ya d'agota, kallanta yai ido cikin ido, yace" bazan yi miki dogon bayani ba, ba kuma zanyi duk wani abu da kikeso ba, abu d'aya na sani shine duk wani mai laifi zan sa a hukuntashi indai da raina, akan ganin bayan Magajiya even u i will have to use u."
Ba tare da wani tunani ba tace " use me ya Turab, kayi amfani dani ta kowace hanya da kakeso, bazai damen ba, me kake tunanin zanyi?."
Wani murmushi wanda ni kaina bansan ma'anarsa ba yai sannan yace " even if i hurt u?"
Kallansa tai sannan ta ce " please yaya hurt me."
Shiru yai yana kallanta dan tabbas kalmar data fada har zuciyarsa ya jita.
Murmushi ta mai sannan tace " Yaya a koda yaushe zam kasance mai ma addu'a."
Wuceshi tai ya fara tafiya, tana tafe hawaye na zubo mata, ji take kamar yau shine rana ta karshe da zasuyi magana irin haka, itakam tasan farinciki? Bataji zata sameshi a duniya.
Idanu ya runtse dan tabbas yana bala'in san Khadija, ya tabbatar yauce rana ta karshe da zasu zauna kamar haka, Allah ka bani ikon yin abinda ya dace, abinda ya fada kenan sannan ya juya.
*********
Duk yanda taso tai bacci ta kasa, juyi kawai take a kan gado tana tunanin abinda ya cancanta.
Tabbas dolene ta gajarta rayuwar Abu Turab, a ranar auransa dolene ta kaudashi ko ta samu salama, duk sanda bacci ya d'auketa sai taga Abu Turab a gabanta ya sa hannu ya shake mata wuya, dole ta tashi daga barcin.
Wannan abu ya dameta.
Da safe ta shirya tsaf dan ta gama yanke hukuncin yin komai da Abu Turab zai umarta na lefensa har ta samu a zo bikinshi ita kuma ta sa Hisham ya aiwatar da abinda ya dace.
Sai yamma ta samu nutsuwa dan tana ta yin aike.
Ta zuba abinci zataci kenan aka sanar da ita zuwan Abu Turab.
Ta rasa dalili duk sanda taji zuwansa kwanan nan sai taji gabanta na fad'uwa.
Mikewa tai ta gyara jikinta dan batasan ya fahimci wani abun.
Zama tai irin zaman data saba.
Turab ya shigo sannan ya gaisheta.
Amsawa tai cikin isa sannan tace " ya akai?"
Murmushi ya sakar mata yace " na d'auka farin ciki zakiyi da ganina? Banji dadi ba ganin ba kiyi farincikin zuwana ba."
Tace " ina fa? Ka taba ganin inda uwa tayi bakin ciki da zuwan d'anta?"
Yace " haka ne fa kuma, ya an fara had'a lefen?"
Ta kalleshi sai dai batace komai ba.
Yace " Jiya naga Khadija ai, nan tazo ko ganina tazo yi kadai?"
Magajiya wani abu ne yazo mata ta kalleshi tace " gunka ta fara zuwa kafin tazo nan ko?"
Turab ya kalleta dan bai fahimceta ba, tace " ai na sani, dama ni nasan yarinyar nan da ba ruwanta ba yanda za'ai tazo min da wannan banzan zancen."
Turab ya fahimcu Khadija magana tai da Magajiga wanda da alama abin ya sosa ranta.
Yace " hmmm ai banyi tunanin wannan abin zai b'ata miki rai ba......"
Magajiya tai dariya kadan tace " kana tunanin in ka zugata karta auri saif zan amince dakai ne? Meye manufarka da neman had'a auran ta da Abdulmajid?"
Sai yanzu ya fahimta baisan sanda yai wata dariya ba, Khadija? He can't believe that naive girl can......
Magajiya ce ta katseshi da cewa " In har kanasan Sirrin mahaifiyarka da kuma auranka ya yiwu karka kuskura ka kara sa Khadija cikin al'amuran mu."
Turab ya kara murmusawa yace " me? Akwai wani dalili ne dazai hana auransu?"
