Showing 78001 words to 81000 words out of 146065 words

Chapter 27 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

gaisheta.
Kai ta d'aga mata, Basira tai murmushi tace " yau kam naga jikin da sauki."


Basira gani tai ta miko mata hannu alamar ta riketa.
Nan ta riketa tace " Hajiya."


Kokarin magana takeyi sai dai ta kasa da alama akwai abinda takesan fad'a.


Kunnenta ta matso dashi tace " Hajiya menene? Akwai abinda kike so ne?"


Ma ma ma ga.......
Basira tace " maga me?"
Hajiya ta kara daurewa tace " Abbbbb......"
Da sauri wannan yarinyar ta shigo tace " Hajiya a kawo miki ruwa?"


Yunkuri takeyi da alama akwai abinda takesan ta fad'a.
Basira ganin yanda taketa keta zufa tace " Hajiya ki barshi sanda kika ji dama in har abun daya kamata ne sai ki fad'amin."
Idanu ta runtse na takaicin kasa magana da take, gashi dama ko zama bata iyayi.


Sun dade kafin su fito, Hajiya tai shiru tana tunanin abinda ya faru shekaru hud'u da suka wuce.


Taya zatai ta sanar da d'anta abinda ke faruwa? Tundaga ranar da ta mata magana akan abin a ranar ta fara rashin lafiya wanda har yau ciwo sai gaba yake baya raguwa.
Kowa ya d'auka tsufa ce ta sata wannan rashin lafiyar sai dai ita tasan ba haka bane.




B'angaren Magajiya suka nufa.
Bayan ta zauna a kilisarta ne, aka shiga ciki dan sanar da Magajiya zuwan Basira.


Ta dade dan takai akalla minti 20 kafin ta fito.


Tafiyarta take cikin takama, tazo ta zauna cikin isa sannan ta kalli Basira a wulakance.
Basira ta gaisheta sannan tace " Zuwa nai muyi wata magana."


Magajiya ta kalleta tace " inajinki, sannan inaso ki hanzarta saboda inada abinyi."


Basira tai shiru tana tunani kafin tace " Me kike tunani game da auran Abdulmajid da Mairo?"


Magajiya ta zuba mata ido sai dai batace komai ba.
Basira tacigaba " Zuwa nai inji ra'ayinki akan auran......."
" nikam a iya sanin kwakwalwata ban ji ance kin sake haihuwa ba, ko ince banji ance kina d'auke da cikin wata yarinya Mairo ba, dan haka banaji kina da hakki akan auranta."


Basira ta d'ago cikin mamaki tace " ai ba sai ka haifi mutum ba kake da hakki akansa ba Ranki ya dade."


Magajiya tai wani banzan murmushi tace " ko? To in haka ne nima bari nai iko da Abu Turab wanda ban haifa ba, inaso kice ya dawo daga garin kano sannan ya janye auren Bilkisu ya auri Mairo wacce kike so."


Tsananin mamaki ya hana Basira yin magana, ta kalleta tace " ban gane......"
"Kurma ce ke? Ko kuwa fahimtace baki dashi?" Sai kuma tai wani lalausan murmushi tace " ko dayake wacce akai rufa rufa agun auranta saboda rashin matsayinta da abinda ta aikata a baya banaji tanada inda zatai tunani a kwakwalwarta."


Gaban Basira ne ya fad'i tama rasa me zatace.
" kin kyauta da kika zo, dama ko bakizo ba zan aika kizo, inhar kinaso in rufe sirrin da aka fad'amin ki tabbatar kin sa d'anki ya janye auran Bilkisu dan d'an sarki sai 'yar sarki, Abdulmajid zai auri Bilkisu shikuma d'anki Turab ya auri Mairo kinga in akai hakan komai yazo da sauki kenan, kema kinsamu abinda kikeso kamar ni."


Basira tai dauriya tace " me kikaji akaina? Banaji inada wani abu da zan......"
"Hmmm kin manta ba'a cikakiya aka aureki ba?"


Tashin hankali ne karara ya bayyana a idanun Basira, ta daure tace " ban....."


Wata irin dariya Magajiya ta saki ta kalleta tace " Basira sunana Magajiya."


