Showing 30001 words to 33000 words out of 146065 words

Chapter 11 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

murmushi tamai tace " yanzu zan dawo Yaya, in na dawo zan cigaba da baka labarin."


Kai ya d'aga mata alamar to, kusa da shi ta dawo da sauri ta kura mai ido, kallanta yai tare da saurin d'auke ido, tace "wani sa'in sai inga kamar kana gani."


Fuska ya d'an hade yace " zaki fara ko?"


Dariya tai tace "karka damu yaya a kullum in nai sallah addu'ar da nakeyi kad'ai kenan 'Allah ya baka lafiya ka dinga gani.'


Fuska ya saki yace "dafatan ba ita kadai kikeyi ba? Addu'ar nake nufi."


Mikewa tai da sauri ta fara tafiya, hannu yasa ya riko hijab dinta ta fizge da karfi sai dataje kofa tace " ita kadai nakeyi."
Tai saurin tai waje.


Dariya yad'anyi tare da girgiza kai, ba shakka Khadija itace take d'ebe mai kewan zaman kad'aici, dan ko sharri akamai ko aka b'atamai rai inyazo ya zauna a d'aki shiru ita ce ke zuwa gunsa, bazatace komai ba sai dai zata zauna kusa dashi harsai taji ya fara mata magana, ya rasa menene dalilin dayasa mahaifiyarsa ma zancenta kenan akan ya rage kula Khadija, ko Lantana ma wani sa'in sai yaji tace " Uban gidana ka rage sa Khadija a ranka."


Bai tab'a tambayar dalili ba dan kuwa yasan ba mai fadamai, kuma yana tunanin dan tana 'yar yayan Magajiya ne yasa ake fadamai haka.





A can kuwa Khadija na zuwa aka sa ta amota, mamaki ya kamata ta kalli Mamanta tace " ima zamu?"


Rufo kofar motar Hisham yai sannan ya kalleta ta yace " ki koma kano gun kanwar Mamanki ki zauna acan, kiyi karatu, inkinyi hankali nida kaina zanzo d'aukanki."


Ihu ta saka tace "itakam bataso abarta anan, gub Ya Turab."


Tana ihu tana kuka aka ja mota akai gaba, kuka take sosai harda shesheka, sai dai Mahaifiyarta kawai ta jawota jikinta ta kwantar.


Tana kuka har bacci ya d'auketa, bata farka ba sai da akai parking a kofar gidan.


Da kuka ta shiga gidan.


*******


Haka rayuwa ta kasance tun Turab na jiran Khadija kwana d'aya, biyu ba labari, nan ya fara tunanin ko batada lafiya ne.


Satar jiki yai ranar datai kwana hud'u ya fito, tunani ya fara ta inane ma inda zaije shidai ba yawo yake ba, ga gidan katon gaske, yana tsaye yana tunani yaji anzo tabayansa ance woo da karfi akai wanda sai daya d'an tsoratashi ya juyo da sauri ganin Mairo ce ya had'e rai tare da dauke ido daga kanta, hannu takai kamar zata dakeshi ta makamai harara tace a hankali " nima ba farincikin ganinka nake ba."
Fuskarsa a had'e yace " kinga Khadija?"


Bakibta tab'e tace " khadija?"
Sai kuma tasamai dariya tace " niban ganta ba."


Kallanta yad'anyi kamar ya tambayeta inda zaije yaganta sai kuma ya fasa, Mairo tace "la ga Yayanta nan zuwa ka tambayeshi."


Juyawa yai da sandarsa zai koma, jiyai Abdulmajid yace " Abu Turab."


Cak ya tsaya ba tare da ya juyo ba, Abdulmajid ya karaso inda yake, ya mai wani kallo na sama da kasa yace " kana d'an sarki menene dalilin fitowarka kai kadai?"


Abu Turab ya kalli gefensa baice komai ba, Abdulmajid yacigaba" in har kanada ido ma ba wani abin amma kana makaho ka dinga yawo kai kadai?"
Ba kalmar daya tsana irin a dinga cemai makahon nan, Mairo dake tsaye ta kalli Abdulmajid dan dama ba kunya gareta ba tace " yau naga ikon Allah, wani inyaji kana fadar haka daukama zaiyi ka damu dashi."


