Showing 72001 words to 75000 words out of 146065 words
Chapter 25 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
dan tabbas taji haushin maganarsa.
Takarda ta d'auko ta taso a hankali tazo ta ajiye mai agabansa.
Kallan takardar yai yace " na menene?"
Tace " tuni nake maka akan rubutu dakai na cewa Abdulmajid ne zai gajeka."
Fuskar shi ya d'aure yace " sai akai yaya kuma?"
Kallansa tai tace " ba abinda akai Takawa kawai dai ina tunatar dakai ne, saboda tsaru."
"Tsaro? Kina tunanin wannan takardar kad'ai zata iya canza abinda ke zuciyata?"
Idanunta ne suka canza ta kalleshi, yace " eh, kina tunanin ita zata canza min ra'ayi? In na ce bani nayi ba fa?"
Kallan tsananin mamaki tamai sam tama kasa magana, murmushi ya sakar mata sannan ya kamo hannayenta yana shafa samansu yace " kin tab'a ji nace miki inaso in d'aura Turab akan mulki? Banaso kidinga zargin abinda bakiji daga bakina ba, ko warkewa bakiyi ba kin sa abinda bashida tabbas a ranki."
Wani kallo tamai dan tabbas tasan bakar magana yake gaya mata a cukurkud'e, kai ta d'an rankwfo sai tin kuncinsa kamar mai shirin sumbatar sa sannan tace " ina fatan Takawa zai tsaya kan maganarsa."
Juyowa yai inda bakinta yake hakan yasa bakinsu suka kusa sumbatar juna, wani lalausan murmushi ya mata yace " banaji na d'auraki akan mai bani shawara."
Fuskarta ce ta canza hakan yasa ta mike tsaye, tace " Ranka ya dade zan koma."
Alama ya mata da ido akan ga fili ga mai doki.
Duk yanda kaso ka gane ranta a b'ace yake bazaka taba ganewa ba saboda fuskarta d'auke take da annashuwa.
Jakadiya tana ganinta ta taho da sauri, Magajiya ta kalleta tace " biyoni."
Haka kawai ta fada tai gaba.
Haka jakadiya ta bita har suka isa b'angarenta ta wuce cikin d'akinta nan ma Jakadiya ta bita.
Bayan sun shiga ta juyo tace " rufe kofar."
Gaban Jakadiya ne ya fad'i ta tura kofar a hankali ya rage daga ita sai Magajiya.
A jikin kofar Jakadiya ta tsaya tana tunanin abin cewa.
A hankali Magajiya ta tako har inda take, fuskarta tayi bala'in canzawa zuwa tsananin b'acin rai.
Tana zuwa kusa da ita ta d'aga hannu ta zubawa Jakadiya mari.
Da yake sam batai zatan hakan ba jin marin yasa hankalinta yayi tsananin tashi.
Kanta na kasa sai dai hankalinta ya tashi sannan takaici ya cikata, kamar ta?duk girmanta? A kalla ta tabbata taba Magajiya shekara 4 amma ko kunya ta sharara mata mari?
Magajiya ta kalleta sannan ta ce " d'ago."
Jakadiya ta d'ago sai dai yanzu ta dake tace " Mai na miki? Banaji nayi wani abu daya cancanci duka."
Magajiya ta kanne ido tace " ke harkin isa kidinga yad'a gulma akan Abdulmajid? D'an nawa? Da alama kin gaji da aikinki. "
Ran Jakadiya ya kara tunzura jitai tsoron da ke zuciyarta yakau ta kalleta tace " Magajiya d'anki fa kikace?"
Gaban Magajiya ne ya fad'i ta juyo da sauri ta kalleta.
Jakadiya ta daure tace " sharri na masa? Ki tambayeshi da kanki kiji wannan karan ya fara jan hannun Mairo zuwa b'angaren sa? Sannan maganar aiki da kikeyi ni da kaina zan sauka in lokaci na yayi, ina sanar dake hakan ne domin kar akaini bango dan zan iya sanarma Yarima Turab komai."
Tana kai nan ta rusuna tace " Tuba nake Ranki ya dade in bakisa wani sakon zan koma kar Mai Martaba ya nemi ni."
Gaba d'aya ma Magajiya ta kasa magana tana tsaye sororo har Jakadiya ta fita.
