Showing 69001 words to 72000 words out of 146065 words

Chapter 24 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

bata shafeka ba, wai ni Sabi'u kai yaushe zakai aurene?"


Turab ya katse shi daga maganarsa.
Sabi'u yai d'an ajiyar zuciya yace " lafinka ne da ka rufe kofa, ai da ka bari an ma kanwa da ba haka ba."


Turab ya girgiza kai kawai baice komai ba, sai murmushi kawai dayai.
Sun d'anyi niss ba tare da kowa yace komai ba, can kuma Sabi'u ya d'an cigaba da jansa da hira haka jefi jefi.
Bayan sun isa garin kano, Mai Martaba Sarkin kano yasa an gyara musu b'angaren da suka zauna waccan karan.
Shamaki yazo ya musu iso, sai daya tabbatar an kawo musu komai na bukata sannan ya tafi.






**********
A zariya kuwa Magajiya zaune a d'aki, Abdulmajid na kasanta.
Cikin muryar takaici take cewa " Abdulmajid wato kai bakada kishi ko? Bakasan darajar kanka ba ko? Kana kallo Abu Turab ya tafi kano gun Gimbiya Bilkisu amma kai ko a jikinka, wai me yasa ne sam kwanan nan baka abinda zai amfaneka?"


Fuskar Abdulmajid a had'e yace " Umma to ya kikeso nayi? Kina gani dai Mai Martaba ya fifitashi a kaina, in ba haka ba ta yaya banyi aure ba ya nema ma kanina aure?"


Magajiya ta mai wani kallon takaici tace " wannan matsalarsa ce, duk da inada takardar da take na shaidar amincewa da yardarsa akan kaine zaka gajeshi sai dai a koda yaushe zuciyata da hankalina sun kasa kwanciya, nasan Abdussamad sarai zai iya yin yanda takardar zata zama bata da amfani nan gaba, dan haka dole ne mu nemo ma mata kaima wacce take 'yar mulki."


Abdulmajid ya d'ago da sauri yace " Umma ki taimaken ki bar zancen wannan auren na 'yar mulki, ni Mairo nake so 'yar gid.
...."
Kamin shiru ko sai na kifa ma mari? Kana tunanin na sha guba saboda inji wannan shirman naka ne?


Shiru Abdulmajid yai kansa na kasa.
Ta cigaba " inasane da duk fa abinda kakeyi a gidan nan, kar in kuskura in kara ji ancemin ma anganka da wannan yarinyar."
Abdulmajid ya d'ago ya kalleta idanunsa yai ja yace " amma Umma bakya gani auran Mairo zai taimakeni? Kinfa san yanda Mai Martaba yakesan Barde bakya tunanin zaiji takaicin rabasu?"


Kallansa tai sannan tai murmushi tace " Lalai Abdulmajid da gaske san Mairo kakeyi, tunda har tsarani kakeyi, to ni nace banaso."


Fuska ya had'e sannan yai kasa da kansa.
Wani kallo tamai tace " tashi kaban guri."
Mikewa yai ca sauri kamar dama can jira yakeyi.


*************


Gimbiya Bilkisu tana zaune b'angaren Fulani, lale aka sa mata tana jiran yaci.
Munnira ta shigo da gudu tacemata "UmmaBilkisu ya iso."
Sam bata kula da Fulani ba bata kuma kula da Bilkisu dake ta mata alama datai shiru ba.
Tana gama fadar haka ta kalli Fulani da sauri ta tsuke bakinta tace "Inna Barka da warhaka."
Ta karasa maganar tana zama a gefen Bilkisu.
Bilkisu ta harareta sannan tace " Munnira Muhsin d'in ya iso?"
Sunan kanin Munnira ne, Munnira ta kalleta alamar rashin fahimta.
Bilkisu ta harareta hakan yasa tai saurin cewa " ya iso."


Fulani ta saki murmushi tace " Bilkisu ayi maza a cire lale aje a kimtsa kafin Muhsin ya iso, yo dama ai nasan domin Muhsin akai lalan nan."
Ta karasa maganar tare da mikewa tai ciki.