Idanu ta zaro tace " baka da hankali ne?"
Ya dan tabe baki yace " ban fahimta ba? Akwai dalili ne?"
Magajiya ta kalleshi tace " ba wani dalili kana san ka hadasu aure bayan ba san juna suke ba?"
"Ooooo soyayya? Banaji dama a aure irin namu ana neman soyayya, kinsan da haka kike neman had'a Abdulmajid da Gimbiya? Hmm banaji kema auran so kikai."
Mikewa tai da sauri tai wani murmushi wanda yake iya lab'anta tace " in ma hakan ne ina tunanin bakada hakki akan auransu, Khadija da Abdulmajid ina tunanin duk 'ya'yanmu ne basuda had'i dakai."
Turab ya jinjina kai yace " kuma haka ne fa."
Tace " ba sai ka kara zuwa bangarena ba, in na gama had'a lefenka zan aika ma uwarka ta gani."
Ta juya tai ciki.
Turab ya bita da kallo.........
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*63*
Kallansa tai tare da yin ajiyar zuciya tace " wai ni Abdulmajid mai na tsare maka ne?"
Kallanta yai sai dai baice komai ba, tace " saboda kai yanzu ko gaida Umma Basira ba na iya yi, na fadama banaso dan Allah ko ana so dole ne?"
Kai ya rangwada gefe ya sakar mata wani lallausan murmushi yace " Mairo inaso inga kina fada, kyau yake miki."
Rasa ma mai zatace tai ta saki baki cikin takaici tace " Dan Allah nidai na rokeka ka kyaleni."
Abdulmajid ya matso hakan yasa tai baya da sauri dan ta san halinsa.
Sai da takai jikin bango sannan tace " matsa menene hakan?"
Abdulmajid fuskarsa a had'e ya sako fuskarsa saicin kuncinta.
Tsoro yasa tasa hannu biyu a kirjinsa ta turashi.
Hannayenta ya rike yace " Mairo sai yaushene zaki daina wahalar dani?"
Gabanta ne ya tsananta fad'uwa, ga dare ne soron ba haske, tace " ban fahimceka ba, wahalar dakai name?"
Jawota yai saura kiris ta had'u da jikinsa gashi ya rike mata hannaye duka, yakai bakinsa saicin kuncinta kamar wanda zai sumbata, da sauri ta runtse idonta cikin tsananin fargaba tare da sa kafa ta taka mai kafarsa.
Ko gezau baiyi ba sai dayai bakisa daf da kuncinta sai kuma ya saki dariya yace " Mairo kinganki kuwa?"
Gabanta sai wani irin fad'uwa yake ta kalleshi, hannayenta ya saki yana cigaba da dariya yace " sry, wlh ba abinda zan miki kawai so nake naga yanda zakiyi."
Lab'enta na kasa ta ciza sannan ta sa kafarta ta kara taka kafarsa da karfi.
Kara ya saki sannan yai baya da sauri yace " Mairo amma dai ke wlh da a india kike da film zakiyi, boss zaki zama."
Harararsa tai tace " Allah Abdulmajid ka kiyayeni."
Kansa ya shafa yace " ba laifi ai in namiji ya kiyayi matarsa."
Ta makamai wata hararar tace " mijin tace kawai."
Ta fada tare da juyawa zatai gaba.
Gabanta yasha da sauri yace " Sai da safe, gobe zan sake magana a fada dan na gaji da jira."
Tana kokarin bashi amsa yai gaba, tsaki taja sannan tai gaba, haushinta ma da mahaifiyarta ta sata ta fito da ai ta ce ko yazo bazata sake fitowa ba.
Tana shiga ta wuce d'akinsu ta fada kan gado.
Ummanta ce ta leko tace " kin dawo?"
Mairo tace " Umma ni dai ko yaran nan ya dawo dan Allah karki kara cewa in fita, ni wlh bana so."
