Showing 18001 words to 21000 words out of 146065 words

Chapter 7 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

kalleshi sannan tace " Basira bata dawo ba."


Kallanta ya sakeyi nan ma bai tanka ba, idanu ta runtse cikin alamar kunar zuci na tausayi tace " gobara ce ta kama da gidansu a daren jiya."


Lalai wannan kalma ta d'agamai hankali wanda bai san sanda ya mike tsaye ba, Magajiya ta kalleshi cikin kulawa tace " Yayanta da matarsa sun rigamu gidan gaskiya."


Sarki a tsaye yake kawai dan hankalinsa ya kai koluluwar tashi, ta cigaba tare da share idanu kamar irin mai kwallar nan, tace Basira da d'anta dai ba abinda ya samesu sai dai firgita datai da abin yasa ta fita da gudu wanda har safiyar yau ba wanda ya ganta.


Hankalin Sarki ya kara tashi ya koma Ya zauna dabas kamar ba sarki ba.


A hankali ta taso tazo inda yake tasa hannu ta kamo nasa hannun tace " nasani sarai hankalinka ya tashi sosai kamar yanda nawa ya tashi, shiyasa na rasa mai zance maka, Hisham tun safe yake nemanta amma ba labari wanda hakan ne yaga dole yazo ya sanar dakai asan abinyi."


Kallanta yai ji yake kamar ya saki wani irin ihu na bakin ciki, Magajiya cikin murya taban tausayi tace " Basira ba yarinya bace na tabbata zata dawo hankalinta ne ya tashi har yasa tai wani hannu sai dai fatan Allah yasa ta fad'a hannu na gari."


Sarki ya d'ago cikin tashin hankali wanda tunda Magajiya take bata taba ganinsa cikin wannan yanayin ba, kallanta yai cikin kakkausar murya yace " inasan kad'ai cewa."


Kai ta jinjina alamar to, sannan ta mike ba tare da tace komai ba tai waje.


Tana fita ta kalli kofar d'akin tai wani murmushi tace " kai da Basira sai a lahira dan duk yanda kaso ko ita taso baku isa ku kara zama tare ba bare har kaga d'anka ka fahimci menene d'a na jini."


Juyawa tai tacigaba da tafiya ana take mata baya cikin kasaita da tak'ama.


************




Shikam tana fita ya runtse idanunsa kam jiyai hawaye ya gangaro mai sau d'aya, mikewa yai yaje jikin tagar d'akin ya bud'e ya kurama taurari ido,jiyake kamar zuciyarsa zata fashe ga zuciyarsa ta fara masa sake sake mara amfani, yana tsaye yana kallan taurari sai dai a zahiri tunani ne fal ransa, nan ya shiga tunanin rayuwarsu da abokinsa da kuma matarsa ga kuma bai taba ma ganin d'ansa ba,kasa jure abinda ke ransa yai ya tsugunna a gun tare da dafe kansa wanda ya fara sara mai....




A wannan ranar Mai Martaba ko gadonsa bai hau ba bare ya samu danar rintsawa.




************


Basira ma bataga bacci ba a wannan ranar, tunani ne kawai ke mata yawo a ranta, ido ta kurama d'anta tana ji wani abu na taso mata, ya zatayi? Zama zatai tayi anan saboda tsoron kar wani abu ya samu d'anta? In tai hakan kenan ta raba d'anta da mahaifinsa, sannan auranta fa?"
Wad'annan tunanukan sun mata yawa fal aranta wanda sukasa idanunta suka kafe kaf.




***********


Magajiya ta sanar da Hisham yanda sukai da Sarki sannan ta sashi yaje ya nema ayima Basira magani akan karta waiwayi gida, a mata maganin da zaisa taji sam batasan gida."




********


Tun bayan tasowar Abu Turab suka kula da rashin ganinsa, da farko sun d'auka lokacin ganin nasa ne baiyi ba sai dai ganin ya kai wata 4 yasa suka fahimci akwai matsala da idanunsa, haka ya taso ba idanu sai dai Allah ya bashi hazaka wanda ko zama kai dashi na awanni sai ka fahimci hakan, yanada baiwa sosai ta fahimta da rike abu.