Bilkisu ta rufe fuska da bayan hannunta dan tasan Mahaifiyar tata ta fahimci me suke nufi.
Tana shigewa, Bilkisu ta harari Munnira tace " Ba wakafi ba alamar tsayawa, baki kalkalkal ya iya wassafa zance, wai ke in kina magana bakya kula da mutanen dake zaune ne?"


Baki Munnira ta turo tace " Ni murna ne yasa wlh sam ban kula ba."


Bilkisu ta kara harararta tace " murna? Dan kina murna sai kisa a gane komai?"


Munnira ta turo baki tare da kumburo fuska, Bilkisu tace " na daina ma had'awa dake."


Munnira tai kamar zatai kuka, Bilkisu tace " jeki ki duba to kiga ko akwai wani abu da suke bukata."
Munnira cikin zakwad'i ta mike tai waje.


Bilkisu tai murmushi tare da yin kasa da kanta.




**************


Abu Turab yai wanka sunyi sallah sannan suka zauna cin abinci, Sabi'u ne yace " Turab jiya ai munsha hira da Babanmu, na tausaya ma Mahaifinka wlh."
Turab ya mai kallan tambaya, sannan yace "name?"
Sabi'u yace " ya dade bai samu haihuwa ba, har fa ya fitar da rai da samun haihuwa."
Abu Turab ya kalleshi sai dai baice komai ba.
Sabi'u ya cigaba " Magajiya fa har kasashen waje ta fita saboda neman magani amma ba labari, sai daga baya kawai akace ciki gareta, kumafa inaji sai da cikin yakai wata 3 sannan inaji itama ta sani."


Kallan sa yai cikin rashin kulawa yace " lalai."


Sabi'u yace " kasan abin dariya?"
Abu Turab ya kalleshi.
" duk fa farko wai mutane dayawa basu yarda da cikin ba, harshi Mai Martaban."


Abu Turab ya kalleshi yace " ban gane ba."
Sabi'u yace " kasan Magajiya kowa yasan yanda takesan ta haihu shi yasa mutane sukai ta zargin ko ta fadane ba wai gaskiya bane."


Abu Turab ya mike yace " Lalai, kace sai da ta haihu suka yarda." Yai maganar cikin salon rashin damuwa da kuma gamsuwa da labarin.
Sabi'u yasa dariya yace " shiyasa randa aka haifi Abdulmajid ai anyi murna wai kamar ba gobe."
Baki Turab ya tabe a ransa yace " ni kuwa sanda aka haifen mutane fiye da rabi bakin ciki sukai, wasu ma tunani hallaka jaririn yaron sukai."




Ciki ya shiga dan zuciyarsa ta karaya da tunowa da wahalar da mahaifiyarsa tasha.


Kwafa yai daya tuna sharrin da suka ma Mahaifiyarsa, tabbas dole ne ya sa tun a duniya a hukuntashi.


Mikewa yai ya d'auko turare ya fesa ya sa hularsa ya d'auko takalmi ya saka, yayi kyau sosai da sosai.

Yana fitowa Sabi'u yace " kai Ango, gaskiya yau inaji sai na rufe kofa dan banaji Gimbiya zata barka ka taho, ko dai in aikama da bargonka can ne? Dan banaji ana san rakiya ta."
Turab ya kalleshi yace " ba sai ka aikp da bargo ba itama ai tana dashi, d'an rainin hankali, ni taso muje karakani."


Sabi'u ya mike yana dariya........








***********
A can gidan Waziri kuwa Khadija tun ranar ko waje bata sake yi ba, kullum tana d'aki, abin duniya ya daneta, takaicinta d'aya yanda zuciyarta ta matso dasan ganin Abu Turab.
..
















