Showing 60001 words to 63000 words out of 146065 words

Chapter 21 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

girke kala kala, kwalliya sosai tai tasa aka jera mata kaya a cikin mota, tana kokarin fitowa Khadija ta shigo.
Bayan sun gaisa Khadija tace " Umma Babba bacci ne ya d'aukeni sai dana tashi Umma tacemin kina kirana."
Magajiya ta kalleta tace " fita zanyi ki jirani inje asibiti in dawo."
Tanajin zancen asibiti tai saurin cewa " zanje Umma Babba inyaso mayi maganar a hanya."
Kallanta tai tace " ba dai san ganin Abu Turab d'in ne yasa kikesan zuwa ba ko?"
Dasauri tace "a'a Umma."
Muje.
Nan suka fito tare.
Masu kula da bangarenta ta kalla tace ku sanar da mutane tafiyata duba Turab kunsan me nake nufi ai, sukace mun gane ranki ya dade.


Tayi hakan ne dan asan abinda takaimai da kuma nunama jama'a tana san yaran.
Sun shiga mota, Magajiya ta kalli Khadija cikin yanayin bugat ciki tace " Ashe Saifullahi yazo?"
Khadija tace " eh yazo jiya."
"Yace zai dawo?"


Khadija tai shiru dan batasan me zatace ba, Magajiya ta tsuke fuska tace " Badai wulakantashi kikai ba ko?"


Khadija ta kalleta jiki a sanyaye tace " Umma ni na kasa gane dalilin had'in auran nan....."


Wani mugun kallo ta mata wanda yasa tai shiru bata iya karasa fadar abinda zata fada ba.
Magajiya tace " Khadija kina tunanin zamu cutar dake ne? Yaran nan d'an gidan manya ne sannan shi kad'ai ne namiji agun iyayensa, ga kudi ga matsayi auranku dashi zai taimaka ma Yayanki Abdulmajid zai kuma taimakeki."


Mamaki ma ya hanata magana, au wad'an nan sune dalilin dayakesa ayi aure? Matsayi?kudi?"


Magajiya ta dafata tace " na yarda dake dan haka karki bani kunya, kinfi kowa sanin Abu Turab bazai taba auranki ba ko matan duniya sun kare dan ko shi ya yarda ni da mahaifinki bazamu taba yarda ba, in ma kina tunanin wani shirme a ranki to kiyi maza ki cire wannan ki maida hankalinki kan Abu Turab."


Khadija tai kasa dakai kawai batace komai ba.


Sun isa asibiti nan aka kwashi kaya aka fara shiga dasu.
Abu Turab na kwance lokacin bacci ne ya fara d'aukansa, Garzali ne ya shigo ya sanar dashi isowar su Magajiya.


Idanunsa na rufe dama saboda dazu Galadima da Barde suka tafi.
Tashi yai ya zauna, ta shigo cikin isarta da yanayin tafiyarta, tana kallansa ta saki wani murmushi, ba shakka yaran nan dan rainin hankali ne harda wani rufe ido?
Shiga tai ta zauna, khadija tana tsaye a jikin kofa bata karaso ba.
Magajiya ta kalleta tace " dan bamu guri Khadija d'a da uwa zasuyi magana, in na gama sai ki dubashi."
To kawai tace tai waje.


Magajiya ta kalleshi tace " Turab bazaka kunce daurin ka gaida mahaifiyarka da kyau ba?"


Abu Turab yace " ai na gaidake ,sannan nida banda lafiya an min aikin ido ta ina zan ganki?"
Murmusa wa tai tace "ahhh na tuna ashe fa makaho ne wanda akamai gyaran ido."


Abu Turab yace " naji dadi da kika tuna."

Shiru sukai kafin can tace "Mahaifinka ya tura mutane yau sunkai kayan godiya da amsawar da masarautar kano ta basu na auranka."

Batajira amsarsa ba tacigaba " Kaifa kana tunanin kaci galaba ko?za kuma ka auri Bilkisu ko?"
Tad'an juya kai sannan tace " sai dai kuma inaso ka sani sai har in an gama shafa fatiha na d'aura auranku sannan zan yarda kaci galaba akan Bilkisu, abinda nazo in fadama kenan."