A duk sanda Basira tai tunanin komawa gida sai taji zuciyarta ta kuntata, hakan yasa ko maganar batasan a mata, Lantana kam ko da wasa bata taba tambayarta ba, haka mutanen gidan.


Abu Turab har yakai shekara 5, Baffa shi yake koya masa karatu, yana tsananin san yaron saboda san karatunsa da hazakarsa, Basira ta d'aurashi a kan tarbiyya mai tsananin gaske, ko laifi ya mata wanda bai kai ya kawo ba haka zatasa shi a tsakiyar rana gashi bashida ido sai yayi kusan awa uku a tsaye, gashi bai isa yai kuka ba, dan kuwa in ya kuskura yai to fa lalai zai gamu da hukunci mai tsananin gaske, a haka in ka kalleshi bazaka taba cewa baya gani ba dan kuwa idanunsa garau suke, bata bari a taimaka mai har sai intaga yana neman faduwa ko yana neman taimakon sosai, komai da kansa yake yi, zakasha Mamaki in har kaga yanda Basira take tsananta tarbiyar d'an nata.


Abu Turab ya taso mai tsananin jarumta gashi dama magana bata wani dameshi ba dan ko abokai bashida shi sannan yaro ne wanda in yana abu dole ka kalleshi domin jinin sarauta na yawo a jikinsa yana da jinkai sannan ko magana yakeyi zakasha mamaki.




Shigarsa Shekara bakwai ga tsufa ya kara kama Baffa, yanzu ko fita zaiyi sai an taimaka masa, a yau ya tashi da zazzab'i wanda yasashi zama a d'aki, Abu turab na zaune kusa dashi yana mai karatu kamar yanda Baffa ya sashi.


Bayan ya gama ne Baffa yace " D'ana(haka yake cemai.) kiramin Mahaifyarka."


Abu Turab ya mike rike da karamar sandar da yake tafiya da ita ya isa b'angarensu, A waje yaji muryarta hakan yasa ya matsa kusa ya sanar da ita sakon baffa.


Mikewa tai ta zura hijabinta ta fita, Lantana na zaune tana sana'ar mangyad'a wanda dashi suke rayuwa, ya matsa kusa da ita dan yanajin sautin aikin datake, zaiyi magana yaji tace " Ka zauna."


Tai maganar tare da tashi a kan kujerar ta ta nuna masa gun zama.


Shiru yai hakan yasa ta rike hannunsa ta zaunar dashi.


Murmushi yai yace " Lantana baki tab'a kiran sunana ba tunda nake dake."


Kasa tai da kai a ranta tace " ina na isa?"


Murmushi ya sakeyi yace " Kujerar da kike kai kika bani ko?"


Batai magana ba sai dai a ranta tace " dole na ne ai."


Mikewa yai ya nufi hanyar cikin d'aki."


*********




Basira zaune kusa da Baffa wanda ya ke a kwance, Baffa ya kalleta yace "Banso na miki magana da kaina ba sai dai inaji a jikina lokaci na ya kusa hakan yasa dole na kiraki."


Kallansa tai sannan ta maida kanta kasa, Baffa ya cigaba" Basira ya kamata ki koma gidanki inhar akwai aure akanki to fa lalai kina d'aukan zunubi ne."






Kallansa tai idanunta suka kad'a sosai ga mamakinsa hawaye yaga tana zubarwa.


Kallanta yai cikin tausayawa yace " ba tillasta miki nake ba sai dai shawara nake baki, in har da aure akanki nace nima ba wani abu ba."


Hawayenta ta share sannan tace "Sunana Basira.........."


Kaf abinda ya faru da ita ta sanar dashi.


Baffa hawaye ne ya gangaromai saboda tausayi, shiru ne ya biyo baya a d'akin domin kuka sosai takeyi miken dake binne a zuciyarta ya tashi.


Sun dade a haka kafin Baffa yahau addu'a, sannan yace" nayi zargin wani abu sai dai rashin sanin labarinki yasa ban tab'a sanar dake ba, sai dai yanzu zargin da nakeyi inaji ajikina hakan ne."