Tana fita Magajiya ta saki wani kara na takaici tace " me yasa komai baya tafiya daidai? Dole ne na saita komai su koma yanda suke."
*************
D'agowa Barde yai hankali a tashe ya kalli Abdulmajid yace " Yarima me kake nufi?
Abdulmajid yace " Mairo nakeso, kuma zan aura dan gobe nake shirin sanar ma Mai Martaba shiyasa naga ya dace in sanar maka a matsayinka na mahaifinta."
Barde cikin rawar murya yace " na kasa fahimtarka ne ai, ta yaya kamar kai zakace kanasan Mairo? Ta yaya? Dan Allah Yarima kabar maganarnan anan."
Abdulmajid ya mike tsaye yace " zan jira a waje inaso ka turomin Mairo in ganta kafin na koma."
Barde sam ya kasa yin komai tsaya wa yai sororo har Abdulmajid ya fita.
Mairo kuwa da yanzun nan Ummanta ta sanar da ita zuwan Abdulmajid ya sa ta shigo falon da gudu ko sallama babu tana shiga ta tsaya ganin Babanta.
Jiki a sanyaye tace " Baba!"
Kallanta yai a sanyaye yace " me nake ji Mairo?"
Kai ta girgiza dasauri tace " wlh Baba ba haka bane, shi kad'ai yake kid'ansa yake rawarsa, kaima kasani Baba wlh ni......"
Katseta yai da cewa " Me yasa baki sanar dani ba?"
Hawaye na fara zubo mata tana girgiza kai tace " wlh na d'auka shirmansa ne, na kuma d'auka zai hakura tunda nace mai banaso."
Mikewa yai yace " kije yana jiranki a waje, mayi magana daga baya, kije in har kinaso komai ya rabu lafiya."
Yana kai nan yai waje.
Dabas ta zauna a kasa, sai kuma ta mike a zuciye tai waje.
************
Hisham zaune a falo, gefensa matarsa ce sai kuma kasansu Khadija ce zaune kanta na kasa.
Hisham ya kalli Khaduja yace " Khadija ba zaki fad'amin me ke damunki ba? Sam kin daina ko magana a gidan nan, na tambayekinko bakida lafiya ne kince ba haka ba, Bazaki sanar dani halin da kike ciki ba? Saifullahin ne bakya so?"
Kai ta girgiza tace "bakomai Abba
"
Ran Hisham ya baci yace " to uban me aka miki kika fito daga gidan Sarki kina kuka?"
Khadija ta kalleshi da sauri, sannan ta maida kanta kasa.
Ganin batada niyyar magana yasa ya mike cikin takaici ya kalli Mahaifiyar Khadija yace " duk laifin ki ne da bakya kula da 'yar da kika haifa."
Ya juya yai waje.
🤝🏻 *TEAM ABU TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*48*
Mairo ta dade a tsaye kafin tai waje cikin tsananin b'acin rai.
A tsaye ta ganshi yana tsaye ya juya baya a jikin motarsa, hannunsa sanye cikin aljihun rigarsa.
Tama rasa dame zata karasa mai.
Tsayawa tai kawai tana tunanin wacce kalma ce mai tsananin muni da ya kamata ta fad'amai?"
Juyowa yai dan jikinsa ya bashi ana kallansa, a hankali ya tako har inda take, tana tsaye kawai tana kallanshi.
Yana zuwa inda take yace " Amince Agareki Matar Abdulmajid ko ince Gimbiya Maryam wacce zata gaji Magajiya."
Wani kallo kawai tamai dan ta ma kasa magana, murmushi yai sannan ya d'an kara matsowa yace " Kin rasa bakin magana ko? Na tabbata dama zaki fahimceni, zaki kuma amince da soyayyata."
Kallansa tai cikin takaici sai kawai ta tsartar da yawo ta gefensa ta juya zatai ciki.
Ransa yakai kololuwa gun baci da sauri ya sha gabanta yace " me kike nufi da abinda kikai? Kyama ta kike?"
Fuskarta a had'e tace "Kyamar hallayanka nake, ta yaya zakazo ka samu mahaifina bayan kasan ba sanka nake ba? Ko kana tunanin hakan dakai shine zaisa a auramin kai?"
