Showing 24001 words to 27000 words out of 146065 words

Chapter 9 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

ganin haka yasa ta samu ta sulale dan itakam taji dadin ganin Khadija.








************




*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)





*HASKE WRITERS ASSOCIATION*


*Wattpad :-AyusherMohd*



*Na Ayusher Muhd🤸🏼*




*16*




Yau da sassafe kafin Mai Martaba ya tafi bada a aika a kira masa Magajiya.


Zama tai irin yanda ta saba sannan ta kalleshi, ba sai an fada mata ba ta fahimci magana yakesan yi mai mahimmanci.


Ya dade baice komai ba kafin ya ja numfashi yace " Magana nakeso muyi, ko ince abu nakesan fada miki."


Kallansa tai sannan ta maida kanta inda take kallo da.


Sarki ya nisa yace " akwai abinda na b'oye miki ko ince akwai abinda ya kasance sirri na ne da ba wanda ya sani."


Bata juyo ba dan bata taba kawo wani abu ne babba ba, Sarki yacigaba " Matata da d'ana zan maido gidan nan zuwa gobe."


Da sauri ta juyo ta kalleshi tana mamakin kalamansa dan sam bata fahimci ina ya dosa bama.


Sarki ya cigaba da cewa "Matata da ke zaune a cikin gari d'aya daga cikin gidajena, uzuri ne yasa take zaune acan saboda d'an data haifa ya kasance yanada lalura, wanda hakan yasa ta naimi zama acan dan ta kula dashi, ba wai dan tana tunanin nan din bazai samu kulawa ba a'a sai dan lalurar tasa babbace wacce take bukatar kulawa."


Tunda ya fara maganar take bin bakinsa da kallo dan ta kasa aminta da abinda kunnenta ke ji.


Daurewa tai tace " aure kai bamu sani ko me? Nifa na kasa fahimtar inda ka dosa."


Kallanta yai yace " Basira nake nufi da d'ana Abu Turab wanda suke gidana shekara bakwai kenan."


"me kace? Basira da d'anta?sannan suna zaune a gidanka shekara bakwai? Takawa mai kake san cewa ne?"


Mikewa yai yace " ana jira na a fada, sannan na tabbata zakiji abin banbarakwai sai dai gaskiyar kenan." kasa magana tai saboda tsananin mamaki, tana kallo ya juya ya fita.


Shikam ya sani in har ya mata lago lago tabbas sai ta bulomai da wani abun.


Ta dade a zaune kafin Ta mike tai bangarenta.


D'aki ta shiga ta rufe, tafiya ta dinga yi a d'akin cikin tashin hankali, me ke faruwa? Meke faruwa?


Ta dade kafin ta aika a kira mata Hisham.


Hisham kam ya taho ko a jikinsa dan dama yanasan ya mata magana akan a nad'a dansa matsayin Yarima mai jiran gado sai kuma ta aika a kirashi.




B'angaren d'ansa ya fara zuwa, yana shiga yaji alamar fasa abu, da sauri ya shiga ciki hankali a tashe.


Abdulmajid ya gani a zaune ga bayinsa sunsa gwiwowunsu a kasa suna bashi hakuri, a hasale Abdulmajid ya kallesu yace " ba nace banasan a kawomin ruwa a irin wannan kopin ba?"


Hakuri suke bashi hankalinsu a tashe, ya wani juya kai irin ba saukin nan yace " bazai yiwu ba Ummana zan sanarwa ta d'au mataki a kanku."


Nan suka shiga rokonsa, Hisham yai dariya ya juya ya fita yana jinjina kai, murmushi ya saki yace " haka akeso ai, gwara ya nuna musu a kasan sa suke hakan zaisa inya zama Sarki a dinga tsoronsa."




A zaune ya tadda Magajiya sai dai kana kallanta kasan tana cikin tashin hankali, nan Hisham ya d'an tabe baki kadan yace "wa ya tabo wannan zakanyar?"


Kusa da ita ya karasa ya zauna yace " Magajiya menene?"


Ta kalleshi cikin tashin hankali sannan ta bada umarni a basu guri, kallanta yai sannan yai dan dariya yace " menene? Khadija tace a gaisheki."