Abdulmajid ya maka mata wani mugun kallo yace " ke kuma uban waye ya sa bakinki?"


Tab'e baki tai tace " wai da...."
A hankali tai maganar, sai dai yajita, juyowa yai ya kalleta yace " wlh kika batamin rai bakeba har ubanki sai na sa an hukunta."
Baki ta murguda kadan tace "badai nawa uba...."

Abu Turab yai saurin daka mata tsawa yace "ke Mairo!"
Idanu ta zaro dan sosau ta tsorata, yace wuce ki tafi gida.


Kallansa tai batace komai ba tai gaba, yauce rana ta farko da taji bazata iya maida murtani ba akan fadan da aka mata.


Tana tafiya Abu Turab ya juya zai tafi, kafa Abdulmajid yasa mai ya kifa kuwa tim.


Kasa duk ta shiga bakinsa, Abdulmajid ya matso da sauri ya kama hannunsa yace " tashi sannu, kaga irinta ko? Yanzu dan Allah yasa ina nan ne da bamai d'agaka."


Mamaki ya kama Abu Turab, sai dai ya daure ya mike ya kade jikinsa baice komai ba ya juya zai tafi.


Abdulmajid yace " Khadija fa? Badai cemin zakai ita ka fito nema ba."




Abu Turab baice komai ba.
Abdulmajid yasa dariya ya dawo gabansa yace " duk amintar ku bata fadama zatai tafiya ba?"


Abu Turab yad'an juyo inda yake, Abdulmajid ya dan dafashi yace "yaro man kaza."


Baijira mai zaice ba ya juya ya tafi.


Jikin Turab ne yai wani mugun sanyi a hankali ya dinga tafiya har ya isa b'angarensa dan yanzu an fitomai da kofa daga b'angaren Basira.


Yana shiga yaga Mahaifiyarsa a tsaye a tsakar gida, ga bayinta da nashi duk a tsatsaye.


Da alama fada take musu, jin bude kofa da shigowarsa yasa duk suka kuramai ido.


Wani mugun kallo tamai ta kallesu tace " ku bamu gu."


Nan kowa ya juya ya fita, Lantana kam jiki a sanyaye ta fita dan tasan Ubangidanta yayi laifi.


Basira tana matsowa ta wanka mai mari.


Hannu yasa a gun bai d'agoba kansa na kasa, cikin kuluwa tace " gidan ubanwa kaje? Sau nawa ina cema karka fita kai kadai?"


Kansa na kasa yai gum da baki.


Ta kalleshi dan tasan bazai magana ba, ita kanta tayi dana sanin marin nasa sai dai itakam tana tsoron abinda za'amai in aka ganshi shi kadai, balle yanzu dataga gefen kuncinsa kasa ta tabbata wani abun ne ya faru.


Juyawa tai a harzuke tai waje.


Abu Turab ya tsugunna a gun idanunsa suka ciciko, ga jin khadija tayi tafiya, ga bakincikin Abdulmajid, gashi ya b'atawa mahaifiyarsa rai.


Lantana ce ta dawo ta d'agashi ta shiga dashi ciki, a wannan ranar kam Abu Turab sai daya zubda hawaye.




***********


Tundaga wannan rana komai na rayuwarsa ya canza, magana wannan sai ya zamarmai dole yake yi, kullum yana b'angarensa, rayuwarsa ta koma ta da, sai dai ko makarantarsu ko kuwa inya fita gaida Mai Martaba ko Magajiya.


A makaranta ne dai Mairo take dan mai magana bayan ita kuwa kaf ajin daga gaisuwa ba abinda ke hadasu da kowa.
Tun randa ya ma Mairo tsawa kuwa ta rage rainashi, sai tausayinsa ma data darayi, gashi yanzu ya canza kullum fuskarnan tasa ba fara'a.


A kwana a tashi ba yuwa yau gashi Abu Turab ya cika shekara 22.


Yau an tashi a gidan Sarki anata shirye shirye sakamakon hawan Sallah na karama da za'ai.


