Showing 66001 words to 69000 words out of 146065 words
Chapter 23 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
kallon da takemai tace " Barkanka da Zuwa."
Ta karasa maganar tare da matsamai ta bashi guri.
Magajiya ce a kwance kamar d'azu sai dai Abdulmajid na zaune a kasa yana cin abinci.
Murmushi ya saki sannan ya kalli Khadija yace " nima zanci abincin."
Da sauri Abdulmajid ya kalleshi dan da ya dauke kai dayaji muryarsa.
Khadija ta kalleshi itakanta tayi mamaki sai dai amsa mai tai dato, tai waje.
Abu Turab ya kara tura kofar ya shiga bakinsa d'auke da sallama.
Abdulmajid ko amsa mai baiyi ba sai kallan mamaki da yake binsa dashi, wannam kwalliyar fa?
Abu Turab ya karaso ciki ya zauna gaban Abdulmajid yace " Abdulmajid Barka da war haka."
Bai amsa mai ba sai kallan mamaki da yake mai.
Shima bai nemi amsar tasa ba Kallan Magajiya yai yace " Har yanzu Umman tamu bata farfad'o ba? Inata tsoro kar muje ta wuce ta can kasan matsalar guba akwai illa ta gaske."
Yanda yake maganar kai kace irin Abokinsa ne Abdulmajid d'in.
Abu Turab ya kalleshi yace " kayi shiru ko baka neman mata sauki ne?"
Abdulmajid ya saki wata dariya ta takaici yace " duk duniya inda wanda zai fi damuwa da ciwon ta ai banaji ya kaini ko?"
Jinjina kai ya shiga yi yana cewa " gaskiya ne kuma kayi magana anan, sai dai ni kaina ina mata fatan samun waraka, dan ciwonta duk ya hanani sukuni."
Mamaki da takaici ma sam ya hana Abdulmajid magana.
Abu Turab ya d'an furzar da wata iska yace " ta ina zanso Ummanmu ta gangara bayan ko bikina da Gimbiya Bilkisu bata gani ba? Sannan Bata ga d'anta akan mulki ba?"
Ba shakka wannan kalma ta hawa mulki ta konama Abdulmajid rai, cikin zafin rai ya mike a zuciye ya kaima Turab naushi a kunci, wamda hakan yazo da daidai Khadija ta shigo d'auke da abinci.
Tana ganin Abu Turab ya fadi ta saki abincin tai gunsa da gudu.
Kallansa tai cikin tsananin kulawa tace " Yaya sannu."
Sannan ta d'ago ta kalli Abdulmajid cikin takaicin abinda ya aikata tace " Yaya kana hauka ne? Ta yaya zaka nausheshi?"
Idanu Abdulmajid ya zaro yace" Khadija? Ni kike fadawa haka?"
Idanunta ya rufe gaba d'aya cikin masifa tace " an fadama, tayaya zaku dinga abu sam ba tunani? Me ya Turab ya maka? Dan yazo duba Umma? Ko dan ana zargin Mahaifiyarsa?"
Wannan kururuwar tasa mata dake zaune a falo leko d'akin dan dama Khadija bata ko rufe kofar ba.
Abu Turab ne ya sauye fuska zuwa yanayin tausayi yace " Khadija ki bari menene hakan kike yi?Laifine in yaya ya hukunta kaninsa?"
Kallansa tai cikin tsananin tausayawa idanunta sun ciciko da kwalla, tace yaya kalli gefen bakinka fa? Ya fashe."
Magajiya dake kwance tana jin duk abinda ke faruwa jitai zuciyarsa kamar zata fashe ba shakka sai taci mutuncin yaran nan.
Abdulmajid ganin yanda Khadija take ma AbuTurab hawaye yasa ma ya kasa magana, tsawa ya buga mata yace " ke dam gidanku fita daga nan."
Kallansa tai fuskarta a turbune cikin tsananin bacin rai, Abu Turab yace " fita mana."
Juyawa tai cikin takaici ta nufi kofa, ta na fita tai gida, tana tafe tana hawaye.
