Showing 21001 words to 24000 words out of 146065 words

Chapter 8 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

Sai yamma lis suka isa garin na Zariya.


Basira bayan sun sauka ta kalli Lantana tace "zaki iya gane gidan da na fara zama?"


Kai ta kada mata alamar eh, ta d'aura da cewa "sosai kuwa."


"Can zamu wuce."


Ba tare da tambaya ba Lantana ta amsa da to, Abu Turab ya rike sandarsa kamar yanda mahaifiyarsa ta umarceshi, dayake dama idanta a bud'e yake tarau a da d'in ma sai ance miki baya gani tukunna dan in kika ganshi haka bazakiyi tunanin rashin ganinsa ba.




Haka sukai ta tafiya har suka isa gidan, dan ma ba nisa sosai.


Suna isa suka karasa bakin kofar da fadawa biyu ke gadinta, Lantana ta kallesu sannan ta musu gaisuwar da take nuna alamar a masarauta take, sannan ta d'aura da cewa " Matar Mai Martaba ce Gimbiya Basira."


Kallan juna sukai alamar basu fahimta ba, dan kuwa su basu santa ba, ba'a dade da kawosu nan ba, sannan ko da ace ma sun santa ai shekarun dayawa dan kuwa mutane dayawa sun manta da ita, wasu sai da insun tunata susa dariya, wasu kuwa suyi tunani ko tana raye?


Basira ce ta kallesu tace " bud'e mana, shiga zamuyi sannan d'aya ya zauna dan ya tabbatar da mudin ba da wani nufi mukazo ba, sannan d'aya yaje Fada ya sanar da Mai Martaba yayi baki na sirri anan."


Kallan mamaki suka mata, Basira ta kalli na hannun dama tace " naga kamar kai bazaka iya mana komai ba in ma munzo da wani nufi ne, ganin yanayinka, dan haka so nake kaje ka samu sarki in ba hali ka samu Barde kace ya sanar da Sarki a kwai bakin sirri a gidansa na cikin gari."


Kallanta yai yana kokonto, Basira tace " kada ka kuskura ka sanarma kowa sai mutanen nan biyu, ganin kafin kaga Sarki abin zai zama mai wuya ina shawartarka ka sanarda Barde, kada ka fadama kowa inba shi ba."




To, ya fada yanzu kam ya fara yarda da sunsan mai Martaba duk da dai bai yarda matarshi bace sai dai gani kamanni iri na Abu Turab yasa ya san tabbas akwai hadin jini na sarki a jikinsa.


Nan yaja d'ayan yace "ka kula dasu kafin naje na dawo."


Nan ya fara tafiya, sukuma suka shiga ciki.


Suna shiga Basira tasa d'anta yai wanka sannan ta bashi rigar data taho mai da ita kala d'aya.


Itama wankan tai Lantana ta d'auko mata kaya tasa, dan kuwa dana akwai ajiyayun kayayyakin datai amfani dasu.


Nan Lantana ta shiga kitchen dan sama musu abin ci.




**********




Bafaden nan ya dade kafin ya samu ganin Barde nan ya sanar dashi sakon, mamaki ya kamashi bakon sirri? Ya kalleshi yace "sanar dani abinda ya faru tundaga farko."


Nan ya kwashe komai ya fad'amai sai dai ya manta sunanta shidai yasan ance matar sarki ce sannan yaganta da yaro."


Barde mamaki ya kamashi yace "shikenan koma gidan zan sanar dashi."


Har Bafaden ya juya Barde ya kirashi, ya karaso da sauri, Barde yace " yaron shekararsa nawa?"


Kai ya girgiza alamar rashin sani sannan ya dora da cewa "bazai wuce dai shida ko bakwai ba."


Gaban Barde ne ya fadi sai dai yai saurin girgiza kai a fili yace " bazai kasance ita bace kar na tadama Mai Martaba hankali."


Bafaden na tafiya shima ya koma fada, ko minti goma baiyi ba magrib tai, nan mai Martaba ya mike aka shiga takamai baya fadawansa.


Turakarsa ya shiga, yana kokarin shiga makewayi dan kama ruwa da alwala jakadiya ta fara sallama.