Hucci ta saki tace "ina amsawa amma ba wannan bane a gaba yanzu, kasan Basira ta dawo kuwa? Ko ince wai ashe tana nan?"


Kallanta yai yace "Basira? Wa ke........" ido ya zari sakamakom tunowa dayai yace " Basira dai?"


Ido ta runtse tace " ita mana, ba ita kadai ba ma harda danta."


Mikewa Hisham yai da sauri yace " ban gane ba? Basira tana nan a ina?"


Magajiya ta kwashe komai ta fada mai, shiru yai sannan ya zauna a kasa dabas ya dafe kai cikin tashin hankali.


Magajiya ta kalleshi tace " naji maganar Mai Martaba sai dai ban yarda da duk abinda ya fada ba."




Hisham yace "ban......"


Tace " kana tunanin Basira tana garin nan shekara bakwai amma sarki bai nuna alama ta zargin haka ba? Ko na fita? Ko na aika abinci ko wani sako?"


Hisham ya kalleta yace " haka ne kuma."


Magajiya tai wani murmushin takaici tace " kwanan nan ta dawo."


"kwanan nan?"
Tace " haka zuciya ta da kwakwalwata ke sanar dani, nasan hali Takawa, nasan yanda yakesan Basira da abin cikinta, na tabbata bazai taba kyalesu ba batare da ya dinga binsu ba."


Hisham yace " gaskiya ne,to yanzu meye nafita?"


Tace "nayi tunani sosai bayan naji abinda yace sai dai nasan babu abinda zamu iya yi, na farko bazamu sa ta koma ba sannan ba zamu kashe danta ba, sai dai akwai kafita."


Hisham ya kara matsowa, Magajiya tace " da farko mu nuna masa ba komai, sai dai ni zan sanar dashi akan in har yanaso in nuna dawowar matarsa ba komai bane har sai ya amince da bukatata."


Hisham yace "kina ganin zai yarda?"
Tai wani murmushi tace " yafi kowa sanin in na tsani matarsa zaman gidan nan gagararta zaiyi hakan zaisa ya yarda."


Hisham ya kata jinjina yace " haka ne, amma meye bukatar taki?"


Tace " ya rubutamin alkawari akan ba mai gadar sarautarsa sai Abdulmajin wato d'ana."


Hisham ya washe baki yace "kai Magajiya da ke namiji ce tabbas da kin taimaki kasar nan da kwakwalwarki."


Kai ta juya tace " sannan basai na damu da d'anta ba tunda yace min yanada lalura duk da banmasan lalurar menene ba."




Hisham yace "lalura?"


Ta tabe baki tace "oho musu sai dai dolene muyi amfani da dawowar yarinyar nan mu amshi takarda a hannun sarki.


Murmushi sukai na farincikin ganin sun warware matsalarsu....


_Nikam nace hmm ba giringirin ba dai........_




**********


Mai Martaba ya sanar a fada akan dawowar matarsa da kuma zamansu a can, mutane dayawa sunyi mamakin wannan al'amari da kuma san suji lalurar d'an nasa.


Sannan ya aikama Basira akan su shirya dan kuwa gobe ne ranar komawarsu.




*********


Basira yau tace Abu Turab yazo su kwanta tare a kan gado, sun kwanta shiru, ta kamo hannunsa tace " yauce rana ta karshe da zamu kwanta tare duk dadai mun dade bamu kwana tare ba."


"dolene ka zamanto mai kauda kai sannan mai gudun rigima in ka koma gidan mahaifinka, zakaga mutane kala kala masu hali daban daban sai dai fatana ka nutsu ka karanci ko wani hali na d'an adam din daka gani."


Kai ya d'aga mata alamar to, tai mumushi tace " kada ka kuskura ka nuna ma mutane kana gani, wannan alkawarinmu ne wanda nakeso ka rike har sai sanda nace ma ka nuna musu."