Magajiya data d'auka Khadija ta fita sannan ba kowa a d'akin kenan sai Abu Turab da Abdulmajid ta mike cikin kunar rai zatai magana.
Idanunta ne ya sauka akan matan dake labe jikin kofar d'aki, suma kallanta suke cikin mamaki.
" Laaa Magajiya ta farfado."
Nan suka shigo ciki, Abdulmajid ya runste ido na takaici sannan ya kalli Abu Turab.
Gani yai Abu Turab ya sakar masa murmushin rainin hankali.
Mikewa yai yace " Umma kin farfado? Kin ganeni?"
Wani irin kallan tsana da takaici takaima Abu Turab dan gaba d'aya ya wargaza mata shirinta ita dataso sai an ma Basira hukunci mai tsanani kafin ta nuna musu ta farfado? Sai an d'auka ta kusa mutuwa tukunna?
Kowa murna ne ya bayyana a fuskarsa, Abu Turab ya sosa keya yace " Lalai na yadda Mai maganin nan ya iya bada magani daga bata yanzu har ta warke?"
Kallansa sukai cikin mamaki sukace " Yanzu ka kawo mata?"
Kai ya d'aga alamar eh sannan ya kalli Abdulmajid yace "ko yaya?"
Abdulmajid bakim ciki yasa kawai ya d'aga kai , nan suka fito cikin tsananin farin ciki.
Suna fita Magajiya ta kalli Turab kallan Takaici tace " kai bazaka tafi ba? Uban me kake jira kuma?"
Fuska ya canza yace " Umma ina kikeso inje bayan yanzu kika farfado ke kanki ai bazaki so d'anki ya barnan ba."
Kallansa tai tace " mene?" Yace " abinda kikaji nace, ni ai yanzu tunanin dawowa kusa dake nake yu saboda na kula bakyasan nai nesa dake."
A zuciye Abdulmajid ya fizgoshi yace " kai wai kanka ko ya zare ne?"
Hannu Abu Turab yasa ya tureshi da karfinsa sannan ya nunashi da yatsa yace " Gargadi ne zan maka shi ka tsaya kajini dakyau, yau inaso ya zama rana ta karshe da zaka kara gigin tabani, wlh duk randa ka sake ina sanarma da duk abinda ya biyo baya kai kuka da kanka."
Sannan ya kalli Magajiya yace " Umma ya kike jinki? Kina farin ciki da dawowa duniya da na taimaka miki kikai da wuri?kinga yanzu kafin na fita d'aga nan zance zai kaiwa mutane na maganin dana baki kika warke da kuma wulakantani da Abdulmajid yai dan nazo baki magani."
Ya d'an langwab'e kai yace " ya kika gani Umma? Puzzle din ya shiryo ko?"
Ta cika taf dan kawai wani kallo takemai, Abdulmajid ma ya gama cika, juyawa yai ya fara tafiya har ya kusa isa kofa sai kuma ya juyo yace " ahhhh ina tayaki murna Umma dan Gimbiya Bilkisu bata yadani ba akan wannan al'amarin, na gode da kara bani karfin gwiwa da kikai na auranta."
Yana kai nan yai waje.
Magajiya yana fita ta juyo ta kalli Abdulmajid cikin tsawa tace " fita."
Waje yai yana fita ta ta kama bargon da aka lulubeta dashi ta matse da karfi kai kace juyemai bakin cikin takeyi.
Bangaren Mai Martaba ya nufa.
A hanya yaga Jakadiya tana ganinsa ta iso da sauri tace " ikon Allah ashe yarima kaine ka samu mata magani? "
Bai tanka mata ba saidai yana tsaye.
Tace " hmm gaskiya ne amma nikam yarima banso ka cece ta ba Kana ganin halin datasaka mahaifiyarka a........."
Katseta yai yace " Jakadiya, in zaki fadi abu ki fada amma banasan zancen gulma."
Ya juya yai gaba.
Zance ya yad'o a masarauta akan Abu Turab shine ya nemi mata magani, ba shakka in har mahaifiyarsa ce take neman kasheta bazata taba yarda d'anta ya nemo mata magani ba, wannan labari yasa mutane dayawa sun canza zargin su na cewa Basira ce ta bata gubar nan.