Murmushi ya saki yace " na d'auka kinzo ne akan mutane susan kinzo duba d'anki? Ashe zuwa kikai kimin kashedi."


Kallansa tai tace " ai dole ne uwa tazo duba danta."
Yace " hmm gaskiya kam
"


Mikewa tai tace " zan koma, ina fatan makaho ya dawo gida a matsayin cikaken ido hakan ne zaisa wasan yafi dadi, muga tsohub hannu da sabon hannu."


Kai ya jinjina yace " kuma fa hakane."
Juyawa tai tai waje.

Khadija ce ta ke kokarin shigowa yanaji Magajiya na ce mata wuce muje ba sai kin shiga ba.
Khadija tace " Umma ba dade wa zanyi ba dan Allah."


Wuce muje ko? Ko kin taba gani an duba mai lafiya?
Zata sake magana ta mata wani kalli, juyawa tai idanunta sun ciciko.


Komawa yai shima ya kwanta, tunda ta tafi jiya duk yanda yaso ya cire zancen Saif a ransa ya kasa, waye shi? Menene matsayinsa a gunta? Sai dayai yaki sosai da tunanin kafin ya samu ya kawar da shi a ransa.


Khadija kam harta shiga mota bata ce komai ba, Magajiya duk da ganin Khadija a haka yasa taji ba dadi sai dai inaaa, bazata yarda da yanda Khadija ke nuna tsantsar damuwarta akan yaron ba.




**********




Yau ya cika sati d'aya kenan da zuwan Turab Asibiti, yau ne kuma ranar da zai koma, tsaf suka shirya komai, Mai Martaba da kansa yazo dan tafiya da dansa, su Hisham da su Barde duk sunyo rakiya.


Mairo kam kusan kullum sai tazo dan Basira ma wani sa'in ita take aike, Khadija kam ba damar zuwa, tun randa suka tafi, sai dai kome take Abu Turab na ranta, kullum sai ta tashi tamai addu'a da daddare.




*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*




🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*40*



Magajiya ce kicinged'e a kilisarta da alama tunani takeyi duba da yanayin da take ciki.
Jin muryar Hisham ne yasa ta katse tunaninta tare da bashi izinin shigowa.
Hisham ya shigo sannan ya zauna kusa da ita, ya gaidata.
Magajiya tad'an ja numfashi bayan sun gama gaisawa tace " Hisham dole ne sai mun kawar da Abu Turab daga gabanmu, domin na kula in bamuyi wasa ba Mai Martaba zai biyo mana ta bayan gida, da farko ya had'a Turab da 'yar sarkin kano sannan mun fahimci yana gani, sannan gashi zamansa a asibiti manyan masu mukamai sunje dubashi sun kuma dawo da yaban d'abi'arsa."


Hisham ya kalleta yace " Magajiya nikaina abin nan ya damen, me zai hana mu raba shi da du......"
Wani mugun kallo ta bugamai tace " so kake ka lalata mana shiri irin sanda yana jariri? Duk badadan kaje kayi shirman kona musu gida ba me zaisa Basira tabar gidan nan? Da cikin ruwan sanyi zamu turashi barzahu ba tare da an fahimci komai ba, dan haka karka kuskura ka kara gigin daukan hukunci ba tare da ni na sani ba."


Ba shakka yaji haushin kalamanta a ransa, sai dai a fili cewa yai " shikenan."
Tace " nayi tunani sosai na fahimci Basira itace lagwan yaran nan, in har muka sata a tsaka mai yuwa to fa Turab zai zamar mana tamkar akala."
Hisham yace " Na d'auka Turab muke hari ba wata Basira ba."


Tsaki tai tace " kai matsalata dakai kenan, kwakwalwarka gaba d'aya bata ja, kai kana tunanin yaran nan ba wani abu bane?"
Hisham yace " to nawa yaran yake?"
" nawa yake amma har ya nemi ja min masifa nida Abdulmajid? To bari kaji in fada ma, wlh wannan yaran in ba munyi da gaske ba reshe ne xai juyi da mujiya."