Kallansa tai cikin rashin fahimta, Baffa ya cigaba " D'ana, wato Abu Turab banaji a haka Allah ya halliceshi." cikin mamaki tace " kamar yaya?"


Yace " sihiri baya taba zama daidai da kaddarar Allah."


Idanu ta zaro tace " kana nufin....."


"kwarai da gaske, bazan rantse ba kuma bazan miki alkawari ba sai dai kafin Allah yad'au numfashina in dai har sihirine to ni zan karyashi da yardar Allah, sannan inaso kimin Alkawari In har d'anki ya warke zaki koma gun mijinki, Allah ne kadai yasan halin da yake ciki na rashin ku."


Basira tace " Nagode kwarai sai dai Baffa na rasa dalili sam banasan ai zancen komawata gidan."


Hannayensa ya had'e ya shafi fuskarsa yace " dole ki cire tsoro a ranki ki taimaki d'anki, ba wai dan ya hau mulki ba a'a sai dan tsira da rayuwarsa, kina tunanin taimakonsa kikai na kawoshi dajin nan? Ko kina tunanin zaki iya canza abinda Allah ya kaddara a kansa ne?"




Kai ta girgiza alamar A'a.


Baffa ya cigaba " Abu Turab inaji a jikina yaro ne wanda za'ayi alfahari dashi nan gaba, kada ki kuskura ki rabashi da mahaifinsa, ki zamanto mai yarda da kaddara mai kyau da mara kyau."


Hawaye ta share sannan tace " na maka alkawari inhar sihirine yana warkewa zamu koma in kuma ba shi bane ma zan maidashi gun Mahaifinsa."


"Alhamdulila, nagode da amfani da shawarata da kikai sannan inkinje ki turomin d'ana sannan ki bashi kaya kala uku a guna zai dinga kwana, yaro ne mai hazaka da ilimi wanda a shekara 7 ya haddace izu 30 wanda tunda nake ban taba ganin yaro mai wannan baiwar ba, ni dashi zamuyi yakin ganin mun warware komai."


Godiya sosai Basira ta shiga yi.





*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
ẞ 🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)





*HASKE WRITERS ASSOCIATION*


*Wattpad :-AyusherMohd*



*Na Ayusher Muhd🤸🏼*




*13*


Haka Baffa da Abu Turab suke wuni karatu da addu'oi kala kala sannan daga dare yashiga kashi uku Baffa yake tashinsa su shiga saloli da addu'oi, ko waje baya fita, a kwanansu na hud'u Abu Turab ya fara wasu mafarkai cikin dare yake farkawa wani sa'in da kuka sai dai daga ya tashi yake manta mafarkin.


Sun dage sosai da addu'oi, karatun qur'ani da saloli.


Yau satinsu d'aya kenan Abu Turab na kwance yana bacci hankalinsa a kwance, yau baccib dadi yake masa gashi ko mafarki baiyi ba, Baffa ya sa hannu ya tabashi yace "D'ana tashi lokaci yayi."


Mamaki abin yaba Baffa ganin bai tashi ba, kallan fuskarsa yai sai dai kana kallansa zakasan yana cikin kwanciyar hankali, Baffa yai murmushi sannan yai bismillah ya kara taba shi, addu'ar tashi daga bacci ya fara karantowa bayan ya gama ne ya bud'e ido a hankali duk da yasan duhu kawai zai gani sai dai me? Dishi dishi ya fara gani, cikin tsananin mamaki yace " Baffa ido na."


Baffa ya dafashi yace " menene? Me idan naka yai?"


Murza idan ya shiga yi, Baffa ya shiga karanto addu'oi yana tofa mai, Abu Turab ma yanayi.


Cikin tsananin mamaki da al'ajabi Abu Turab yaga tsohon dake kusa dashi, a hankali yakai hannu inda Baffa yake yace "Baffa!"
Kallansa Baffa yai shima ya kasa magana sai addu'a yakeyi Allah ya taimakesu.


Abu Turab ya tsugunna kusa dashi ya rungumeshi sai ya saka kuka.


Baffa ma hawaye ne ya zubomai dan ya fahimci ya ganshi.