Basira tai shiru sai jikinta dake tsuma.
Magajiya ta mike ta zo inda take ta tsugunna tare da dafata tace " Me yasa banyi tunanin komai ba da? Sai dai karki damu sirrinki zan tayaki ajiyewa in har kika sa d'anki ya janye maganar auran Gimbiya, dan ko za'a mutu bazan taba bari ya aureta ba."


Ta karkad'e mata kafada tai gaba.


Magajiya tana shiga d'aki tai wani mugun murmushi tace " lalai da gaske ne."
Tunowa tai jiya bayan ta rasa mafita kawai ta kira Hisham tace ya kira abokinsa dake garin Daura, yasa yamai bincike akan Basira, ba shakka sai yanzu ta fara tunanin tabbas haka kawai sarki bazai auri Basira a b'oyeba, duk da batai tunanin wannan matsalar ba tadai san akwai wani abun.








Basira kam da kyar ta mike jikinta na rawa ta fito.








🤝🏻 *ABU TURAB TEAM*
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


_AyI hakuri da Jina shiru da kukai kwana biyu, azumi nakeyi_🙈




*52*




Abu Turab dama ya sanar da Fulani zancen tafiyarsa, nan sukai sallama da mai martaba cikin jin dadi dan bai tambayeshi dalilin tafiyarsa ba.


Sai da suka gama shiryawa tsaf sannan ya nemi ganin Bilkisu dan yin sallama.


Itakam Bilkisu tunda Munnira ta sanar da ita take tsaye tana zagaye d'akin, meke faruwa? abinda ke mata yawo kenan har mai kula da ita ta sanar da ita neman da Turab yake mata.


Cikin sauri ta duba fuskarta a jikin madubi sannan ta nemi fita, harta kai kofa sai kuma ta tsaya, taja wani dogon numfashi sannan ta kara neman nutsuwarta kafin ta fito.


Yana zaune yayi shiru ta shigo da sallama, dagowa yai tare da amsawa yana kallanta.


Sai data zauna sannan ta gaisheshi tare da cewa " Lafiya dai ko?" kallanta yai yace " nikaina abinda nake san sani kenan."
Kallan mamaki tamai sannan ta d'ora da cewa " badai wani abu mara kyau bane ya faru ko?"


Hannunsa ya sa yad'an shafi saman goshinsa sannan yace " Ina ji nane ba dadi, inajin kamar da wata babbar matsala datake faruwa a gida."


Kallansa tai sannan ta d'anyi murmushi tace " Insha Allah ba abinda ya faru sai alkairi, sannan in har wani abu mara kyau ya faru ko ka fuskanci kana cikin tsaka mai wuya ina rokonka da karka yanke hukuncin da nan gaba zakai dana sani, ka jinkirta yanke hukunci har sai zuciyarka ta aminta da wannan hukuncin."


Murmushi ya sakar mata yace " Nagode."


Itama murmushi tamai sannan ta sunkuyar da kanta kasa.


Mikewa yai yace " zan wuce."
D'agowa tai ta kuramai ido sai dai batace komai ba, a hankali ya tako zuwa inda take sannan ya tsuguna a gabanta tare da zaro abu a aljihu, ya nuna mata takardar databa Munnira na layin waya, yana murmushi yace " na gani na kuma gode."


Kallansa tai sannan ta saki wani lalausan murmushi.
Mikewa yai yace " kafin in dawo maybe an tsaida rana."


Da sauri ta maida kanta kasa, wata yar karamar dariya yai wacce batada sauti yace " wannan d'in kunya ce?"
D'agowa tai ta harareshi tace " dama haka ake yi? da kanka ya kamata ka fad'amin zancen?"


Dariya ya sakeyi yace "au haka ne? to goge abinda na fad'a a zuciyarki inyaso sai a sake sabon la le."


Murmushi tamai tare da juya kanta gefe tace " na goge." cikin zolaya yace " nikam me ma nace?"


Hararar sa ta sakeyi sannan ta maida kanta kasa tana murmushi, ashe yanada side na zolaya, farkon ganinsa ta d'auka mutum ne wanda bayasan wasa sam, sai dai yanzu ta fara tunanin tsauri da jinin mulki ne ya sashi haka.


Dagowa tai ta kalleshi sai dai batace komai ba.
Murmushi ya mata sannan yace " zan kira." kai ta d'agamai, yace " zan wuce" nan ma kai ta d'agamai.
Lab'ansa ya d'an hade sannan yace " nagode."