Lab'ansa ya d'an ciza yace "me kika d'auken? Kina tunanin sanar ma mahaifinki danai nayi ne dan in aureki?"
Mairo tamai kallan ba haka bane? Gira ya d'aga mata ya na kad'a yatsunsa yace " kin makaro Mairo dan kuwa bazaki taba jin shirina a kan aurenki ba, sai dai na d'au alkawari a zuwa daren yau zakisan matsayina a garin nan zakuma kisan nid'in yaro ne ga Sarki Abdussamad."
Yana kaiwa nan ya juya ya shiga mota yai gaba.
Da harara ta bishi tace " ba zuwa dare ba inji an shafa fatiha a nan da awa d'aya." Tai ciki.
************
Sabi'e ne ya mike daga kan kujerar daya kwanta ya kalli Sabi'u yace " Me kake tunanin Mai Martaba zai tambayeka?"
Abu Turab dake rike da littafin Riyadul Salihin yana dubawa yace " ina na sani? Sannan meye naka na damuwa da abinda bai shafeka ba?"
Sabi'u ya d'an yi ajiyar zuciya yace "yau ma tafiya zakai kenan ka barni anan ni kadai? Da alama dai ba amfani a rakiyar nan dana maka."
Tsaki yai yace " Kai dai wlh akwai sanjin gulma ni na shiga ciki."
Ya mike ya shiga d'aki, Sabi'u ya shafa kansa yace " ahhh Sabi'u ka zama d'an d'aki, ni ba mace ba."
Abu Turab kam yana shiga ya kwanta yana tunani.
Ta yaya zai warware matsala da kuma hukunta wad'anda suka wulakanta mahaifiyarsa? Suka kuma halaka masa kawunsa? Ina ma bai tab'a sanin Khadija ba a rayuwarsa, ina ma itama muguwace irin iyayenta? Hakan shine zaisa yaji dadin hukuntasu, idanunsa ya runtse da karfi, baisan meyasa ba bayasan Khadija taga wulakantar iyayenta, kuma ya zamana shine silar wulakantarsu wanda takeso tun tana karama.
A da auran Bilkisu zaiyi ne saboda ya kuntatawa Magajiya da kuma umarni na sarki, sai dai a yanzu ya cire wannan a ransa zai auri Bilkisu ne saboda rad'in kansa, tunda wacce yakeso bazai taba samu ba to gwara ma ya aminta da wacce ta fahimceshi wacce kuma ya yarda da ita, Mairo fa?
Idanunsa ya bud'e daya tuno da ita, wata zazzafar iska ya furzar tabbas dama shi yasan a rayuwarsa ba auran soyayya ba kuma farinciki mai d'orewa ya yanke wannan hukuncin ne tun a sanda Mahaifiyarsa ta sanar dashi komai.
Wajen Azahar yai kwalliya sosai dan babbar riga ma ya saka ya saka hula akan sumarsa, yayi kyau sosai da sosai ya saka takalminsa irin mai lankwasan nan na sarauta.
A falo ya tada Sabi'u yanata baccinsa, fita yai.
A waje yaga dogarawa guda biyu a tsaye da alama sun d'an dade suna jiransa.
Suna ganinsa suka matso suka gaidashi.
Yace " tun yaushe kuke nan?"
D'ayan yai kasa dakai yace " tun d'azu muka zo, Mai Martaba ne yace mu tsaya a waje mu jira har sai ka fito karmu takura maka."
Kai ya jinjina kawai yace " muje."
Bilkisu ce ta shigo b'angaren Fulani, ta zauna kusa da ita sannan tace " Umma da gaske Baba ne yace miki zasu fita da Turab?"
Fulani ta kalli Bilkisu sannan ta kalli Munnira tace " Uwar gulma har kin kai mata rahoto?"
Munnira ta b'oye bayan Bilkisu tana dariya.
Fulani ta kalli Bilkisu tace " me? Kina tsoron kar a wahalar dashi?"
Da sauri Bilkisu tai kasa dakai cikin kunya tace " Umma wlh ba haka nake nufi ba kawai dai abin ya ban mamaki ne ganin baya fita da kowa, dan kosu Yaya ban tab'a ji ance ya fita da wani daga cikinsu ba."