Tacigaba " so nake kasa a samomin guba amma mara karfi."
Cikin mamaki yace " guba kuma? Wace iri?badai Basira zaki kashe fa ita ba?
A fusace tace " wai meyasa in na fadi abu ne yaya sai kace sai na fadama dalili? Kasa a samo abinda na fadama, sannan ka tabbatar kasa anba wannan yarinyar da muka saka a bangaren basira data saka a cikin abincin da za' a kawo min?"
Idanunsa ne suka firfito yace " bangane abincin da za'a kawo miki ba? Kina nufin kece zakici gubar?"
Tace " wannan ba damuwarka bace in har kanaso mu d'aura Abdulmajid akan mulki to kawai ka dinga bin abinda na umarceka ba tare da tambaya ba."


Daurewa yaiyace "to."
Tace " gobe zasuzo gaisuwa, dan haka ayau zaka samo gubar ka kuma aika da ita a daren nan."
Yace to, mikewa yai ya fito yana mamakin me take shirin yi.


Yana fita ta mike, sannan tai murmushin mugunta.




**********


Shikam Abu Turab bayan ya iso yana gun Mahaifinsa sun dade suna tattaunawa game da bikinsa da kuma wasu al'amura na sarauta da mahaifinsa ya nemi shawarar d'an nasa akai.


Sun yanke shawarar komawarsa garin kano a wannan sati, in ya dawo kuma sai a tura kayan gaisuwa da na lefe a saka rana.




Bayan ya fito ne ya nufi gun mahaifiyarsa, duk inda ya wuce mutane sai tayashi murnar warkewa sukeyi har ya isa.


Basira tasa an mai girke kala kala kana ganinta zakaga tsantsan farinciki a fuskarta.
Bayan sun gaisa ne tasa aka jera mai abimci kala kala, Abu Turab yai murmushi yace "Umma kenan sai kace wanda na bar garin?"
Lantaba Tace "ai Uban gidana inaji da kai mace ne in kai aure binka zatai."
Dariya suka saka, nan ya fara zuba abinci.
Basira tace " Magajiya ta shirya walima na kusa da zamuje gobe na murnar warkewarka."


Kallanta yai sannan ya baida kansa kan abincin yace " she is trying hard."
Basira tace " magana kai?"
A'a, amma su waye zasu gun?
Tace "hmm daga dai mu matan Takawa da shi Mai Martaban sai kai da Abdulmajid, amma bansan ko da wasu ba."

Yace "hmm."
Basira tace " tace insa ayi abinci daga nan, nafi san kowa in mai abincin danasan yafi so, saboda taro ne akayishi saboda d'ana."


Zuciyarsa d'aya dan bai kawo komai a ransa ba yace " to, amma karki wahalar da kanki Umma."
Tace " wace wahala bayan ba ni zanyi girkin ba?"
Murmushi yai ya cigaba da cin abincinsa.


Sai daya gama ya mike ya fito, bangaren kakarsa ya nufa wacce ta tsufa sosai gashi batada lafiya, yana tafe su Garzali na bayansa.


Sam bai kula da ita ba wacce ta shigo gidan na sarauta dan kawo ma Abdulmajid sakon da mahaifiyarta ta aikota ta kawo.


Sai da suka kusan junan su sannan suka ankara da juna.
Kallanta yai sannan ya d'auke idanunsa ya cigaba da tafiya.
Wani sanyin dadi ne ya kamata ta karaso da sauri tace " Yaya."
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalleta fuskarnan a d'aure.
Murmushi ta saki tace " Yaya baka taba ganina ba ko? Nice Khadija, ahhh nasan kasan muryata, hmm Alhamdulila yau Allah ya amshi addu'a ta."


Kallanta yakeyi kawai sai dai zuciyarsa ta karaya sosai, Khadija ta share kwallarta data taho tace " Yaya Allah ne kadai yasan farincikin danakeyi ganin idanunka sun bud'u da izinin Allah bud'ar idanunka zai kawoma alheri masu yawa a rayuwarka."
Ta karasa maganar cikin rawar murya dan kuka na neman kufce mata.
Sama ya d'an kallan kadan yana neman dake zuciyarsa dan tabbas kalamanta sun ratsashi.
Kallanta yai yace " nagode, sai dai inaso ko a hanya muka hadu ki daina nuna kin sanni, banasan inzama mai jawo miki bakin ciki shiyasa nake fatan ki cireni daga ranki ki kuma daina damuwa dani."