Ya kara d'aga kai, tace " zan zamo mai zafi a gareka, zan ki bin bayanka, zan ki nuna ma kulawa, sannan zan nuna rashin damuwata akanka sai dai inaso kasani hakan gata ne wanda zanma, a yanzu bazaka fahimta ba sai dai nan gaba kai da kanka zaka fahimci dalilina nayin hakan."


Abi Turab ya kalleta idanunsa sunyi raurau, ba komai yake fahimta ba a kalamanta saboda yarinta sai dai ya san abu d'aya tana nufin akwai dalili dazaisa ta daina nuna mai kulawa.


Kallansa tai, batai magana ba yai saurin had'iye kukansa, daurewa yai yace " nikam banasan gidan."


Kansa ta shafa tace " Allah ya albarkaci rayuwarka ya karemin kai, wannan itace addu'ata a ko da yaushe."


Shirun da sukai ne yasa bacci yai gaba dashi, ta dade tana kallansa zuciyarta na tsananin tausayama rayuwarsa.








_nikaina tausaya d'an yaron nan nake cewar Kanwata Yar Fara(Meema White)....Lol_😅






*#TEAM ABUTURAB 🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)






*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*






*Wattpad :-AyusherMohd*



*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🤸🏼*




*17*




Itama Magajiya a daren ta shirya taje ta samu mai martaba da nata sharad'in, yayi mamaki kwarai dajin wannan zancen, ya kalleta harzaiyi magana sai ya fasa yace " shikenan ya amince, hakan datai ya nuna masa lalai ba zaman amana take dashi ba haka kuma ta nuna d'ansa ba nata bane."


Magajiya ta juya kai bata ce komai ba dan itakam a yanzu abu d'aya kawai ta sani wato ta tabbatar ta d'aura d'anta a mulki ba komai ba.


Haka mai martaba ya rubuta mata a takarda ya kalleta cikin takaici sannan yace "na dauka na sanar dake d'ana yana da lalura?"


Bata amsa mai ba ta dai amshi takardar hannunsa sannan tai murmushi tace " ba wai rashin yarda ne ko rashin san d'anka bane yasani yin haka sai dai nayi haka ne saboda kauda matsala dazata iya afkuwa nan gaba, me zai faru idan nan gaba ka tara 'ya'ya anzo ana takara da kishi akan mulki? Amma kaga in har mun riga mun tsaida babban d'a a matsayin magajinka banaji wata babbar matsala zata faru."


Kallan yai cikin mamaki duk da dai maganarta ba karya bane sai dai yana ganin sankai da san mulkinta ne yasata yin haka, yafi kowa saninta ya san abinda take tunani, tana tsoro kar nan gaba yaron ya warke in fara tunanin sashi a mulki.


Sallama tamai ta fita.


************


Washegari wajen sha biyun rana aka turo da mota dazata daukesu.


Kofar gidan sarauta aka bud'e, Abu Turab ya kurama kofar ido yana kallo, gannin tsari da girman gidan yasa ya shiga kalle kalle, mamaki yakeyi duk wannan katan gidan na mahaifinsa ne?


Basira ce ta tabashi, ya juyo ya kalleta hararar sa tai sannan ta nuna mai sandarsa, da sauri yai kasa da kansa sannan ya d'auki sandar.


Sun sauka Lantana ta kama hannunsa suka nufi b'angaren da wata baiwa tazo dan nuna musu.


Ba b'angaren ta na da bane wannan yafi girma saboda an warema Abu Turab nasa bangaren.


Haka akai ta zuwa ana gaidasu wasu gaisuwa sukazo, wasu kuwa gulma sukazo, wasu kuwa so suke suga lalurar da yaron ke dashi.


Kafin kace me? Zance ya baza gidan akan Abu Turab makaho ne.


Abdulmajid kam yana gun Magajiya tana kara huremai kunne akan karya kuskura ya bari yaron nan ya rainashi, dan nan gaba baisan mai zai zamar masa ba.


Sun dade a d'akin kafin tace ya tashi ya koma bangarensa.


Abdulmajid nada tsananin kishi, jin akwai wani d'a bayanshi a gun Mai Martaba yasa ransa ya bace, kallan masu kula dashi yai yace " muje in ga kanin nawa."