Amsawa yai tare da cewa " ya akai?"


Ta kalli Zagi sannan ta kalli Barde tai kasa dakai tace "Barde ne ke neman iso Ranka ya dade, a gafarceni."


Mamaki ya kama Sarki ganin Barde baya biyoshi, nan yai gyaran muryar dayake nuna alamar ya shigo.


Nan tace "Godiya yakd Takawa."


Nan ta kalli Barde tace " bismillah."


Barde ya bud'e kofar ya shiga, a zaune yaganshi nan ya karasa ya zauna a kasa kansa na kasa yace "Tuba nake Takawa na katsema lokacin al'amuranka."


Mai Martaba ya kalleshi yace "ya akai?"


Barde yai dan huci yace "wai baki ne na sirri suke jiranka a gidanka na ciki gari."


Cikin mamakin zancen yace " na sirri kuma? Me kake san cewa?"


Barde ya kwashe komai shima ya sanar dashi, a zabure ya mike yace " Barde Basira ce! Basira ce."


Barde yace "Mai Martaba kayi a hankali kasan bangon gidan sarauta akwai ji (azancin magana yai - yana nufin ya kula akwai masu lab'e.)"


Sai alokacin hankalin Sarki ya dawo dan jin ance Basira ba karamin tadamai hankali akai ba, cikin murya kasa kasa yace " ka shirya ka fara zuwa gidan ni zansan yanda zanyi na fito."


Barde yace "an gama Takawa."


Su Jakaddiya kuwa an baje kunne ana san jigo gulma ko dayake ba ita kadai ba wasu fadawan ma hankalinsu duk yana d'akin, sai dai ba wanda yaji me akace sai dai sunji kamar an ce Basira kamar kuma Barira kamar dai wai suna ake fada da ya fara da Bas, abinda yasa ba wanda yai tunanin Basira saboda ganin tsawon shekarun, na farko shikansa sarki ba kiran sunanta yake ba bare suyi tunanin wani abun.




**********




Mai Martaba kam wasu kayan yasa a jikinsa ana sallah ya samu ya wuce tare da bafadensa na kusa, sannan ya umarci d'ayan akan yace ya koma turakarsa ya kwanta sakamakon kansa dake sarawa.




Sun samu sun isa gidan tun a hanya yaketa add'ua akan Allah yasa sune.


Bayan ya shiga cikin gidan ya nufi kofar ya sa hannu kamar zai murd'a sai kuma ya fasa, karatun qur'anin dake tashi ya tsaya ji, can ya daure yai sallama, Basira tana zaune akan sallaya tanata addu'a akan Allah ya bata ikon shanye komai ya kuma sa komai yazo da sauki.


Abu Turab na gefenta yana karanto suratul Rahman cikin kira'arsa mai dadi.


Shiru Mai Martaba yai yana sauraron karatun.


Gaban Basira ne ya fad'i jin sallamar muryar da ta kasa b'ace ma kunnuwanta, mikewa tai a hankali tazo bakin kofar ta bud'e gabanta nata fad'uwa.


Kallan juna suka shiga yi cikin tsananin kewa da tausayama juna, a hankali hawaye ya zuboma Basira, Mai Martaba ya sa hannu ya riko nata hannu jin yake kamar a mafarki, ba shakka muryar d'ansa ne kenan yake karatu? Hakan yasa ya kamo hannunta ya shigo inda take a tsaye.


Cak ya tsaya yana kallan yaron dake zaune kan sallaya yana karanto Suratul Rahman cikin kira'arsa mai dadin gaske, zuciyarsa ce ta karye ya juyo ya kalli Basira sannan ya nuna yaron da hannu ya kuma nuna kanshi da hannu alamar ( wannan nawa ne?)"


Hawayenta ne ya gangaro sosai ta kada mai kai tana zubo dasu kamar ana zugo kukan.


Sakar hannunta yai ya karasa inda yaron yake a hankali dan jikinsa duk ya gama mutuwa, Zama yai a gaban yaron kan sallaya, Abu Turab ya kura mai ido amma bai daina karatunsa ba, yana kallansa.