Zaune yake a gaban Mai Martaba, Sarki yace " Ka kawomin shaida ne?"
Abu Turab yace " a'a sai dai na rage zargin da akema Ummana."
Yace " kana tunanin wannan ya isa?"
Kai ya girgiza alamar a'a yace " sai dai zai rage zagi da gulmar da ake mata, gaskiya kuma zan bayyanata ko ba yanzu, na kula in nace zan nemi gaskiya yanzu bazan taba samun komai ba dan na tabbata Magajiya ta riga ta gyara komai."
Sarki ya jinjina kai yace " na fahimceka."
Abu Turab yace " sannan maganar Gimbiya Bilkisu." Ya karasa fadar sunan yana susa keya.
Sarki yace " inajinka."
" Dama ina ganin zan shiga gunta karshen satin nan."
Murmushi mai Martaba ya saki yace " Naji dadi da fahimtarka da kuma amincewarka Allah ya kaimu karshen satin lafiya."
Abu Turab yace Ameen.
*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*44*
Mikewa Magajiya tai daga kan gado cikin tsananin takaicin abinda Turab ya mata, abin haushi jitai baiwarta tana sanar da ita isowar baki dan tayata murnar warkewarta.
Haka ta bada umarni suka shigo, kan gado ta koma ta zauna, kowa yazo tayata murna sai ya jinjinama Turab da kokarinsa wannan abu yafi kular da ita, wasu dan gulma ma so suke suji me ya had'a Abu Turab da Abdulmajid.
In taji haka sai dai kawai tace " zancen mutane ne kawai amma su ba abinda ya had'a su."
Sai wajen Magrib ta samu sauki tai wanka ta sa kaya sannan ta aika a kira mata Hisham.
*******
Mairo kuwa bayan ta ba Umma magani nan ta dafa mata abinci ta bata taci, suna zaune labarin abinda ya faru ya isomusu, wannan labari yasa Umma dan jin dama dama.
Mairo kuwa jitai Abu Turab ya kara birgeta, ba shakka jinin sarauta ma yawo a jikinsa, ba shakka kwakwalwarsa da basirarsa tana aiki.
Sai wajen Magrib ta baro bangaren, Basira nata mata godiya, tana tafe tana murmushi dan ba shakka hankalinta ya kwanta da abinda ya faru.
Sam bata kula da shi ba tadai san ta wuce wasu daga gefenta sai dai bata san su waye ba.
Tana tafiya kawai taji an cafko hannunta ta baya.
A tsorace ta juyo, dan sai da gabanta ya fadi lokacin daya rikota.
Kallan mamaki da takaici ta sakar masa, sannan ta kalli hannunta tace " Malam sakeni ko"
Yace " ina san magana dake."
Tace " To dan kanasan magana dani sai akace ka rike min hannu? Sakeni tun kafin mutane su gamu."
Ga mamakita gani tai ya kara kankame hannunta yace " kina tsoron aganmu ne?"
Kokarin kwace hannunta ta shiga yi tana cewa " meye hakan?"
Abdulmajid ya matso daf da ita kamar zai rungumeta tsoro yasa tai baya, karfi yasa ya rikota, cikin murya mai kama da rad'a yace " zaki biyoni ko sai na rungumeki anan?"
Idanu ta zaro ta cigaba da kokarin kwace hannunta.
Murmushi ya sakar mata yace " Gimbiyata muje ko?"
Ya karasa maganar tare da sakar mata hannu sannan ya nuna mata hanya.
Harara ta makamai sannan tai hanyar daya nuna mata.
Bangarensa ta nufa da ita a tsakar gida taja ta tsaya tare da hard'e hannayenta.
Kallanta yai yace " muje mana."
Tace " muje ina kenan?"
Da kai ya mata alama da ciki.
Harara ta kara makamai tace " d'ad'in abin ni d'in da hankalina bawai a bola ka ganni ina tsince tsince ba."
Dariya yai sannan yama masu kula dashi alama da su fita.
Suna fita ya fara matsowa inda take, hannu ta d'agamai tace " dakata daga nan Malam ko kuma wlh insama ihu."