Zaune yake a d'aki ya saka kayan da aka aikomai inji Magajiya wai ya saka, tunda ake hawan sallah Abdulmajid ne kadai yakeyi, amma wannan sallar wai ta aikomai da kaya akan shima zaije hawa.


Murmushi ya saki sannan ya d'aga kayan sama ya tabbata akwai wani makirci da aka shirya mai.


Yana nan azaune yaji ana kwankwasa mai kofa.
Mikewa yai ya tako yazo ya bud'e.


Mahaifiyarsa ce hakan yasa ya matsa mata ta shiga ciki.


Zama tai a bakin gado sannan tace " akacemin an aikoma da kayan hawa?"


Kai ya d'an jinjina yace " gasu can."


Kallan kayan tai sannan tace " Turab amma dai....."


Murmushi ya mata yace " zanje."


Kallan mamaki tamai tace " baka tunanin so take a mutanen gari su fahimcu baka gani? Ko kuma wani abun sukama dokin kaje ya yarda kai mutane su gane baka iya doki ba? Sannan su fahimci makantarka?"


Idanunsa ya d'an rufe kadan sannan yace " Umma."


D'agowa tai ta kalleshi yace " har sai zuwa yaushe ne zan nunama mutane ina gani?"


Kallansa tai tace " Abu Turab!"


Yacigaba " Wani irin tsoro ne damu da haryanzu bamu cireshi a ranmu ba? Kina tunanin wannan tsoron namu akwai inda zai kaimu?" bai jira amsarta ba ya cigaba "a'a, wannan tsoron haka zai cigaba da dawammar damu a inda muke ba tare da mun tsinana komai ba? Na sha wahala tun ina yaro har zuwa wannan lokacin, har sai yaushe ne zamu kwaci 'yan cinmu? Har sai yaushene zaki bari d'an da kika sha wahala akansa zai sama miki farin ciki?"


Kallansa take yi cikin tausayawa da tsananin kauna.


Hannayenta ya kama yace " na gaji da wannan tsoron, nifa namiji ne, jinin mahaifina haka kuma d'a gareki, haka kikeso incigaba da zama? Ana nuna ked'in ba kowa bace balle ni? Bayan kuma ni nasan ked'in mace ce wacce kaf duniya a gurina banga kamarta ba?"


Idanunta ne suka dan tara ruwa kadan, kai ya girgiza mata yace " tun ina d'an yaro kika haneni da ragonta da kuka, Umma kina tunanin Mai Martaba shine zai kwatar mana 'yancin mu?"


Kallan mamaki tamai, kai ya girgiza yace " ko kad'an in har kina tunanin wannan ki cire a ranki, Mai Martaba sarki ne, sarkin mutane masu dumbun yawa wanda yake mulkarsu sai dai ba sarki bane a tsakanin matansa, Magajiya bazata taba barinsa yai yanda yakeso ba akan matansa, yaci ace a shekaru goman nan kin fahimci haka."


Murmushi tai sannan tace "nasan da haka Abu Turab sai dai ina tsoron karmu lakutowa kanmu abinda gaba bazamu iya magani ba."


Dariya yai sai dai mai dan sanyi, wanda rabon dayai dariya haka ya dade yace " ina Umma na ne wacce take tsaidani in nai laifi? Ina Umma nane wacce take hanani kuka? Ina Umma nane wacce ke marina duk sanda na b'ata mata rai?"


Harara ta makamai tace " da alama girma ya fara kama wannan Umman taka."


_Nikaina sai da na saki wata bazawarar dariya....Lol_




*TEAM ABU TURAB🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)






*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*






*Wattpad :-AyusherMohd*



*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*




*21*




Shiru tai tana tunani, kayan da aka aikomai dashi wanda ke kan gado ya d'an kura ma ido alamar tunani kafin ya dawo da kallansa kan mahaifiyarsa yace " Umma zan shirya."


Kai ta d'aga sannan ta mike ta dafa kafadarsa d'aya tace " duk hukuncin da ka yanke ina tare da kai dan kuwa na tabbata d'ana bazai bani kunya ba."


Bata jira amsarsa ba tai waje.

