Showing 81001 words to 84000 words out of 146065 words
Chapter 28 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt
yanzu mikin da ke b'oye a zuciyar matarnan sai data taso mata dashi hankalinta ya kwanta, lalai yaji dadi da mahaifiyarsa ta sanar dashi komai kafin rana irin ta yau, da bai san yanda zaiji maganar nan ba.
Murmushi ya sakar mata ko ince yake ya mata yace " Sai me Ummana? Iya kace mutane su gujemu to sai me?"
Kallansa tai cikin kunar zuci tace "kanaso kacemin baka fahimci me take nufi ba? In har magana ta fito zargin tsatson ka za'a shiga yi, in kuma ba haka ba sai dai kabi umarninta ka auri Mairo shikuma Abdulmajid ya auri Gimbiya."
Gani tai yasa dariya mara sauti yace " ohh wannan shine dalilinta?"
Basira ta kallshi tace " Kana tunanin Sarki zak taimakemu ko? Ka cire wannan a ranka in har kana wannan tunanin, Sarki ne shi kafin mahaifinka ko ince kafin ya zama mijina.'
Turab yace " Umma kin taba gani nace Sarki ya ya shiga ko ya taimakamin a yayin da matsala ta kunno min kai? Sai dai inje gun Abba na dan neman shawara, sannan maganar auran Bilkisu da Mairo duk wannan lamari ne na ubangiji Allah shine yasan matar da Abu Turab zai aura, Allah shine yasan ko dukansu zai aura, Allah ne yasab ko duk cikinsu ma ba wanda zan aura, sai dai nasan abu d'aya duk yanda zanyi bazan bar Abdulmajid ya auri Mairo ba saboda kamar kanwa take a gurina, sannan bazan bari ya auri Bilkisu ba saboda yarinya ce wacce bata cancanci miji kamar Abdulmajid ba."
Yana kaiwa nan ya juya zuciyarsa fal da bakin ciki.
Sam ya rasa ma ta ina zai fara.
Har bayan Magrib ya rasa mafita kawai ya nufi b'angaren Mahaifinsa.
Jakadiya ta matso ta gaisheshi sannan tace "Ranka ya dade Magajiya tana ciki."
Magajiya?
Ya maimaita yana kallan Jakadiya.
Jakadiya tai gyad'a kai tace "Sai dai ka dawo gobe inkuma kanaso in sanar masa."
Turab ya girgiza kai sannan yace "Barshi, sannan karki sanar mai da zuwana ko daga bayane."
Tace "to."
Harya juya ta biyoshi da sauri tace "Yarima."
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalleta yace"Lafiya?"
Daurewa tai tace "naji abinda ya faru, sai dai abu d'aya na isa fad'ama wannan abinda ta shirya reshe zai iya juyawa da mujiya, dan kuwa Magajiya tanada babban sirri duk abinda ake tunanin nata ne ba nata bane."
Turab ya kalleta cikin mamaki yace "Jakadiya ni fa......"
"Na barka lafiya Ranka ya dade, kai mutum ne mai zurfin tunani da kaifin basira zaka gano abinda nake nufi in har Allah ya nufeka da ganowa."
Ta juya tai gaba.
Da kallo ya bita sannan ya juya yai gaba.
*************
Abdulmajid wanda bayan shigarsa fada yana neman yin magana mahaifinsa ya mai wani kalli wanda kwarjini yasa ya kasa karasawa.
Ana magrib kuwa ya zari mota yai gidansu Mairo.
Tana xaune a waje ta kurama sararin samaniya ido tana kallan yanda yanayin duhun gari yake, yaro ne ya shigo yai sallama sannan yace " wai ana kiran Mairo."
Mairo ta kalleshi tace "inji wa?"
Yace "wai mijinki."
Kwafa tai sannan ta ciji lab'anta ta kuma mike da sauri, mayafita kawai ta zura tai waje dan ko Mamanta bata sani ba.
Yana cikin mota yana ganinta a tsaye a soro ya fito da sauri yana murmushin jin dadi.
Itama murmushin ta maida mai hakan yasa yaji kansa ya fasu.
Ya karaso gunta yace "Mairo na."
Tace "Yarima na."
Kallan mamaki ya mata sannan yasa dariya sosai yace "Mairo kece kuwa?"