Tace " Mairo shifa aure da kike gani ba wai mutum ne yake zab'awa kansa ba, babu yanda za'ai wani ya auri matar wani, haka kuma babu yanda za'ai wata ta auri mijin wani, duk wanda kika ga sunyi aure to fa dama akwai aure a rubuce a kaddarar rayuwarsu, inhar yaran nan ba mijinki bane cikin ruwan sanyi sai kiga kun rabu bawai fadanki bane zai sa ku rabu."
Mairo ta turo baki, tana san magana taga Umma tayi waje, kara komawa tai ta kwanta a fili tace " Ya Allah!"
************
Magajiya kuwa a daren yau ta tsaya sosai tayi tunanin al'amarin dake faruwa, yanzu ta fahimci Abu Turab bai san sirrinta na Abdulmajid ba, tunda a tunaninta da hankalinsa bazai yi tunanin had'a auren Abdulmajid da Khadija ba in har yasan wannan sirrin, tunda yasan ba abu bane mai yiwuwa.
To wanne ya sani? Maganin nan ta tuno da abinda ya fad'a mata a lokacin, mikewa tai zaune tace " yasan sirrin ba Hajiya magani." da alama wannan shine sirrin da ya sani.
Washegari da sassafe tasa aka kira mata wannan yarinyar, yarinyar ta shigo jikinta sai tsuma yakeyi, ta shiga ta zauna a falon da ba kowa.
Magajiya ta shigo sanye da rigar bacci dan ko wanka batai ba, karfe 6 ne na safe.
Magajiya ta kalleta tace " ina abinda aka baki?"
Da sauri tasa hannu a lalitarta ta d'auko maganin.
Magajiya ta kalleta tace " akwai wanda ya kamaki da wannan maganin?"
Kai ta girgiza alamar a'a tace "ba kowa, ina kuma zuba mata kullum."
Magajiya ta kalleta tace " kin tabbatar? Kinsan dai mahaifinki na cikin wani hali, kuskurenku d'aya zai jawo masa ajali."
Da sauri ta sunkuya tace " tuba nake rankiya dade amma ba wanda yasan maganar nan."
Magajiya ta amshi maganin sannan tace" jeki."
Mikewa tai tare da karayin godiya.
Tana fita tai ajiyar zuciya, kalan Abu Turab ta tuna sanda ya ce karta kuskura ta nuna yasan komai, sannan ya bata maganin saboda gudun zargi."
Magajiya tai shiru bayan ta fita, tace " to me yake nufi? Ta tabbatar akwai wani sirri da ya sani, sannan ko baisan maganin nan ta hannun yarinyar nan ba ta tabbatar yasan da zancen maganin, dan tabbas irin wannan ne a hannunsa.
Ajiyar zuciya tai tace " mai ya sani yaran nan?"
Tun kafin asiri ya tuno gwara ta salwantar da maganin, sannan yarinyar nan ta turata wani garin ita da mahaifinta.
*********
Abu Turab zaune kusa da Hajiya wannan yarinyar tanamai bayanin komai, ya jinjina kai yace " hakan yayi, sannan ki shirya zan canza ma mahaifinki asibiti sannan ke kuma ki koma ki kula dashi, kafin lokacin da zaki bada shaida yayi."
Tace " to."
Turab ya kalli Lantana yace " Lantana akwai wacce kika yarda da ita a gidan nan?"
Tace " eh akwai wata yaruwata da aka kawo."
Turab yace " ki dawo da ita nan sannan ke ki koma gun Umma dan kar Magajiga ta fahimci wani abin, ina tsoron kar ta ma Hajiya illa ta wani gun."
Lantana tace "to."
Mikewa yai ya wuce bangarensa, yana shiva Garzali ya sanar dashi kiran da Mahaifiyarsa take masa.
Turab ya juya.
Sai da ya gaisheta sannan yace " Umma gani."
Ta kalleshi tace " Abu Turab me yasa baka zuwa gub Mahaifinka?"
Kansa na kasa bai d'ago ba baikuma ce komai ba.
Basira tace " Mahaifinka na nemanka, yana san ganinka."
To, kawai yace, sannan ya kalleta yai murmushi yace "zanje Umma, shikenan?"
Fuska ta saku tace " ko kaifa?"
Kansa ya sunkuyar yana murmushi, tace " Ya maganar Mairo?"