Fulani ta murmusa tace " nima d'azu ya aiko a fad'amin sannan bai fad'i inda zasu ba."
Bilkisu tai kasa dakai tare da wasa da hannayenta tana murmushin kunya.
***************
Su biyu ne zaune a cikin mota a baya sai mai tukasu da dogari d'aya a gabansu.
Sai da suka fara tafiya sannan Sarki ya kalli Turab yace " baka tambayi ina zamu ba?"
Abu Turab yai kasa dakai yace " tuba nake ranka ya dade amma ina ni ina tambaya?"
Sarki yai murmushi yace " a kowani karshen wata ina fitowa inga yanayi da halin da 'yan gari na suke hakan na karamin karfin gwiwa wajen kula da basu hakkinsu."
Abu Turab ya kalleshi cikin jin dadi.
Sarki ya kamo wannunsa hakan yasa ya kalleshi cikin mamaki, Sarki ya mai murmushi yace " bansan dalili ba ina ganinka naji gamsuwa da yabawa da kai danai, duk da nasan hakan yasamu karfi ne daga mukamin mahaifinka sai dai dukda hakan matsayi da yardar da nake maka dabance."
Turab yai kasa dakai yace " Godiya nake."
Haka sukai ta shiga gari guri guri kafin daga karshe suje wani katon gida wanda kana ganinsa kasan gida ne na sarauta duba da zanen da ke jiki.
Sai da suka shiga ciki, Bafaden nan ya sa makulli ya bud'e gidan, nan suka shiga ciki.
Abinci ne kala kala an shirya musu an kuma ajiye da alama dama ajiye wa akai kawai dominsu.
Bayan sun zauna Sarki ya kalli Turab yace " Abu Turab!"
Kallansa yai sannan yai saurin maida kansa kasa yace " Ganinan Ranka ya dade."
Mai Martaba yace " Bilkisu 'yatace wacce duk cikin 'ya'yana nafi kauna, bawai dan wani abu ba sai dan maraicin ta, batasan mahaifiyarta ba, ita kanta mahaifiyarta ko riketa batayi ba Allah ya amshi ranta, hakan yasa nake tsoron auran da ita saboda banasan ta auri wanda bazai kularmin da ita ba, sai dai duk yanda naso ba yanda zanyi tunda mace ce ita."
Abu Turab yai kasa dakai, Mai Martaba ya kalleshi yace " Turab ka kularmin da Bilkisu wannan rokone daga bakin mahaifi zuwa wanda zai kasance abokin rayuwa ga 'yarsa ba wai roko bane daga bakin sarki ba."
Da sauri Abu Turab ya mike ya d'ora gwiwowinsa a kasa yace " ni ne ya kamata inyi roko inkuma yi godiya, sannan bazan ma alkawarin bata kulawa wanda take samu anan ba, dan in na fad'i haka to tabbas nayi karya sai dai ina zanyi iya kokarina wajen ganin na bata kulawar da ya dace sannan zanyi kokari wajen ganin bakai dana sanin auramin ita ba."
Kallo d'aya zakama Sarkin ka tabbatar ya gamsu ya kuma ji dadin kalamansa.
Mikewa yai yazo inda Turab yake ya d'agashi sannan ya rike hannayensa yace " Nagode Turab."
Nine da godiya.
Sarki ya zaunar dashi kusa dashi yace"muci abinci."
Cikin kunya haka Turab yake cin abincin.
************
Magajiya ce ta d'au kofin dake hannunta wanda take shan ruwa dashi ta shilo inda Abdulmajid yake, da sauri ya kauce.
Idanunta karara suke nuna b'acin rai tace " me? Auran Mairo?"
Abdulmajid ya daure yace " Umma kitaimaka ki amince dani inhar kika yarda da hakan nikuma na miki alkawarin hawa mulkin garin nan."
Cikin b'acin rai tace " Abdulmajid fita ka bani guri, sannan kar in sake jin maganar nan."
Mikewa yai ya fito cikin b'acin rai.
Kofar d'akinta ya kalla bayan ya rufe yace " Kiyi hakuri Umma wannan karan zan saba miki, dan auran Mairo shine kadai zai sa in rama yawun da ta tofa a kusa dani."
Yai gaba.