Tace nice, kana mamaki ne?
Fuskarsa ya shafa cikin jin dadi sannan yace " Sosai ma "
Wani banzan kallo tamai tace "Kana tunanin haka zan ma in ka min ta karfi?"
Kallan tai yai yace "me kik....."
Katseshi tai tace " please Abdulmajid ka tashi daga wannan wawan baccin da kakeyi, wlh wlh in har ka kuskura ka dage da aurena har aka yi wlh ina tausaya maka da ni kaina dan a yanda nakejin tsanarka komai zai iya faruwa, dan wlh dana aureka gwara na auri talaka wanda bashida komai."
Jiyai zuciyarsa ta d'au zafi yace "Mairo how can u?"
Tace "me? Kana tunanin sunyi kadan kalaman nawa Busuru kawai, ka lalata 'yan mata sannan ka nemi auren wacce batasanka? Ko kana tunanin nima so na kake?"
Ta kalleshi cikin takaici tace "Aurena? Hmm please go ahead, a kaini gidanka inga ko zaka samu abinda kakeso."
Taja dogon tsaki zata juya.
Hannunta ya rike da sauri yace "Mairo taya zaki fadamin bakaken maganganun nan ki tafi?"
Ta makamai harara sannan ta kalli hannunta daya rike tace " sakeni ko?"
Kallanta yai sai taga ya sa dariya yace " Mairona in baki shawara? Ki bala'in kwantar da hankalinki ki aureni cikin farinciki dan wlh duk duniya ba wanda ya isa ya aureki sai ni nan Abdulmajid d'an Magajiya da Abdussamad."
Hannunta ta fizge tai cikin gida.
🤝🏻 *SASSANIN KUNGIYA TA ABU TURAB SADAUKI🏇🏻*
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*54*
D'agowa yai cikin tashin hankali ya kalleta yace" me?"
Idanu tad'an juya tace " Na yaba da kokarinka wajen ganin ka kare hakkin matar so, sai dai duk yamda kaso ka b'oye sirrin nan matar ki ta gano komai."
Tambayar ki nakeyi me kike nufi?
Ta sakar mai lalausan murmusji sannan tace " Ya zamuyi ai dolene mu cigaba da b'oye sirrin nan, gaskiya na tausayawa kanwata Basira fyad'e ai mugun abu ne."
Tai tagumi kamar wacce take cikin halin tausayawa tace " Ya zamuyi in zancen nan ya fito? Sannan wace dabara kai nikam dan a sanda ka kawo Basira gidan nan tabbas ankawomin zanin gadon dake d'auke da budurcin ta."
Tai ajiyar zuciya tace " Hmm ni yanzu tsorona ma kar a maida zancen daga fyad'e ya koma karuwanci kasan mutanen mu akwai matsala."
Tsananin tashin hankali je ta gani karara ya bayyana a idanun Abdussamad.
Mikewa tai ta tako a hankali zuwa gabansa sannan ta tsugunna tace " Tuba nake ranka ya dade dan bakina yayi kuskure dan tuni na tura mata d'anta akan yaji meke faruwa."
Zuciyata ta turnukoshi ya kalleta wani irin kallo na tsana da kiyayya, kai ta juya sannan ta kalleshi idanunta sun canza kala tace " Ba sai ka min kallan tsana ba, na dade da sani tsana da kyamar da kakemin, kana tunanin banajin haushi? Ko kana tunanin nid'in ba mace bace? Tunda ka auro Basira zan iya kirgama sau nawa ka kusanceni."
Ta mike tsaye tace " Baka min kara a harkar abinda kakeso, nima bazanyi kara akan zartarda abinda naga yayi daidai da zuciyata ba."
Da karfi yasa hannu ya fincikota sai gata a gabansa, idanunsa sun kada sosai da sosai yace " Kara? Ke har kinsan kalmar nan ta kara? Duk karar danake miki? Kina tunanin shakkarki ce tasa nake shanye duk laifin da kike min?"
Kallansa kawai take saidai tsoro da shakka sun d'arsu a zuciyarta dan tunda take yauce rana ta farko dataga Abdussamad cikin irin wannan b'acin rai.
Daurewa tai tace " Kadaifi kowa sanin hukuncin matar da take ba cikakiya ba a matsayin matar Sarki..."