Hannayensa Sarki ya kamo,hakan yasa yai sadakallahul azim.


Sarki yace "ya sunan ka?"


Ko kifta ido baiyi ba haryanzu yace "Abu Turab."
Kalla. basira yai cikin jin dadi.


Sannan ya nuna kansa yace "ka gane ni?ah ba haka zance ba, kasan ko ni waye?"


Tunowa da alkawarin dayama Mahaifiyarsa yasa yad'an kalli gefe kad'an ya girgiza mai kai alamar a'a.


Sarki yace "ina dama zaka sanni? Ni kaina sai yau na tab'a ganinka."


Kai Abu Turab ya sake girgizawa yace " ba haka nake nufi ba, ba na gani ta ina zan ganeka?"


Basira wacce ke tsaye tsoro duk ya kamata ganin yanda d'an nata ya kurama mahaifinsa ido ta d'auka ya manta alkawarinsu sai dai jin abinda yace yasa tau ajiyar zuciya.




A zabure ya kalli Basira, ganin yanda idanunsa sukai yasa ta daure ta d'agamai kai tana hawaye tace " tun yana jariri idanunsa basa gani."


Zuciyar Sarki ta kara karaya jiyake kamar ya sa kuka, da sauri ya jawo d'an nasa jikinsa ya kankameshi kam.


Sundade a haka kafin ya sakeshi.




Shiru ne ya biyo baya a d'akin, yana zaune kan kujera rike da hannun matarsa ya d'aura d'an nasa kan cinyarsa.


Basira ta kalleshi tace "in wani ya ganka fa?"


Murmushin yake yai ya shafa kan d'an nasa yace " duk laifinane, da bance kije gida ba d......."


Kai tai saurin girgiza mai tace " ko kad'an ba kaifinka bane."
Kallanta yai sai dai baice komai ba..


Sun d'anyi shiru kafin Basira ta kalli d'anta tace "koma can ka zauna zamuyi magana da mahaifinka."


Nan ya mike ya koma can gun 'yan tumtum ya zauna sai dai hankalinsa na kansu.


Jiyai Mahaifin nasa yace " basira ina kuka shiga?hankali na yayi matukar tashi."


Murmushi tai tace " ka yafeni nasani nayi babban laifi sai dai ba komai bane ya hanani dawowa sai d'ana, ina tsoron rayuwar da zaiyi a gidan sarauta ba ido, ina tsoron wulakanci da gulma da habaici da zai fuskanta, nafarko ni ba wata mai matsayi ba sannan ga d'ana ba ido, tsoron wulakancin da za'amai yasa na kasa dawowa, sai dai tunanin raba d'a da mahaifi da kuma raba kaina da kai yasa na dawo."


Tunda ta fara magana yake kallanta yauce rana ta farko da ta saki jiki take mai magana haka, murmushi yai sannan yace " na fahimcike na kuma gode da kika dawo gareni baki bari na mutu banga d'ana ba."


Shiru suka d'anyi kafin yace " ku zauna anan in har kina ganin zaman can zai ma d'ana wahala."


A ranta tace da kenan, yanzu in har na zauna anan wayasan me zasumin a bayan idanka?ai in kana tsoron kura ba inda yafi maka saukin zama irin raminta, domin duk abinta bazata taba kawo akwai wanda ya isa shigar mata rami ba bare tai farauta a ramin nata.


Murmushi tamai sannan tace " a'a nafisan zamana kusa da kai sannan in na zauna anan yaushe Abu Turab zai dinga ganinka? Sannan in akaji labarin zamana anan baka gani xai jawo ma da ni kaina matsala?




Kallanta yai yana kara mamakin yanda ta canza.........






*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)





*HASKE WRITERS ASSOCIATION*


*Wattpad :-AyusherMohd*



*Na Ayusher Muhd🤸🏼*




*15*




Mai Martaba ya juya ya kara kallan d'an nasa zuciyarsa a raunane, ba shakka kam d'ansa na bukatar kulawa ji yake kamar laifinsa ne yasa yaron ya makance.


Basira ganin yanda yake kallan d'an nasa yasa tace " Ba laifinka bane, kaddararsa ce babu makawa sai hakan ya faru ko da kuwa a gunka muke."