🤝🏻 *TEAM ABU TURAB*






🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


_Ina 'yan group na fans d'in kungiyar Haske Writer's? Ina kuke 'yan group d'in The Queen Bee? Ga taku sadaukarwar, wannan shafin sadaukarwace gareku....🤝🏻_


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*46*




Jakadiya ce tazo dan kaisu inda aka tanada dan ganawarsu, an kayata gurin sosai, gun kamar rumfa yake, salo da kayata gun da akai duk yanda kaso da karka nuna sai gun ya burgeka.
Gashi sai hayaki na turaren wuta ne ke tashi.
Sabi'u cikin mamaki yake kallan gun ya kalli Turab wanda shikansa abin ya kayatar dashi yace " Kai gun nan ya burgeni, amma dai ba dan kai aka shirya gun nan ba ko?"
Abu Turab ya kalleshi yace " kai kuma sarkin zuga zugi, to kardai ka wuce makad'i da rawa."

Sabi'u ya kara shan mamaki ne a sanda yaga yanda aka saka irin carpet da 'yan tumtum a gun sannan aka jera kayan ciye ciye kala kala, ya jinjina kai yace " Turab da alama gaisawa kawai zamuyi da Bilkisu banaji anyi wannan shirin dan mu biyu."
Cikin gatse Turab yace " Gaisuwar ma sai ka hakura."
Sabi'u yace " ahh lalai Turab abin ba kara? To bari inje waje in tsaya in yaso in kungama ganawar na shigo daga baya mu gaisa."


Turab kai kawai ya girgiza, ya juyo da niyyar mai magana yaga bayanan.
D'an tsaki yaja kad'an yace " Sabi'u kenan."


Zama yai a gun da aka shirya dominsa, irin zama na manyan 'ya'yan Sarki.


Sai dayai minti 15 da zama sannan wani dadadan kamshin turare ya bugi hancinsa.
Cikin isa da takama take takowa, tafiya takeyi irin ta kasaitatun mata masu mulki.


Bai d'ago ya kalleta ba haka itama ko data shigo kallo d'aya ta masa ta cigaba da takunta.


Har sai da ta iso gun da zata zauna sannan ya d'ago ya kalleta, itama a lokacin ta kalleshi.


Tabbas yarinyar tana da kyau, balle yau datai shiga mai kyau sosai sannan tai kwalliya haka, wani sansanyan murmushi ta sakar masa, shima murmushin ya maida mata, a hankali ta zauna sannan ta umarci bayinta dasu fita.


Shiru ne ya ratsa gun kafin cikin muryarta mai dadi tace "Barka da isowa Yarima Turab."


Kallanta yai cikin yarda da amincewa yace " Barkanki da isowa Gimbiya Bilkisu."


Murmushi tai sannan tace " ka dade a zaune ko?"
" Ya zama dole ai in jiraki tunda haka tsarin yake, sannan ba wani dadewa nai ba."


Bata ce komai ba sai shiru da suka sakeyi.
Kanta na kasa, batai zato ba sai jitai yace " Bilkisu." Yanda ya kira sunanta sai dayasa taji wani yarr a jikinta.


D'agowa tai a hankali ta kalleshi idanunta sun canza zuwa salon soyayya, murmushi yai yace " Naji dadi da yanda kika amince da ni."
Idanunta ta lumshe sannan ta bud'esu.
Yacigaba " ban taba zatan zaki yarda dani ba haka, duba da rashin sani na da kikai, tunda haduwarmu d'aya dake."


Nan ma idanunta ta kara lumshewa ta bud'e, yace " A wannan lokacin na sa ma raina tabbas zaki zama mace ta gari a gun duk wanda kika aura, sannan na yaba sosai da yanda kike da tunani."


Murmushi ta saki sannan ta maida kanta kasa, hannayenta ta had'e gu d'aya tana murza zoben hannunta da d'aya hannun.


Harya d'auka bazatai magana ba sai jiyai tace " I can feel the pain that hide behind ur smile Turab."


D'agowa yai ya kalleta sai dai jikinsa yai sanyi, kallansa tai tana murmushi tace " me zakace game da ni?"


Kallanta yai kallo mai alamar tambaya.
Kanta ta d'an karkatar tace " ka taba sanin Fulani ba ita ta haifen ba?"


Idanunsa ne suka fifito alamar mamaki, Tace " bansan ta ba, bansan ya kamanninta suke ba, tana haifata a gun Allah ya mata cikawa."