Abu Turab ya shirya tsaf ya fito daga d'akinsa, inda yake zama ya wuce dan bayin sa su nad'amai rawani.
Tunda ya shigo suke kallansa dayake sunsan baya gani yasa suka kura mai ido kowa da abinda ke ransa nan fa suka dan fara gulma da ido wanda duk yana ganinsu.


Rawanin dayake so ya basu nan suka nad'amai, ya sa takalmi yace su tafi.

A kofar gida yaga wani bawa rike da doki yasha ado, bawan na ganin Abu Turab ya taho da gudu ya dan rusuna yace " Ranka ya dade ha doki nan inji magajiya."


Murmushi yai sannan yace " ayya? Ya za'ayi? Gashi na riga na aikama Barga akan ya aikomin doki sai dai ma maida wannan gun Bargan gudub kar a maka fada akan rashin isar da sakonka da wuri.


Bawan yai saurin sunkuyawa yace "Tuba nake D'an Sarki."


Abu Turab yai murmushi sannan yace " ba haushi naji ba ina dai gujema fada ne."


Kallan d'aya daga cikin bayinsa yai yace " sanar da Barga ya baka dokina."


Cikin mamaki yace " Ranka ya dade ai ba'a mai....."
Katseshi yai da cewa " hakan nakesansa."


To, abinda ya fada kenan yai saurin fara tafiya.




Bai dade ba sai gashi da rike da dokin Abu Turab ya hau.


Sai daya bari Sarki zai fita hawa sannan ya shiga cikinsu, bai bari sun ganshi a gida ba.


Tunda ya shiga cikinsu kuwa ake kallansa, kowa mamaki wannan wanene haka?


Dama tawagar Abdulmajid ya shiga, dan kara gudun dokin yai ya matsa bayan Abdulmajid kadan.


Nan fa kowa ya fara kallansa, mutand sai juyowa suke ana nunashi da hannu, ganin yanda ake nunuwashi yasa Abdulmajid ya tsargu ganin saitinsa ne.


Kallan na kusa dashi yai yace " menene?"


Juyawa yai shima, cikin mamaki ya kalli Abu Turab sannan ya matso inda Abdulmajid yake yace " Yarima ai kaninka ne yake bayanmu."


Murmushi yai dan dama yasan da zuwan nashi, sunyi shiri sosai dan kuwa d'inki Magajiya tasa aka mai irin wanda zai saka a wannan ranar, wanda hakan sab'awa ne ga al'adarsu ace anyi anko da Sarki balle kuma bai sani ba.


Ya sake murmushi tunawa dayai dokin ma kwalliyar irinta Sarki sukasa akamai.


Sai yanzu ya fahimci dalilin dayasa ake nuna Abu Turab.


Sai da sukaje inda Sarki zai d'an tsaya kafin ya juyo alokacin ne Abdulmajid yaga yanda ake ta nuna Abu Turab, dariya ya kunshe ya juyo dan ganin yanda ma kayan yamai.


Sai dai me????


Idanu ya zaro sosai cikin tsananin mamakin abinda idanunsa suka ganemai, me ke faruwa? Menene hakan?


Shi kansa Sarki ya fahimci yanda mutane suke nune nune, hakan yasa ya tambayi Galadima yace " meke faruwa?"


Nan Galadima yasa aka bincika.
Matsowa yai wajen kunnen Sarki ya rad'amai.


Ransa ya b'aci sosai nan ya bada alama akan su juya.


Haka sukabi har suka koma gida.
Abdulmajid kam sukuku ya karasa wannan hawan zuciyarsa tana ta san taga wani irin hukunci Mai Martaba zai yankema d'an lelen nasa.


Suna isa akazo aka sanar ma Abu Turab akan Mai Martaba na nemansa a fada.


Yasan za'ai haka shiyasa ya sauka zuciya d'aya ya bada dokinsa ya nufi fadar.


Dayaje zai shiga sai ya ajiye sandarsa sannan ya shiga ciki.


Zama yai irin zaman gurfana d'in nan, Mai Martaba ya kalli dumbun manyan mutane masu mukamin sarauta dake gun, sai dai wannan karan yazamarmai dole duk san da yakema d'an nasa ya mai tambaya a nan Saboda yau a matsayin Sarki yake ba uba ba.