Kai ya jinjina cikin tausayawa, tai murmushi tace " ka koma tun kafin mutane su farga da rashinka."


Yace " haka ne, kiyi hakuri zuwa wasu 'yan kwanaki zan san yanda zanyi ku dawo ba tare da mutane sunyi zargin komai ba."


Ta lumshe ido sannan ta murmusa tace " na yarda dakai."


Mikewa yai a hankali yaje kusa da d'ansa ya rungumeshi kam sannan yace "sai da safe d'ana."


Abu Turab ya d'aga kai.


Haka ya fito tana bayansa, a tsakar gida taga Barde nan ya gaidata sannan ta juya ciki, su kuma suka tafi.


Abu Turab ya matso inda take idanunsa fal kwalla sai dai ya rasa mai zaice, ya kuma rasa dalilin jin yana san yai kuka, kallansa tai tace " me kake shirin yi?"


Yad'iye kukan yai sannan yace " bakomai."


Ta mike ta wuceshi ta nufi cikin d'aki, zama yai dabas yanzu yana ganin mahaifinsa ba dama yace ya ganshi?


Shikam ya kasa gane mai mahaifiyarsa take nufi da hakan.


*********


Sarki ya kasa bacci sam sai juyi yake akan gadonsa, tayaya zai b'ulowa mutane da matansa? Mai zai fada wanda mutane bazasuyi zargi da korafi ba akan matarsa da d'ansa? Sam ya rasa amsar tambayarsa sai juyi kawai yakeyi.


*********


Washegari da sassafe sarki yasa bafaden nan nasa ya tuko mota ya kawo musu kayan abinci sosai, duk wani abun bukata ya kawo musu sannan ya aiko da kudi akan a siyoma Abu Turab kaya da wasu abubuwan bukata.


Wajen karfe 10 suka shirya itada Lantana da Abu Turab suka fito dan zuwa kasuwa siyo kaya.


Suna tafe suna 'yar hira itada Lantana jikin wani shago ya tsaya dan shi sam bayasan shiga mutane da alama hakan ya faru ne saboda inda ya taso.


Yana wajen shagon su kuma sun shiga ciki, kallan wata kantanga yake wacce akai mata zane da wasu rubutu wanda bai taba gani ba, ido ya kurama rubutun yanasan sanin namenene?


Wasu yara ne su uku suka fito daga ciki sanye da fararen kaya riga da wando da hijabi, basu wuce shekara 5 ba, su biyu ne mata d'ayan kuma namiji ne.
An tashi tara.


Suna tafe kamar masifa biyun babbar macen da namijin, d'ayar wace take karama itakuma da alama kuka takeyi, kura musu ido yai yana neman amsar tambayarsa, daga ina suke hakan?


Wata ce yaga ta fito da gudu 'yar karama bata wuce shekara hud'u ba, daga inda suka fito tazo ta d'akama babbar cikinsu duka ta kara zurawa da gudu, inda yake tsaye take yowa mamaki ya kamashi ya tsaya yana kallan ikon Allah, yana nan tsaye yaga tana nufoshi shi dai bai matsa ba sai kallan ikon Allah yake.


Da gudunta kuwa ta cigaba, kai ya girgiza ya juya ya kalli inda Mahaifiyarsa take, yana juyawa yaji an wani irin hankad'eshi iya karfinta, dukansu suka fad'i a kasa tim, shikam ya fita jinjiki dan sar da hannunsa na hagu ya kurje, cikin fad'a ya d'ago dan ya mata magana, mamaki ne ya kamashi ganin ko a jikinta kad'e jikinta tai tana shirin kara sa wani gudun.


Da karfi yasa hannu ya fizgo hijab d'inta ya dawo da ita inda yake.


Kallansa tai sannan ta kalli wacce ta daka tace " dan Allah yahkuri ka sakeni karta kamani."




A ransa yace wasa kike yarinya, saurin kauda kansa yai daga kallanta sannan yace " malama bakya gani ne?"


Kallansa tai taga yasa hannu yana neman gefenta yana jujuyawa kamar irin neman inda fuskarta take yakeyi.