Kai ta jinjina ta na kokarin share hawayenta da hannu tace " naji yaya, zanyi abinda kace."
Kallan mamaki ya mata dan bai yi tunanin abinda zatace kenan ba.


Khadija ta kara share hawayenta tace " kasan meyasa zan rabu dakai yaya?"
Kallan ta yai baice komai ba.
Ta cigaba " saboda ka daina murmushi in kana tare dani, ka daina fara'a, ko farin ciki kakeyi daga kaji muryata sai inga farincikin nan ya tafi daga fuskarka."


Hawayenta ta kara sharewa tace " kaine mutum na farko dana taba so, banaji zan kara san wani haka, ba kuma naji zan daina ma fatan alkairi da yima addu'a a rayuwarka sai dai bazan taba yarda inzama nice sillar bakin cikinka ba, bansan dalilinka na canzamin hala ba, sai dai ba yanda z........"


Hawaye ne suka taho sosai wanda ta kasa karasawa, jiyai gaba daya daga tsakiyar kansa har zuwa 'yan yatsun kafafunsa sun amsa, shikansa sai dayaji idanunsa suna neman canzawa na yanayin kawo ruwa.


Kallansa tai sannan ta kakaro murmushi tamai sannan ta juya ta fara tafiya.


Kasa motsawa tai daga inda yake, su Garzali na gefe duk da basusan me tacemai ba amma sun fahimci yana bukatar keb'ewa.


Abu Turab kallanta yakeyi har sai da ya dena hangota sam ya kasa motsawa, yafi minti 20 a haka kafin ya taka kamar wanda aka tsuma a ruwa ya karasa bangaren kakar.


Jikinta kam ba sauki duba da yanayin tsufan datai, bai dade ba ya taso.



D'akinsa ya nufa ya shige ya kwanta rigingine, rayuwarsu da Khadija ya shiga tunowa, wasu kananan hawayene suka zubo ta gangaren idanunsa, mirginawa yai ya kwanta ganin tunaninta na neman addabarsa ya mike zaune da sauri ya bud'e cikin drawer dinsa ya dauko d'ankwalinta har yayi kamar zai yadda sai kuma ya fasa ya d'aga can kasan kayansa ya saka shi.


Ya koma kan gado ya kwanta........


Khadija kam tana fita ta wuce gida dan kuka kawai takeyi, sam bata kula da Hisham ba dayake tsaye gefen kofar shiga gidan shi da su Galadima.


Hisham ya kula da kukan da takeyi sai dai ba damar magana saboda bayasan a ganta tana kuka.




*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*
.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)





*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*




*_Wannan Shafin sadaukarwa ce gareku Aminan arziki, BillynAbdul, Billy Badaru da Ummu Basheer Allah yabar zumunci da aminta (Ameen)_*




*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*41*




Yau tun safe ake hidimar yin walimar da Magajiya ta shirya, barin ma bangaren Basira wanda aketa hada hadar girke girke, katon d'akin da suke taro na lokaci zuwa lokaci tasa aka gyara, an mai kwalliya sosai, kowa an waremai gurin zamansa.


Abu Turab kam yana can gun hutawar mai martaba wanda ya saba zama, yarasa meyasa yakejin hankalinsa bai kwanta da wannan walimar ba sai dai ya rasa ta ina matsalar take, kalaman Magajiya ne suke ta mai yawo a zuciyarsa, ya tabbata akwai abinda ta shirya a wannan taron.


Ganin bashida amsa da hujjar dazai kama yasa ya mike, ya nufi bangaren Mahaifiyarsa.


Tana tsaye a kitchen tana kula da abincin da ake tayi, Mairo ma aiki take tukuru, murmushi yai na jin dadin yanda take taimakon mahaifiyarsa.


Basira ce ta juyo ta kalleshi sannan ta kalli Mairo tace " Mairo bari na shiga ciki."
Tace " To Umma" kallan Abu Turab tai tace " Yaya Ina Wuni? "
Yace " Mairo sannu da aiki."