Abu Turab cikin kuka yace " Baffa na ganka, Ina ganin komai ga katifarka, ga kayanka nan a lank'aye, ga kwanan abinci nan ga leda nan a tsakar d'akin, Baffa ina ganin komai."


Idanu Baffa ya lumshe yace " Alhamdulila lalai babu abin bautawa da gaskiya sai Allah."


Tashi muyi alwala muyima Allah sujjada.


Mikewa yai cikin wani jin dadi mara misaltuwa yai waje.


Bayan sunyi addu'ar godiya ga mahallici ne ya kalli tsohon yace " inje gun Ummana?"


Baffa yace " ka barta ta samu bacci zuwa asuba."


Nan ya zauna cikin zakuwa, sai kallan abubuwa yakeyi......


Ana asuba yai b'angaren da gudu jin kofar a bud'e ya shiga bugawa, Basira ta mike a d'an tsorace ta matso tace "waye?"


Cikin jin dadi Abu Turab yace " nine Umma."


Mamaki ne ya kamata da sauri ta bud'e, ya matso da gudu ya rungumeta yana kuka yace " yau Allah yayi na ganki."


Idanunta ne suka ciciko da kwalla, ya saketa sannan ya kura mata Ido yace " Umma na ganki, Umma naganki."


Rungumeshi tai itama tace Alhamdulila.


***********


Satinsa d'aya da warkewa Baffa ya kara kiranta ya mata maganar tafiya nan, tace nan zuwa kwana uku zasu tafi.


Zaune take a d'aki tana kan gado Lantana na kasa haka shima D'an nata.


Kallansu tai tace "inaso duk ku bani hankalinku, akwai abinda nakesan sanar daku masu mahimmanci guda biyu."


Tai d'an ajiyar zuciya sannan tacigaba" na farko zuwa jibi zamu tafi Zariya."


Da sauri Lantana ta kalleta shikam baisan me hakan yake nufi ba shiyasa bai wani damu ba.


Tacigaba " abu na biyu wanda yafi komai mahimmanci shine inaso Lantana kada ki kuskura ko da wasa ki nuna Abu Turab na gani."


Cikin mamaki ta kalleta, Basira tace "wannan umarni ne ba shawara ba."


Da sauru Lantana tace " angama Ranki ya dade."


Basira ta kalli Lantana tace " d'an bamu guri."


Da sauri tai waje.


Basira ta kalli d'anta ta mikamai hannu hakan yasa ya mike tare da zuwa inda take.


Basira ta zaunar dashi kusa da ita sannan ta rike hannayensa biyu tace " nagode kwarai da baka tab'a tambayata mahaifinka ba."


Kallanta yai sannan yai murmushi, ta cigaba " ka nutsu sosai da abinda zance maka."


Kai ya d'aga alamar to sannan ya kada nutsuwa, tace " zamu koma gidan da mahaifinka yake wato gidanku sai dai ina tsananin tausaya maka, da farko inaso kada ka nunama kowa kana gani, hatta mahaifinka ka zama makaho a gaban kowa, ka zama mai ido agabana kad'ai."


Cikin mamaki yace " me....."


Kallan datai mai yasa yai shiru, tacigaba " banaso ka tambayeni dalilin hakan dan kuwa inka mallaki hankalin kanka na tabbata dakanka zaka sanar dani komai, domin zaka samu cikaken amsar tambayarka."


Kai ya d'aga alamar to,tace " Abu Turab!"


Yanda ta kira sunansa da kakkausan murya yasa ya kalleta jiki a sanyaye, tace "kamin alkawarin zakai wannan abin?nasan kasan me alkawari yake nufi a muslunci ka kuma san hukuncin wanda ya karya."


A hankali yace "na miki alkawari ko mai zai saman bazan nuna ina gani ba."


Ajiyar zuciya tai na jin dadin baiwar da Allah ya mata wato na azurtata da wannan yaron, tacigaba " gidanku ba kamar gidajan daka sani bane, dolene ka nutsu kaji me zance, da farko duk yanda ranka yaso da b'acci banaso ka nuna, sannan abu na biyu banaso ka zama ragon yaro."