Haka ya taho dan ya matso yaga kanin nasa da sam baya farin cikin kasancewarsa, sannan yanasan yagani in da gaske baya ganin.


*******


Abu Turab na xaune aka dinga shigowa da kaya, sai dai ba dama ya nuna yana gani, kansa ya kawar gefe yana wasa da hannunsa, sun ajiye kaya dayawa daga na sawa, takalma da sauransu, sannan suka gaidashi.


Juyowa yai inda suke ya amsa tare da cewa "su waye?"


"Mai Martaba ne ya aikomu mukawoma kayan sawa, sannan ga abinci kala kala ya sa a girkama, yace a sanar dakai xai turo anjima a kaika gunsa."


Abdulmajid wanda ke tsaye dan ya shigo kenan yaga ana shiga da kaya yasa ya bisu, wani mugun kishi da tsanar yaron ne ya turnukeshi.


Abi Turab ya saki fuska yace " nagode kwarai."


Wasu kaya aka ajiye a kusa dashi, sannan wanda ya ajiye yace "wannan zaka sa in zakaje gunsa dan a fada yakesan nunaka."


Kai ya daga alamar to, sannan suka juya suka fita.


Abdulmajid ya juya ya juya ya kalli bawansa yace " akwai almakashi?"


Mamaki ya kamashi sai dai batare da ya tambaya ba yace "akwai amma sai gun soro."


Yace " yi gudu maza ka amson."


Nan ya fita da gudu.


Shiga ciki yai ya tsaya a gaban Abu Turab, Lantana ta gaisheshi.


Kallanta yai sannan yace " bamu guri."


Hanyar waje ta nufa gabanta na faduwa, shi kuma Abu Turab ya mike ya mika mai hannu dan su gaisa duk da ba saitinshi ya mika ba, sannan yace " sunana Abu Turab."


Dariya Abdulmajid yai yace " ta ina zamu gaisa bayan ba gani kake ba? Sannan ni yayanka ne baka gani rusunawa ya kamata kayi?"


Abu Turab ya dan kalleshi kad'an sannan ya juya kai baice komai ba.


Shigowar bawansa ne yasa ya juyo ya mikamai hannu yasamai almakashin, rigar da aka kawo dan ya saka ya dago ya sa almakashin ya yanka bayanta takai har wajen wuya sannan ya ajiye ya kalli Abu Turab yace " ungo kayanka saka ni ne wanda zan rakaka gun Mai martaba."


Abu Turab yana kalan mai yai sai dai ba yanda zaiyi, ya kalli Abdulmajid yace "amma karar me naji?"


Kallansa yai a wulakance yace "abu na cire a rigata."


Abu Turab ya runtse ido, yana tunanin yanda zaiyi, in ya nuna ya sani alama ce ta yana gani kenan.


Haka ya amshi kayan ya
kankama a jikinsa bayan yasan duk bayansa a waje yake.


Abu Turab ya kalleshi yace " Amma ance turowa za'ai inje ai."


Abdulmajid ya kalli Bawansa yace "ga wanda aka aiko nan, sannan cewa akai in kaika."


Fitowa yai rike da sandarsa, Abdulmajid na gaba shikuma yana baya, masu kula da Abdulmajid na bayansu.


Tunda suka fito ake kallansa ana dariya, lalai wannan ba makanta bane kadai a kansa akwai alama ta hauka.


Shikanshi Abdulmajid sai dariya yakeyi sam baisan abin zai kayatar dashi haka ba, shidai kawai yayi ne saboda yasa amai dariya a fada bai dauka tun a hanua za'a fara ba.


Sai da sukaje kofar shiga fadar, ya kalleshi yace "shiga."


Abu Turab idanunsa suka kada sukai jaa, jiyake kamar ya sa ihu, mahaifiyarsa ya tuno da kuma kashaidinta akan idanunsa.


Haryaje shiga ya tsaya


Shi mamakinsa mai ya mai? Daga zuwansa ko awa biyu cikakke baiyiba ace harzai mai haka? To shi mai yayi?


Daga bakin kofa akace " Bawan Allah ya akai?"


Abu Turab ya juya zai bargun da gudu, nan fa akaga bayansa.