Tausayinta ne yaji ya kamashi.
Idanunta ne suka d'an ciciko tace " karka kallan da fuskar tausayi Turab, i am okay, tunda dadewa na cire san ganinta a raina, sannan ina ganin in har na nuna damuwata akan mahaifiyar data haifen ya Fulani wato mahaifiyata ta yanzu zataji?"


Turab ya kura mata ido yana nazarin kalamanta. Can yace " U are indeed a good woman, sai dai jin zancen nan naki yasa na fara tunani ban kai qualification na aurenki ba, kin cancanci saurayin da zai soki kamar ransa wanda zai kula dake har rabuwa ta rai ta zo."

Hannu tasa ta goge hawayen daya d'an gangaro ta kwarmin idanunta tana murmushi tace " kai bakada confidence na sona kamar haka?"


Jitai yayi shiru sai dai yanayin kallan da yake mata ya canza, kallansa tai tace " Me kake nufi?"


Yace " Bilkisu inada abubuwa da dama a gabana wanda sai na ga sun kammala ne hankalina zai kwanta, banida lokacin soyayya ko farin ciki sai na ga mutanen nan an musu hukunci."


Shiru yai dan tuno abinda aka ma Mahaifiyarsa.


Baiyi tsamani ba bai kuma ji alamun tasowarta ba sai gani yai ta mikomai kofi.


Kallanta yai idanunsa sunyi ja, sannan ya kalli kofin ruwa ne a ciki alama tamai da kai akan ya amsa.
Hannu yasa ya amsa yana murmushi, yace " sry......"
Katseshi tai tace " naji dadi."


Fuskarta d'auke da murmushi tace " naji dadin yanda ka nunamin, yarda harka ke sanar dani hakan."


Kofin ya ajiye bayan ya shanye ruwa ciki yace " Bilkisu i....."
Kara katseshi tai tace " is okay, na fahimceka, na kuma san tabbas akwai wahalhalu da kasha ko fansar wani abu da kake san d'auka, sai dai inaso in taimakeka gurin d'aukar wannan fansar, bazan nemi soyayyarka ba har sai ka kammala abinda zakai, sai dai kaima bazan yarda kaso wata ba har zuwa wannan lokacin, in kuwa har da wacce kakeso yanzu inaso ka ajiye soyayyar a iya kacin zuciyarka harsai ka gama aiwatar da abinda zakai, a wannan lokacin ne nakeso ka tambayeni abu d'aya."


Idanunsa na kanta tacigaba " inaso ka tambayeni in har banyi dana sanin auranka ba, in har nace ma banyi dana sani ba to inaso ka tirsasa zuciyarka ta soni in har aka kai wannan lokacin baka sona, in kuma har nace nayi dana sani inaso ka tambayeni abinda nakeso a wannan lokacin."


Tana gama fad'ar haka ta koma ta zauna sannan ta d'ago ta kalleshi tace " Deal?"


Bai san sanda wani murmushi ya bayyana a fuskarsa ba yana murmushi yace " Deal! sannan naji dadi da kalamanki, ba saki a tsarin aure na ko da shi kike tunani a karshe sannan yanda kika amince dani ba tare da kinji abinda nakesan aikatawa ba, zanyi kokari wajen ganin bakiyi dana sanin aurena ba."




A tare sukama juna murmushi nan tamai alama da hannu akan yaci abinda aka kawo masa.





Tabbas tana bala'in san yaran nan, ko da kuwa zatai dana sani akan auransa bataji zata iya rabuwa dashi a wannan lokacin, sai dai ta d'au alwashin taimaka mai da tayashi d'aukan fansa akan duk wani wanda ya cutar dashi ko da kuwa zatai amfani da karfin mulki na mahaifinta ne.


Kamar yasan me take tunani jitai yace " for using you, dole ne ma nemi yafiyarki, sai dai zan nemane in na gama komai, is that okay?"


Kai ta jinjina mai alamar eh, ta bishi da kallo na so tsantsa.


Bayan sun gama hira ne ya mata sallama sannan ya mike, har ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya tako a hankali zuwa inda take.


Awarwaro ya ajiye mata wanda suke cikin gidansu sannan cikin magana mai kama da rad'a yace " da kunyar badawa nakeyi, sai dai bani na siya ba Sabi'u ne ya siyo"
Mikewa yai ya fara tafiya, kallansa tai tana murmushi tace " nagode."