Yace " Wayyo da naji dadi, ni ai so nake kisamin ma ihun kinga duk abinda za'ayi na riga na mallakeki kenan dan Sarki zai sani auranki saboda rufin asirin mahaifinki."
Kallansa tai kallan tsana tace " wai dan Allah in tambayeka? Ana so dole ne?" Sai kuma ta girgiza kai tace " bama haka ya kamata ince ba, dan ba so na kake ba."
Yace " Mairo abinda zakice kenan? Wlh tunda nake a duniya kece mace ta farko da zuciyata take so, inaji a raina in har ban aureki ba to tabbas zan shiga wani hali."
Baki ta tabe tace " da alama bada gidan sarauta ka dace ba da d'an siyasa ka dace, to ni ko soyayyar ce nace banayi, ko anayi dole?"
Kallanta yai sai dai yanzu fuskarsa ta nuna alamun jin haushin kalamanta.
Mairo tacigaba " Akwai wanda nake so, banaji akwai wani karin bayani dakake nema daga bakina."
Tana fad'ar haka ta juya zata fita.
Da karfi ya jawo hijab dinta, jikin bango ya sata, idanunta ne suka firfito. ya kalleta ransa a bace yace " badai wanda kike so d'in a gidan nan yake ba?"
Kai ta juyamai bata bashi amsa ba, cikin takaici ya kara cewa " badai wanda kike so sunansa Abu Turab ba?"
Juyowa tai ta kalleshi tace " koma wanene wanda nake so d'in banaji yazama dole na sanar dakai."
Hannu yakai kamar zai kifa mata mari dan har ta rintse idanunta, sai kuma taji shiru, a hankali ta bud'e idanunta.
Kallansa tai, hannunsa ya ajiye sannan yace "Mairo ko duk duniya zasu had'u dan ganin ban aureki ba wlh sai dai kowa yayi ya gaji, amma wlh nine mijinki, inkuma harni Abdulmajid ban aureki ba to wlh duk duniya ba namijin daya isa auranki sai dai in bana dorar kasa."
Kafin ta nemo amsar da zata bashi gani tai yayi ciki.
Da kallo ta bishi tama rasa me zatace.
Haka ta fito jiki a sanyaye.
Jakadiya wacce tazo wucewa dan ta dawo daga duba magajiya ta hango Mairo ta fito daga bangaren Abdulmajid, kai ta gyad'a tace " abin harya kai haka?" Dan dama an sha kawo mata gulmar an gansu.
************
Hisham zaune a kilisar Magajiya shi kadai, sai dai kana ganinsa kasan tunani yakeyi.
Magajiya ce ta shigo cikin takunta.
Ta karaso ta zauna sannan ta kalleshi tace " Yaya na d'auka na sanar dakai umarnin mikewa in har zam shigo guri ko?"
Kallanta yai yace " tuba nake Magajiya hankalina ne ya tafi."
Girarta ta d'aga sama tace " a kiyaye."
A ransa yace " ki jira hawan Abdulmajid mulki, lokacin ne zan kiyaye."
Kallansa tai tace " Abu Turab ya wargaza mana shirinmu na hukunta uwarsa."
Hisham yace " ni kaina abinnan ya kona mun rai."
Murmushi tai tace " Abu Turab! Abu Turab! Lalai na yadda jinin Abdussamad na yawo a jininsa, dole ne in zamuyi shiri na gaba sai mun shirya yanda ya kamata."
Kallanta yai sannan yace " ni Magajiya ina ganin kawai mu mikashi kabarinsa."
Wani kallo ta bugamai tace " na d'auka na fadama ba kisa ko?"
Yace " haka kikeso to muyi ta yin shiri yana wargaza mana?har sai yaushene zamu d'aura Abdulmajid akan mulki? Sai mun tsufa? Ko......"
Tsawa ta daka mai tace " YAYA!
Kallanta yai tare da yin shiru, tace " kana tunanin ni Magajiya? Ni Gimbiya Magajiya wacce mulki da takama da isa suka bi jinina, kanaso kace ni wannan Magajiyar har wani yaro wanda na girmi uwarsa, wanda aka haifa kwanan nan zaici galaba akaina?"