Barde cikin mamaki dan dashi akaje daukosu yasan yaran ya kalleshi yace "Ba......."


Shiru yai ganin yanda rigarsa ta baya take.




Dariya aka shiga guntsewa ganin kayansa kowa ya tabbatar d'an sarki ne.


Abu Turab duk ya rikice garin gudu ya fadi a kasa, hannayensa ne suka kurje, jiyai idanunsa sun ciciko, fadan mahaifiyarsa na ragonta ya tuna hakan yasa ya hadiye kukan ya mike jiki a sanyaye ya daina gudu, sandarsa ya rike kam yana tafe.


Yana fitowa daga fadar, Lantana ta taho da gudu dan labari ya kaimusu ga Abdulmajid can da Abu Turab suna tafe zuwa fada amma shi Abu Turab rigarsa ta baya a yage take sosai.


Lantana tunda ta ganshi hawaye yake zubo mata, yaron daya taso a kauyen kayau hankalinsa a kwance yau gashi daga dawowarsa gidan mahaifinsa an maidashi shashasha.


Hannunsa ta kama ta rufa mata babban kyallen data d'auko tana hawaye.


Kallanta yai sai dai jiyake kamar taimaka mai tai wajen yin kukan dashi yakesan yi.


Basira kam tun da aka fada mata take zaune ko motsi ta kasa yi, hannayenta kawai ta matse kam.




Abu Turab na shigowa ta shige d'aki da sauri, bayan ta ya kalla ya bita da gudu.


Yana kokarin shiga yaga ta rufo kofa.


Zama yai a bakin kofar.
Hakoransa ne suka shiga kadawa, sanyi ya fara kamashi.


Yana nan a zaune bacci ya daukeshi, wani zazzafan zazzabi ne ya kamashi.




*******




Magajiya kam jin abinda ya faru yasa ta cikin wani farinciki ba shakka lalai d'a dole ya gaji ubansa, bayan Hisham ga ta ai dolene Abdulmajid yai gadon makirci Da kissa.


Dadi ne ya kamata sai murmushi take.




Jin wannan labari yasa Hisham cikin farin ciki, shida Magajiya sunyi dariya sosai sun kuma yaba kwazon d'an nasu da alama in ya girma abinda zaiyi ba wanda zai iya tunani.


Hisham sai kara wasa Magajiya yake yanacewa "ai kwakwalwa da kwazonta ne ya gado yo dama kaza bazatai gudu d'anta yai rarrafe ba...."


Dadi sai kara kamata yake.
Da alama basai ta taimaki d'an nata ba, komawa zatai ta zauna ta dinga ganin yanda Abu Turab zai kasance gun Abdulmajid........




nαcє hmmmmmmmm....


*ⓐⓑⓤ ⓣⓤⓡⓐⓑ ⓣⓔⓐⓜ🤝🏼*


************
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)





*HASKE WRITERS ASSOCIATION*


*Wattpad :-AyusherMohd*



*Na Ayusher Muhd🤸🏼*




*18*


Lantana ce ta zo ta daukeshi tai b'angarenshi dashi, akan gado ta kwantar dashi har lokacin bata daina zubar da hawaye ba, bargo yaja ya luluba ita kuma ta mike ta fito.


A tsaye ta taradda Basira, kusa da ita taje ta tsaya ba tare da tace komai ba.
Basira ta juyo tace " yana ina?"


"nakaishi d'aki." ta fad'a tare da kara share kwalla, Basira ta had'iyi wani yawo na takaici sannan tace " ki amso mai magani yasha."


Tace to, sannan ta juya ta fita.


*********


Mai Martaba kam ana la'asar ya kalli Barde yace " a aika a kira Abu Turab."


Barde ya kalleshi jiki a sanyaye yace " Takawa kayi min afuwa amma ina ganin ka bari sai zuwa wata rana sannan a nunashi a fada." a hankali yai maganar.


Mai Martaba yasan halin Barde tunda ya fadi haka da alama akwai wani kwakwaran dalili, hakan yasa bai sake magana ba.


Ana tashi daga fada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login