Zaune ake a fada a cike taf, Abdulmajid ya shigo a zauna a gun zamansa sannan ya gaida Sarki.
Tunda ya shigo Barde gabansa ke fad'uwa.
Bayan Sarki ya amsa gaisuwarsa sannan Abdulmajid yace " inada magana Ranka ya dade."
Nan aka bashi izinin magana.
Durkusawa yai alamar roko yace "Ina neman alfarma gun Mai Martaba .
Sarki cikin mamaki ya kalleshi yace " ina jinka."
Abdulmajid ya kalli Barde wanda yake had'a zufa sannan ya kalli Hisham wanda shi kansa ya kosa yaji da wace magana Abdulmajid yazo.
Abdulmajid yai kasa dakai yace " Mairo 'yar gidan Barde nakeso a auramin."
Tsananin mamaki ne ya bayyana a idanun Mai Martaba, tashin hankalin dake idanun Hisham kuwa ba'a magana.
Sarki ya kalleshi cikin mamaki sannan ya kalli Barde.
Galadima ne yai caraf yace " Masha Allah wannan had'in yayi kuwa ranka ya dade, ba shakka wannan had'in zai karfafa zumuncin sarauta."
Nan kowa ya fara fad'in gaskiya kam.
Sarki ya kalli barde yace " me kace?"
Barde ya daure yace " Ai 'ya'yana da ni kaina umarnin ka ne, duk abinda ka yanke shi za'ayi............
Sarki ya d'ago ya kalli Abdulmajid.
🤝🏻 *TEAM ABU TURAB*
.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
_Gareku 'Yan Ayusher Fan Club, wannan Shafin naku ne kacokal...Allah ya bar zumunci_
*49*
Sarki ya kalli Abdulmajid sannan ya kara kallan Barde wanda duk jikinsa ya gama mutuwa.
Gyaran murya Sarki yai yace " Zan duba maganarka, sannan bana jin hakan dakai ya kamata, Mahaifinta ya kamata ka sanarmawa sannan nima ka samen ka fad'amin hakan ne zai sa musan abinda ya kamata, bawai dan kana d'ana ba zakai tunanin dole namaka duk abinda kake so."
Abdulmajid yai kasa dakai yace " Tuba nakeyi."
Bayan ya fito, Hisham ya taho shima da sauri.
Tsayar dashi yai ta hanyar kiran sunansa.
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalli Hisham.
Hisham cikin sauri ya karaso yace " Abdulmajid menene hakan? Wace irin Mairo? Wacece ita da har zaka zo cikin fada kace kanaso a baka?"
Abdulmajid ya kalleshi cikin rashin kulawa da abinda ya fad'a yace " wacce nakeso kuma zan aura."
Hisham yace " Abdulmajid yar gidan barde ce fa, me kake tunani?"
Yace " D'an 'yar gidan Barde ce sai me? Ni wai kawu me yasa kai da Umma bakwa duba halin da nake ciki ne? Me yasa bakwa tausayawa soyayyar da nake mata?"
Mamaki ma sam ya hana Hisham magana, Abdulmajid bai jira jin wani abu ba kawai yai gaba.
Yana kokarin shiga b'angarensa, wata baiwa daga b'angaren Magajiya ta karaso da gudu tace "Yarima ana kiranka."
Nan ya juya zuwa b'angaren Magajiya.
A tsaye ya ganta a cikin d'aki yana shiga ya rufe kofa, matsowa tai inda yake ta zuba mai wani mari, jikinsa sai daya amsa, tsoro karara ne ya bayyana a idanunsa dan yanda yaga bacin rai karara a idanunta.
A hankali ya zauna a inda ya fara zama kansa na, juyowa tai cikin tsananin takaici tace "Abdulmajid kai harka isa har ka isa ince karkai abu kayi? In haifeka a cikina kace kana neman kafi karfina? To bari kaji tunda nake a duniya duk wani buri nawa ba wanda ban cikashi ba sai abu d'aya wanda shikad'ai ne nake danasanin gangancin danai, daga shi kuma bana bukatar wani danasani a rayuwata, baka isa kai ka sani bakin ciki ba....."
Katseta yai yace " Umma yanzu menene aibun auren Mairo?"
"Aibu? Shi kake san