Kallanta yai sannan yace " Hmmm Umma yanzu ba wannan bane matsala, sai dai insha Allah shima ba wani matsala."
Tace " to, amma Turab nidai kayi a hankali da Magajiya dan wlh wannan matar bala'i ce."
Yace " Nasani Umma, bala'in gaske ma kuwa, sharrinta ya wuce duk yanda kike tunani, zan sanar dake komai sai dai ba yanzu ba."
Tace "shikenan."
Sai yamma sannan ya nufi gun mahaifinsa, sai daya gaisheshi sannan Sarki ya kalleshi yace " Turab ina ka shiga ne haka?"
Turab yace " ina nan, abubuwan ne sukai yawa." kansa na kasa yai maganar nan.
Sarki ya kalleshu yace " kasan tunda ka shigo baka kalleni ba?"
Turab a ransa yace " ina na isa? Nima ai mai laifine tunda nima na b'oyema sirrin nan "
Katsemai Tunaninsa yai da cewa " na aika abin bukatu na lefen."
Kansa na kasa yace "to, angode."
Mamaki ya kama mai martaba yace " Umarni sarki zai baka ka d'ago ka kalleshi."
Turab ya d'an runtse ido kad'an sannan ya d'ago a hankalu ya kalli Mai Martaba.
Sarki yace " Turab menene?"
Abu Turab ya kakaro murmushi yai sannan ya girgiza kai yace " ba komai, sai dai jikin Hajiya da ba dadi, ne yasa baza'a kaita asibiti ba a kwantar da ita?"
Ajiyar zuciya yai sannan yace " Hajiya mace ce mai masifar kishin al'adarta, ko sanda za'a kaika asibiti sai datai ta fada wai akan me za'abar maganin hausa a koma maganin bature? Ita ko mutuwa zatai bata yarda a kaita wani asibiti ba."
Turab yai shiru sannan yace " Amma Abba yanayin jikinta ne ba dadi."
Yace "haka ne ni kaina har banasan zuwa dubota."
Turab yad'anyi shiru kafin yace " Ko za'a maidata cikin gari? Sai a tafi nata da masu kula da ita?"
Mai Martaba yace " Turab kenan, nan d'in ba'a kula da ita?"
Kai ya girgiza alamar a'a yace "ba haka bane kawai dai gani nake zatafi jin dadi in tana can."
Sarki ya kura mai ido ya tabbata akwai dalilinsa ma fad'ar haka, sai dai baisan menene ba, yace " shikenan, zansa a maidata a satin nan."
Turab yai saurin cewa " a maidata gobe, dan Allah."
Sarki ya kalleshi yace " Akwai abinda kake b'oyemin ko?"
Turab yai kasa dakai, Sarki yace " na sanka da taurin kai tun kana yaro, jn har bakaso fad'ar abu ba to fa bazaka tab'a fada ba, zanyi yadda kace sai dai ka tabbatar ka sanar dani abinda ke faruwa nan kusa ba da dadewa ba."
Yace "godiya nake, sannan insha Allah zan sanar dakai."
Nan ya mike ya fito.
Hakan kuwa akai washegari da safe a ka d'auke hajiya, wanda ba wanda ya sani sai Turab sai Sarki da masu d'aukan, Jakadiya kuwa sai dariyar mugunta take kasa kasa dan ta tabbata akwai wani abu da Turab yake shiryama Magajiya tunda taga ta zake tana shirya mai lefen auren da tace ko zata mutu bazata bari ayishi ba.
*"*******
A duk bayan kwana biyu Turab suna waya da Bilkisu, shakuwa ce a hankali take shiga tsakaninsu, duba da yanayin gidan da suka taso da kuma aminta ta yarda dake tsakaninsu.
Magajiya ta shiga tashin hankali, ta rasa wannan yarinyar wato Zakiyya sannan an d'auke Hajiya wanda ba wanda yasan inda aka kaita, da farko ta aika gidan cikin gari sai dai bata nan, shikansa Turab baisan inda Mai Martaba ya kai ta ba.
Sai dai yasan Sarki ya fahimci Uwarsa na cikin