Hannu ya d'aga kamar zai kifa mata mari wanda hakan ya tsoratar da ita sosai, sauke hannunsa yai sannan ya runtse ido cikin takaici yace " ke ba mace bace? Tayaya rashin imaninki zaisa ki taso da mikin daya riga ya warke a cikin zuciyar marainiyar Allah, Magajiya wani irin rashin tausayi da imani gareki?"
Bakinta ta d'an rufe dan magana take san yi taji yana rawa, kallansa tai bayan ta cije tace " inhar ka damu da ita ba kuma kasan mutane su san kazantar data aikata kasa d'anka ya janye auren Gimbiya sannan ya auri Mairo, sannan kayi murabus ka barwa Abdulmajid kujerarka."
"mene?" ya fad'a sannan ya d'anyi dariyar datake kunshe da tsantsan takaici yace " kinaso kicemin akan auran Bilkisu kike neman halaka rayuwar Basira?Ko kuma tsoron Turab ne yasaki b'ulo da wannan makircin?"
Kallansa tai cikin tsananin takaici tace "mene?"
Sarki yace "Ahhh yanzu na fahimta, tsoron kar Turab ya samu power ne ta b'angaren auransa yasaki haka, kina tsoron abinda zai miki inhar daga baya yaji abinda kika aikata masa."
Idanunta ne suka firfito tace "mena aikata masa?"
Sarki yace "kin dauka bansan kece silar nakashewar idanunsa ba? Ke har zakiyi maganar kara da matar so? Ko kina tunanin tsoronki ne yasa na kasa miki hukunci?"
Da sauri ta juya mai baya tace "bansan wannan zancen ba, meye nawa na nakasa mai ido?"
Sarki yace " fita."
Juyowa tai ta kalleshi tace " koma waye ya fada maka haka karya yamin sannan kace ya kawo shaida, sannan maganar aure da Murabus ina jiran amsarka inba haka ba Basira da d'anta subar gidan nan." Ta juya da sauri tai waje.
Hannunsa dake kan cinyarsa ya dunkule tamau saboda bakin ciki da takaici.
***********
Abu Turab jeka ka dawo ya shigayi a tsakar falonsa.
Da sauri naga ya fito ya yi waje.
Bangaren Basira ya nufa, lokacin tana bandaki, sai daya jira ta fito sannan ya mike yazo inda take ya tsugunna yace " Umma akwai wani laifi da Magajiya ta tab'ayi ko kuma wani Makirci da kikasan ta tab'ayi?"
Kallansa tai alamar tana nazari sannan ta girgiza kai tace "kasan halinta duk makircin da takeyi bata taba yarda tabar wata shaida da zata sa a ganeta."
Shiru yai kafin can yace " ki sake tunani Umma ko wani abu ne wanda kikasan baki yarda dashi ba sai dai bakida tabbas akanshi, abu d'aya ne zaisa muci galabarta wato yanda tasan weakness d'inmu muma musan nata."
Basira ta girgiza kai bayan dogon nazari tace "ban tuno komai ba Turab."
Mikewa yai jiki a sanyaye yace "shikenan Umma, inkin tuno ko daga bayane."
Har ya fara tafiya tace Turab.
Juyowa yai da sauri.
Tace " Akwai wani abu da take bamu kamar shayi a farkon zuwana gidan nan, to ni dayake banashan ruwan zafi na sanar da ita, sai dai abinda yaban mamaki tursasamun tai sai dana sha, sai dataga abinda nai sannan ta daina bani."
Tai ajiyar zuciya tace "nasan ba wani abun zargi bane amma na kasa cireshi a raina, sannan Turab mai zai hana ma hakura da auran Bilkisu?"
Kallanta yai yace " Umma kina tunanin saboda hana aurena ne kawai yasa tai wannan maganar? Sannan in ma haka ne kina tunanin nan gaba bazata sake amfani da wannan kalmar ta kara samu abinda tai ra'ayi ba?"
Basira tai shiru, murmushi ya kakaro yace " Na tafi."