Bai kara magana ba yai gama yana murmushi.
Tabbas Bilkisu ta samu daraja a idanunsa, yanaji zai iya zama da ita a rayuwar aure dan dama ya ma cire burin ganinsa da Khadija daga sanda yaji abinda mahaifinta ya musu ko da santa zai zama ajalinsa bazai taba yarda ya bakanta ran mahaifiyarsa akan 'ya mace ba.


















*🤝🏻TEAM TURAB*

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*47*




Duk yanda taso ta danne zuciyarta ta kwanta ta kasa, mikewa tai ta zura alkyabbarta sannan ta kalli Mai kula da ita tace " yau kwanan waye?"
Kasa tai dakai tace " naki ne ranki ya dade."
Magajiya ta d'an d'aga gira sama sannan tace muje inasan ganin me martaba.
Tayi mamaki sosai dan rabon da Magajiya taje turakar mai martaba da niyar kwana har ta manta.


Haka suka fito suka nufi b'angaren Mai Martaba.
Sunje shiga soro bangaren nasa sukaji ana gulmar Abdulmajid da Mairo, d'ayar tace " wlh jakadiya ce ta gansu da idanta yar gidan Barden ta fito daga b'angaren Yariman."
Magajiya ta cusa kai suna ganinta suka rude a tsorace suka tsugunna sukace " Barkanki da zuwa Magajiya."


Kallansu tai fuskarta dauke da iza tace " ina san dukanku kuje bangarena ku jirani, kada kuma ku manta a tsaye nakeso kuntsaya har na iso."


Kara runkufawa sukai suna neman bada hakuri, wani kallo ta musu da ya sa sukaja bakinsu sukai dif.


Nan suka karasa ciki.
Jakadiya ce ta fito da sauri kana kallanta zaka gane abinci takeci ta taso.
Wani banzan kallo Magajiya ta mata, da sauri tai rusuna tana gaisheta.
Magajiya bata amsa ba sai alamu da ta mata na ta mata iso.
Mikewa tai ta nufi b'angaren Sarki.


Rubuce rubuce yake tayi, yana jin sallamar Jakadiya yai saurin had'e takardun nan ya sa a kasan carfet din da yake kai.
Jakadiya ta shigo ta gaisheshi sannan ta sanar mai da zuwan Magajiya, alama kawai ya mata da kai akan ta shigo.


Magajiya ta shigo ta zauna a inda ta saba zama, sannan ta kalleshi tace " Barka da dare Haikawa."


Sarki ya amsa sannan yace " lafiya dai da daddaren nan?"


Tace " ina tunanin yau kwanana ne? Banaji na cancanci inji wannan kalmar daga bakinka."


"Kwana? A tun wani karnin kenan?"
Murmushi tai sannan tace " Turab na garin Kano ko?"
Kallan ta yai sai dai bai amsa mata ba, a ransa yace abinda ya kawoki kenan?"
Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace " na yaba da d'ana Turab ba shakka yanada hazaka da tunani, ina kuma kara godemai da maganin da ya bani."


Sarki ya jinjina kai yace " ai dama hakkin d'a ne ya kula da uwarsa, in har ita uwar tana neman cutar dashi to shi ya kamata ya nuna mata yana santa."


Kura mai ido tai dan tasab magana yake gwab'a mata.
Isakar ta d'an firzar kadan tace " haka ne, sai dai inaso uban d'an ya cigaba da nunama d'an nan hanyar dazai kula da mahaifiyar tasa."


Murmushi Mai Martaba ya saki tare da d'an juya kai kad'an harzaiyi magana sai kuma ya fasa.
Kallansa tai dan fuskarta cikin fara'a tace " yaushe zaka yima babban d'anka mata? Dan na tabbatar kanada babban buri akansa shiyasa ka kasa yimai cikin gaggawa
"
Ya fahimci me takesan cewa hakan yasa yace " ni ai danayake na d'aura buri akansa shiyasa nai tunanin barinki ki nemomai mata."


Fuskarta ta tsuke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login