Abu Turab ya kalla fuskarsa a had'e sosai yace " Me zaka fad'a game da wannan shigar ta cin zarafi dakai?"


Nan fa aka kara kallansa, Abdulmajid wanda ya shigo yanzu yai murmushin jin dadi tare da zama.


Abu Turab yai shiru baice komai ba, kallansa Mai Martaba yai yace " in har bakada amsa akan hakan to lalai ne ka fuskanci hukuncin masarauta."


Ya fad'a tare da kauda kai.


Abu Turab kansa na kasa yace " Tuba nake in har shigar danai laifice a tsarin masarautarmu."


Nan fa kowa ya kara kallansa, rigace ta shadda wacce ta tsufa kana ganinta kasan tsohuwace, sannan na babbar riga a jikinsa ya maka wani tsohon rawani, wannan shigar ko a cikin gida ba yinta yake ba balle a gun hawa cikin jama'a.


Hisham ya kalleshi yace " kanasan kace shigarka batada laifi kake nufi ko me?"


Abu Turab ya kalleshi fuakarsa a sake yace" kuskure nane sai dai ina fatan amin afuwa."


Cikin takaici Mai Martaba yace " Abu Turab! Nasan ba gani kakeyi ba dan haka laifin bayinka ne zasu amshi hukuncin barinka kayi wannan shigar dolene su fuskanci hukunci mai tsauri."


Abu Turab ya kara kasa dakai cikin kalar tausayi yace " ko wani hukunci ne amin domin kuwa sun bani kayan da ya kamata insaka sai dai daga laushin kayan da yanayin su yasa nasan ba nine na dace da kayan ba, sai dai hakan baisa na musa ba na saka kayan dan kuwa bansan ya suke ba da idona, ka gafarceni Mai Martaba ina fitowa aka sanar dani kayan irin naka ne sak, sannan dokinma irin kwalliyarka ne dashi, wannan yasa na hanzarta na janyo kayan dabansan ya suke ba na saka sannan na aika Barga ya bani dokina nasa amaida mai waccan."


Jin kalamansa lalai sun ba kowa mamaki, Abdulmajid kam cikin tsoron kar asirinsu ya tuno yai saurin cewa " menene shaidarka ta fadar haka? Kana tunanin ko me kace yarda zamuyi?"


Abu Turab wanda ana cemai Mai Martaba na kiransa ya tura Salau(mai kula dashi wanda suka fi shiri) akan ya d'aukomai kayan nan,sannan ya aika Barga yazo.


Nan yace " Salau!"
Daga waje Salau ya amsa da karfi.


Nan ya shigo rike da kaya.
Abu Turab yaba shi kuna ya ware kayan anan kowa ya gani, to fa!
Nan aka fara magana kasa kasa.


Abu Turab yace " ka gafarceni Ranka ya dade ba gani nake ba bare nasan da haka."


Barga! Nan ya amsa shima daga waje sannan ya shigo.


Abu Turab yace " wani irin kwalliya ne da dokin danasa a dawom dashi?"


Nan Barga ya musu bayani.


Mai Martaba cikin tsananin mamaki yace " wanene ya aikoma da kayan da kuma dokin?"


Abu Turab yad'an sadda kai tunowa yai da yanda suka karashe da mahaifiyarsa.


Harta fita ta dawo tace " Abu Turab! Me kake san yi dan hankalina bazaj kwanta ba sai naji."


Ya kalleta yace " bazansa kayan ba haka kuma bazan hau dokin ba, na tabbata akwai wani makirci akasan wannan kayan da dokin zanje inga wani irin makircine sannan insan abinyi."


Muryar Galadima ne ya katseshi da cewa " kayi shiru."


Cikin Abdulmajid da Waziri ne ya d'ebi ruwa, tsoro da fargaba ya kamasu, duk suka runtse ido saboda tsoron abinda zai ce.


Abu Turab ya d'ago yace " ina wannan wanda baya ganin zai sani? Tuba nake ranka ya dade sai dai nikaina bansani ba andai aiko ne ance ga kayan dazansa."


Mai Martaba ransa a b'ace yace "dolene abinciko wanda yai wannan laifi dan kuwa bazan laminci irin haka ba."


Abdulmajid ya kurama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login