Yana shiga d'akinsa ya rufe kofa yai shiru yana tunanin kalaman Ummansa, tabbas akwai abinda ake sawa a cikin ruwan zafin nan, to amma menene? Kalaman Jakadiya ne suka kara fad'omai, da sauri ya girgiza kai yace " inhar na tambayeta ta fad'amin gulma ina da tabbas gaskiya zata fad'amin?matar da sam bai yarda da ita ba? Sannan tayaya ma zata bi bayansa ta ajiye Magajiya?
********
A kano kuwa Bilkisu kwance a makeken gadonta ta kwantar da kanta a kan matashi ta lumshe idanunta ta shiga zazarfan tunani, tunanin da ni kaina bansan wani iri takeyi ba.
Murmushi ne d'auke a fuskarta kai kace wani albishir aka mata wanda yasa ta fara'a har a cikin bacci.
A hankali ta bud'e idanunta, da sahri ta mike tai baya tare da d'an zabura tace "Munnira meye hakan?zakizo ki sani a gaba, wlh na tsorata."
Munnira tace " Gani nai kinata murmushi shine nakesan ganin abinda ke saki murmushin."
Harara ta maka mafa tace " an kirani a waya?"
Munnira ta girgiza kai alamar a'a, baki Bilkisu ta turo tace " Lalai ma Turab ai ka kira kacemin ka isa ko wani abun." tai maganar cikin d'an kukuni.
Kallan Munnira tai rai bace tace "Fitarmin daga d'aki."
Munnira tai waje tana mamakin abinda ya samu UmmaBilkisun ta.
************
Duk wani tunani yayi amma ya rasa mafita mai karfi, cir ya kwana bai runtsa ba yana neman mafita sai dai bai samu ba.
Yanayin sallar asuba Mahaifinsa ya aika a kirashi.
Sun zauna shiru a d'akin bayan sun gaisa, Sarki ya kalleshi yace " Naji ance kazo jiya."
Kallansa yai baice komai ba, Sarki yace "naji kuma ance kace kar a fad'amin kazo."
Turab yai kasa da kansa.
Murmushi Sarki yai yace " To ya? Ka nemo mafita?"
Kallan Mai Martaba yai sannan cikin sanyin jiki ya girgiza kai alamar a'a.
Ajiyar zuciya Sarki yai yace " Murabus takeso nayi."
D'agowa Turab yai cikin tsananin mamaki yace "Murabus?"
Sarki ya murmusa yace " ya ya? Kana mamaki ne? Ko so kake kacemin bakasan Magajiya ba?"
Idanu Turab ya zaro yace " amma....."
"Hakura zakai da auran?" katseshi yai da wannan tambayar.
Kallansa Turab yai sai dai bai iya cewa komai ba.
Sarki yace " Hakura zakai saboda mahaifiyarka ko saboda ni?"
Kallansa TURAB yai yama rasa me zaice, kai ya girgiza yace "bansani ba Abba, kwakwalwata ta rufe, Magajiya ta fara sani shakkar makircinta, how can she ask u..How c...."
Dariya Sarki yai mara sauti yace " baka taba tunanin zatai haka ba?"
Abu Turab idanunsa suka ciciko yace "Abba ta yaya zaka cigaba da zama da matar da bata ganin girma da darajarka? Ta yaya zaka cigaba da zama da matar da take neman muzguna maka?"
Sarki ya kalleshi cikin wani yanayi yace "Kasan me yafi komai wuya a harkar sarauta? When u have something to protect."
Turab ya mai kallan rashin fahimta, murmushi sarki yamai yace " me kake tunanin zai faru in na rabu da ita ba tare da babban dalili ba?"
Turab yace "matarka ce fa ka kuma rabu da ita, me zai faru?"
Kai Sarki ya girgiza mai yace " Turab kenan, Magajiya zata iya sa a kwace mulki daga hannuna duk da kuwa sarautar tawa ce."
Me kake nufi?
Sarki yai murmushin yake yace " shiyasa na ke san ka auri Bilkisu wacce tasan kanta ta kuma san darajar sarauta wacce mulkin a jininta yake ba koyarsa tai ba."
Turab ya kalleshi yace " is she that powerful? Magajiya nake nufi"
Sarki ya kalleshi yace " Tasan hanyar makirci kala kala, ta kuma san manyan mutane kala kala, ta kuma san yanda zatai ta samu duk wani abu da takeso ko ta wani hali ne kuwa ko da hakan zai zama silar halakar nata ne."