Kasa yai dakai yace " Tuba nake ranki ya dade, ni din wa? Ina na isa ince haka? Kawai dai gani nai mutuwarsa tafi sauki."
Idanu ta juya tace" to nace banda kisa, sannan ina tunanin ya kamata Saifullahi ya kawo kudin gaisuwa, in har bamu isa raba Turab da Bilkisu ba dolene mu nemi wanda yakeda mukami a gomnati saboda kudi dan neman taimako nan gaba
"
Hisham yace " to Ranki ya dade angama."
Mikewa yai ya fito, yana fita yabi d'akin da harara yace " wlh zakisan ni kikema tsawa, duk 'ya'yan da kike takama dasu na waye? Daga khadijan har Abdulmajid d'in?
Kiyi ki gama wlh sai nima na gasa miki aya a hannu, wa kike dashi? Wa kike dashi da zai taimakeki? Harni zaki dingama tsawa? Harni zaki ce in mike dan zaki shigo?"
Kwafa yai sannan yai gaba.
**************
Magana ta lafa a gidan Sarauta, yau take juma'a yau kuma Abu Turab ya shirya shida Sabi'u dan zuwa garin na Kano.
Mai Martaba yasa ankawo kaya sosai wanda zasu kai gidan.
*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*45*
Sabi'u kamar jira yakeyi su shiga mota, suna shiga ya kalli Turab yace " Mutumina wai ta yaya basirar taimakon Magajiya yazo maka? Gaskiya ka birgeni da ka nuna musu kai dasu d'aya ne."
Abu Turab ya dafa kafad'arsa yace " baka kawo komai a ranka ba da akacema nine na kawo mata magani?"
Cikin rashin damuwa yace " sosai ma, abu d'aya ne yazomin na tabbas kai ba ruwanka."
Murmushi Abu Turab Yai yace " then it's okay."
Sabi'u yamai kallan mamaki yace " ban gane ba? Ba kai kakai mata magani ba?"
Nine mana.
Sabi'u yace "yauwa sannan dan Allah inada tambaya, wai wannan yarinyar menene tsakaninku?"
"Yarinya? Wacce kenan?"
Fara tuki yai yana cewa " yarinyar gidan Waziru wacce da na d'auka ni take kallo, sai daga baya na fahimci kai take kallo tun kafin idanun ka su dawo gari."
Kallansa Abu Turab yai sai dai ya kasa cewa komai dan tabbas kasan zuciyarsa begen Khadija yakeyi, dan ranar ya tabbata da b'acin rai ta tafi.
Duk yanda yaso ya tsani yarinyar abin yaci tura.
Sabi'u ne ya kalleshi, gani yai Abu Turab yai saurin maida kallansa jikin window.
Sabi'u yace " yauwa Khadija, na tuno sunan dai sai dana tambaya saboda gulma dake cina."
Abu Turab ya kwantar da kansa jikin kujera ya lumshe idanunsa yace a hankali yace " wacce ya kamata in tsana, sai dai a duk lokacin dana b'ata mata rai nakejin zuciyata na zafi."
A hankali yai maganar wanda Sabi'u sam baiji ba yadai san magana yake sai dai bai san jeyake cewa ba, hakan ne yasa yace " me kace?"
Abu Turab bai bud'e idanunsa ba yace " bakomai."
A zuciyarsa yace " Allah ka cire mata sona, bazan taba addu'a ko dana sani akan san da nake mata ba, dan ko da ace za'a maida hannun agoggo baya na tabbata i will fell for her, i will always pray for her happiness."
Sabi'u ganin kamar bayasan magana yasa yad'an yi shiru, can yace " Mutumina ni daga waya ne kuka dinke da Gimbiya Bilkisu ne?"
Abu Turab ya bud'e idanunsa yace " kaidai kanasan kaji gulma, koma me mukai menene damuwarka?"
Sabi'u yai dariya yace " wlh kayi babban tunani, kun bala'in dacewa da Bilkisu, tun randa na ganta na san ....."
"To malamin had'aka na sanjin gulmar soyayyar da