Kallanta yai baice komai ba, ta riga tasan wannan sai dai ya zama tuni amma tun yana karami ta horar dashi akan haka, ita dama matsalarta shine taurin kansa dan inbaiyi niyyar abu ba ko za'amai dukan dazai kasa tashi tofa bazaiyi ba, wannan hali nasa shi take jiye masa.


Ta riga ta d'au alwashin sadaukar da komai nata dan ta kare d'anta.


Sun dade rike da hannu juna tana mai fada a karshe tace " in muka koma gun Mahaifinka banaso ka yawaita cewa komai sai ni, dolene ka rage nuna damuwarka akaina, kallan mamaki ya mata a ranta tace (in aka fahimci nice komai naka to lalai za'a nemi yin amfani dakai da sunana wanda nikuma ba lalai in iya kwatarka ba daga hannun makirai."


Abu Turab zaune kusa da Baffa yana jin nasiharsa sun dade suna hira kafin Shehu yazo su zauna, Abu Turab yanajin hirar tasu har bacci ya d'aukeshi.


Sukam sunyi hira sosai, da shehu ya mike zai tafi sai yasa hannu zai d'auki Abu Turab akan kaishi b'angarensu.


Baffa yace " barshi anan so nake na kwana dashi."


Nan Shehu ya ajiye shi ya tafi, Baffa ya d'auko rubutun daya wanke ya tashi abu turab yace ya wanke fuskarsa har zuwa kansa, yana magagin bacci ya wanke sannan ya kwanta, Baffa ya dinga mai addu'a sannan ya kwanta.




Jin kiran Sallah yasa Abu Turab ya mike, mamaki ne ya kamashi ganin Baffa a kwance yana bacci, kusa dashi ya matsa ya shiga tashinsa, hankalinsa ya tashi ganin ko motsi bayayi.


Da gudu yau cikin gida b'angaren Shehu, a waje ya sameshi yana alwala matarsa na tsaye kusa dashi.


Abu Turab ya kalli Shehu yace " Kawu kazo Baffa yaki tashi daga bacci."


Inalilahi wa ina ilaihi Raji'un wannan kalma ita Shehu yai ta ambata, dan ko ba'a fada ba ko bai gani ba yasan me hakan yake nufi.....




Allah ya jikan Baffa da Rahama Ameen........




*********




A ranar da akai uku su kuma suka shirya tafiyar tasu.


_Wannan kenan_








*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)





*HASKE WRITERS ASSOCIATION*


*Wattpad :-AyusherMohd*



*Na Ayusher Muhd🤸🏼*


_'Yan grp na Kainuwa Dashen Allah ga naku shafin, tnx 4 d love....._


*14*


Sun shirya tsaf ba kaya suka d'auka ba dan komai nasu anan tabarma matan gidan saboda tasan inda zasuje.


Shehu shi ya kawosu inda zasu hau mota dan a wannan shekara wato ta 1978 (shekarar Abu Turab 7 sannan shekararta takwas da aure.) a wannan lokacin an sanu cigaban wata yar kurkurar mota bayan akuri kura da motar itace, sai da suka shiga sannan Shehu ya musu sallama ya juya ya tafi, matansa sunsha kuka dan kuwa Basira ce silar zaman lafiyansu.


A hanya Basira sai kara jaddadama d'anta takeyi akan abinda takesan yayi.


Daga baya bacci yai awun gaba dashi, Lantana ta kalleta sannan tace " Ranki ya dade inasan tambaya duk da dai ba hurumi na bane."


Basira ta kalleta alamar tana ji, Lantana tai ajiyar zuciya sannan tace " me zakice ya hanaki komawa? Dan ina tsoron kar a miki wani sharrin."


Basira tai murmushi tace " Lantana kenan, a da na yarda ni sukuwa ce wacce bata tunanin abinda zai faru, sai dai yanzu inada abinda nakesan karewa dolene in canza daga sukuwa zuwa nai dabara, karki damu." ta karasa maganar tare da dafata.


Sun dade suna tafiya kafin a d'an tsaya saboda wasu yaran na mota najin fitsari, nan fa aka fifita hardasu Abu Turab, bayan an dawo ne aka ci gaba da tafiya.


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login