Turab ya kalleshi yana kokarin magana Sarki yace " Turab kasan kai kad'aine zaka iya sa Magajiya ta amshi hukuncinta? Ni bazan taba iya cin galaba a kanta ba ko dan saboda zuri'ar dake tsakaninmu, bazan taba san d'ana ya shiga halin tashin hankali ba saboda wani buri daya ke nawa, zan kula da Basira in ta kama ma zan iya d'auketa daga gidan nan kn maidata inda ta fara zama, kada ka kuskura Magajiya tasan wani lago naka, kada ka kuskura ka bari ta nemi cin galaba akanka, na sani zaka iya, a duk lokacin dana tuna da kai inaji a raina komai zaizo da sauki da yardar Allah."
Turab duk yanda yaso ya daure sai da kwalla ta gangaro masa kad'an.
Ashe haka mahaifinsa yake zaune cikin takaici?
Jiyai Mahaifinsa yace " Kuka ba wai ana yinsa bane saboda bakin ciki, sannan dariya bawai ana yinsa bane saboda farinciki, a koda yaushe zuciya tanayin abinda tasan hankalinta zaifi kwanciya dashi ne."
Idanunsa ya runtse yai kasa dakai, mai yasa yakejin kansa yayi nauyi sosai yakeji kamar an d'auramai wani babban nauyi na kare mahaifansa da kuma duk wani abinda yake so?
"Idanunka itace silar lahantasu, banso sanar dakai ba sai dai a yanzu na fahimci dolene na fada maka, ni dakai dolene mu had'u dan ganin mun kawar da masifar dake nanad'e damu, bazan taba bari Abdulmajid ya gajeni ba dan kamar naba Magajiya kujerata hakan zai kasance, ita kuma nasan bazata taba bari na baka kujerata ba."
Turab ya daure kansa na kasa ya d'ago ya jinjina kai yace " Na fahimci me kake nufi, sannan ni kaina na dade da zargin itace silar matsalar idona sai dai ganin ba wanda ya taba zancen ba kuma wanda ya nuna yasa ban taba maganar ba."
Sarki ya mai murmushin tausayawa yace " Kayi hakuri Turab da samun Mahaifin da bashida karfin hukunta wad'anda suke da laifi."
Turab ya girgiza kai yace "Ba haka bane Abba, a koda yaushe ina alfaharin kasancewarka uba a gareni."
*ABU TURAB TEAM*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*55*
Turab na fitowa daga b'angaren sarki ya hau tafiya, Garzali ya biyoshi da sauri yace "Ranka ya dade ina zamu?"
Juyowa yai ya kalli Garzali yace " akwai makullin mota a hannunka?"
Kai ya girgiza alamar a'a.
Turab yace "d'an hanzarta ka d'auko fita nakesan yi." Garzali ya juya da sauri.
Turab ya shafi fuskarsa zuwa kansa sam jiyake gidan ya mai zafi, duk hirman masarautar jiyai kamar a takure yake.
Inama ya iya mota? Da dakansa zai d'auka yai waje, sai dai matsalar idanunsa yasa bai tab'a koya ba gudun kar asiri ya tuno.
Bai dade ba sosai sai ga Garzali nan ya bud'emai gidan baya ya shiga shikuma ya shiga gaba sukai waje.
Tafiya kawai sukeyi, ganin baice komai ba yasa Garzali yace "ina zamuyi Ranka ya dade?"
Turab yana kallan window yace " ka cigaba da tafiya kawai, ni kaina bansan inda zamu ba."
Jin haka yasa Garzali ya cigaba da jan mota.
Komar da kansa yai jikin kujera ya rufe idanunsa kamar maiyin bacci.
Sai da sukai tafiyar a kalla awa d'aya sannan yace mu juya.
Nan Garzali ya juya da kan mota, kasancewar safe ne dan lokacin karfe 10 ne na safe, gashi lokacin damuna ne yasa garin yai luf abin sha'awa ba kuma rana.
Sai da suka shiga garin Zariya sannan ya kalli Garzali yace " kasan gidan Barde?"
Garzali ya murmusa sannan yace "eh."
Turab ya d'anyi karamin tsaki yace "Garzali a idanuna dana mutane ina ganin kamar