Kusa da fuskarsa ta matsa ta kalleshi sannan ta mai gwallo, ganin baice komai ba yasa tasa hannu ta toshe baki tana dariya wato da alama baya gani.


Hannu tasa ta fara kokarin zare hijab dinta alamar zata cire hijab din ta gudu ta barshi, jitai ance " me ya faru Abu Turab?"


Kallan matar datai magana tai ta ciji leb'e cikin takaici ga waccan ta karaso daf, ganin yana neman sanar da matar yasa ta fizge hijab dinta iya karfinta, ta sakar mai gwalo tace "makaho kaje ka nemo sanda."
ta kara falawa da gudu kamar zata kifa.


Juyawa yai yana kallanta cikin takaici, yanaji d'ayar tana binta tana cewa " Mariya wlh ko me zakiyi sai na rama gwarama ki tsaya."


Daga can itama ta juyo ta jefo mata dutse tace " ki kamani in kinada karfi."




Yaja tsaki yace " Umma amma waccan batada hankali, bigeni fa tai kiga yanda naji ciwo amma ko hakuri bataban ba." yakarasa maganar yana nuna hannunsa.


Basira ta matso ta duba hannunsa tace " da alama daga makarantar boko suke amma wannan yarinyar kwai fitinaniya, kaga yanda taketa gudu ko ajikinta?"


Abu turab yai kwafa ahankali yace " Allah yasa inganta watarana."


Basira tace " me kace?"
Kai ya girgiza yace bakomai.


Lantana tace " inba dan yanayi ba inama ta isa ta ganka a haka? Bare har ta tureka?"


Basira tace " muje nikam."


Sun gama siyayarsu sannan suka koma gida, Abu Turab sai dayaga sunyi salla sunci abinci sannan yace " Umma menene boko?"


Tace " makarantace da ake koya karatu, menene?"


Kai ya girgiza alamar ba komai.


Kallansa ta sakeyi tai murmushin dan ta fahimci abinda yake nufi.




A waccan lokacin ba kowa bane ya damu da karatun, yawanci zakaga yara ba zuwa suke ba, wasu kuwa iyayensu ne malaman makarantar, wasu kuma turasu ake bawai dan sai sunyi karatun ba.


*********




Magajiya zaune a kilisarta tanacin inibi, gefenta d'antane Yarima yana zaune kusa da ita shima yanacin ayaba, ta kalleshi sannan ta kalli Jakadiya dake zaune tace " jiya ina Mai Martaba yaje?"


Jakadiya tace " ba inda yaje."


Wani kallo Magajiya ta mata tace " me kikeso kice?karya na miki ko me?"


Dasauri ta rusunnar da kai tace " tuba nake Magajiya ni kaina bansani ba daga gun sallah ne bai dawo ba."


Ta bud'e baki zatai magana wata yarinya yar shekara hud'u ce ta shigo da gudu ta zo ta fad'a jikin Magajiya.


Fara'a ce ta karfafa a fuskarta ta d'agota tace "wa nake gani haka kamar uwata?"


Yarinyar ta d'ago tana murmushi tace " nice Aunty."


Kallan d'an Auntyn nata tai wanda ke zaune ko kallanta baiyi ba, ta taboshi tace " Yaya bakaganni bane?" Kallanta yai yace " Yaushe zaki girma ne Khadija? Sai ki dinga gudu kamar wata....."


Magajiya ce ta katseshi tace " a mata afuwa Yarima yarinya ce, sannan na tabbata inta ganni ne take haka ko Uwata?"


Baki ta turo sannan ta d'aga kai.


Magajiya na tsananin san Khadija wacce take 'yace ga Hisham, wanda yanzu 'ya'yansa hud'u itace ta uku, duk da dai 'ya'yansa a matsayin uku suke tunda ba wanda yasan Abdulmajid d'ansa ne.


Har mamaki mutane suke yanda ta sakar ma yarinyar fuska, ko dan sunan mahaifiyarsu ne?


Haka ta sa Khadija a kusa da ita tana tambayarta 'yan gida da karatun ta.


Jakadiya kam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login