Bata amsa ba sai murmusawa datai.
Bayan Basira yabi, Suna shiga ciki ta kalleshi tace " Dazu na tura a kiramin Mairo, sai datazo hankalina ya kwanta har nake shigowa ciki."


Kallanta yai yace " Umma kinaji da Mairo, itama haka."
Tace " Abu Turab in fadama gaskiya babban burina a duniyarnan a wannan lokacin bai wuce in ganka cikin farinciki ba, sannan banaji akwai mai saka wannan farin cikin daya wuce ta."


Kasa yai da kansa baice komai ba, ta kalleshi tace " komai da lafiya ko?"
D'agowa yai ya kalleta cikin wani yanayi yace " Umma sam hankalina ya kasa kwanciya, inaji a jikina akwai abinda zai faru a gun taron nan sai dai na rasa menene."


Kallansa tai cikin kulawa tace " Turab nasan me kake tsoro sai dai inaso ka sa aranka ba abinda zai faru in shaAllah, dana menene abin jin? Bai wuce ta zuba mana wani abun a abincin mu ba, to ninake yin abincin kaga ba wani abu da zata iya yi."


Jitai yace " shine abinda ke damuna Umma, yin girki a nan bangaren."
Kai ta girgiza tace " Abu Turab kenan, insha Allah ba abinda zai faru."


Shiru yai baice komai ba, sai dai shikam abin na damunsa menene dalilin barin mahaifiyarsa ta d'au nauyin girke girke?"
Basira ce ta katseshi tace " ka tashi kaje ka shirya nima shirya wa zanyi tunda ankusa kamala komai, sannan Mairo da Lantana suna gun."


Mikewa yai ya fito jiki a sanyaye.
Sai dayazo saitin kitchen sannan ya kalli kitchen din aiki kawai akeyi, Mairo ce ta fito tazo jikin kofa tace " Yaya lafiya?"


Yace " Mairo dan zo."
Takowa tai har zuwa inda yake, ya kalleta kamar zaiyi magana sai kuma taji yace " shikenan."


Kallan mamaki tamai sai dai batace komai ba, juyawa yai zai wuce sai kuma taga ya tsaya ya kalleta yace " Nagode Mairo."


Nan ma kallan mamaki tamai, sai dai bata iya cewa komai ba.
Abu Turab ya fita zuwa bangarensa.


Wanka yai sannan ya shirya cikin wata had'adan yadinsa d'inkin yamai kyau sosai, yasa hula sannan yai sallar la'asar.


Ya dade yana addu'oi kafin ya mike ya fito.
Su Garzali dama suna tsaye suna jiransa.


*************


Magajiya ta sha ado na gani na fada, tayi kyau sosai kamar batakai yawan shekarunta ba, kallan kanta tai a madubi ta saki murmushi a ranta tace " nayi kuskure babba na bawa kishiyoyina maganin hana haihuwa, kaine ka nunamin kuskurena Turab, ba su ya kamata in ba wa magani ba mijina ya kamata inba, sai dai ganin an haifeka ina zaune kamar wawiya yasa na dawo hayyacina, tun kuwa daga lokacin nasa aka amsomin magani akesama Mai Martaba a abinci, ba'a ja dani, ka jirani zan nunamaka wacece Magajiya a ranar yau, zan nuna maka bakasan komai ba a harkar wasa.


Takalmi ta saka ta zura alkyabbarta kyanta da kwarjininta suka kara fitowa.
A falonta ta tadda ragowar matan kannan mai martaba da kuma kishiyoyinta.
Nan suka gaisheta, tana gaba suna bayanta haka har suka isa.


A zaune suka tadda Basira, a mazauninta, sai matar Galadima da Mamar Khadija.


Tana shigowa ta mike sai data zauna sannan kowa ya samu gu ya zauna, wannan tsarin ita tafito dashi, duk sanda za'ai taro dolene sai ta zauna kafin kowa ya zauna.


Sun d'anyi gaishe gaishe kafin a sanar da isowar Abdulmajid.
Nan ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login