Murmushi tamai, nan ya juya yai hanayar fita.
Sai dayaje kofa yaji muryarta a hankali tace " Allah ya kiyaye hanya."
Juyowa yai yana murmushi yace " Ameen."
Nan ya juya ya fita, yana zuwa ya tadda Sabi'u ya sa an fita da komai, nan suka kama hanyar gida.




Basira kam abin duniya duk ya gama damunta tama rasa ina zata saka kanta, da farko tayi tunanin fad'ama Sarki sai dai tace me? wad'annan tunanin sun hanata sakat, fatanta kawai d'anta ya dawo, ta sanar dashi hukuncin magajiya.


Magajiya kam tana zaune a kilisarta tana kurb'an shayi wanda yaji kayan kamshi, tana sha tana lumshe ido, kana ganinga kaga wacce take cikin nishad'i da jin dadi.


**********




Da rana su Abu Turab iso, Sabi'u yana ajiyeshi ya sauka daga motar yace " ni nayi gida mutumina."
Turab kai kawai ya d'aga mai, fadawa ne suka taho da sauri suka shiga kwashe kaya.


Kallansu yai yace"ku kai kayan b'angaren Umma ni zan shiga fada na gaida Sarki." nan suka amsa da to, shi kuma yai gaba.


Bayan ya shiga fada ne ya kwashi gaisuwa, Sarki cikin mamaki yace " me ya dawo dakai yau? bayan sai gobe kace?"
Shiru yai na wasu dakiku kafin ya d'an sosa keya yace " zuwa nai na sanar da Sarkin Kano mahaifin Gimbiya yace ya na jiran lokacin sa rana." ya karasa maganar tare da maida kansa kasa.


Galadima yace " Alhamdulila abu yayi kyau, nikam Takawa mai zai hana ka had'a auran yarima Abdulmajid da na Yarima Turab kawai ayi a rana d'aya?ko har yanzu ba'a tsaida maganar ba?"


D'agowa Turab yai cikin mamaki sannan ya kalli Galadima, cikin neman karin bayani yace " Abdulmajid ya samu mata ne?"


Galadima yana murmushi ya kalli Barde wanda yai shiru kamar wanda aka daka haka yake jinsa, sannan ya kalli Wambai yace " au ashe fa bakanan? ai 'yar gidan Barde yakeso yama sunan ta?"


Wambai yace " Mairo."




Idanu Turab ya zaro cikin tsananin mamaki yace " Mairo? ya fad'a yana kallan Barde, sannan ya kalli Hisham wanda shima yaci magani."


Murmushi ya kakaro sannan yace " Bari na shiga ciki Ranka ya dade."


Sarki wanda shima ya rasa ta cewa yace " Ya kamata kam, kaje ka huta."


Turab ya kara gaidasu sanan yai waje.


Cikin hanzari yake tafiya Mairo? lalai ma yaran nan ba karamin mahaukaci bane, an tab'a aure dole?


Hangoshi yai a gabansa kamar irin yasan maganarsa d'in nan yakeyi.


Tsayawa Turab yai ya kafeshi da ido, shima Abdulmajid wanda ke hanyar Fada dan jin hukuncin da aka yanke ya tsaya tare da kafe Turab shima da ido.


Cikin kasaita kowannen su ya fara takowa, idanunsu na kallan juna har zukazo daf da juna.
Abdulmajid ya kalleshi yace " Sirikin sarkin kano ka iso?"


Wani murmushi na gefe Turab ya saki yace " Sai ina?" Abdulmajid ya tab'e baki sannan yace " ya zanyi? kasan na kusa zama ango dole ba zama."


Turab baisan sanda yai wani banzan murmushi ba har hakwaransa suka fito ba yace " Ango? Are u kidding me?"


Abdulmajid ya had'e rai sannan ya kara takowa jikin Turab daf yace " Kana tunanin zaka hanani? to ka bud'e kunnuwanka da kyau kajini, yanzu ba lokacin damuwa da abinda bai shafeka bane na aurena da matata Mairo ba kaje ka duba lafiyar tsohuwarka dan naji Umma tace ta saita komai akanta" sannan ya murmusa yace " ka kuma san Umma in tace abu to da abun ne."


Sosai Turab ya harzuka da kalamansa, ya juyo ya kalleshi sannan ya sa hannu ya kade mai kafadarsa kamar irin abu ya hau kai d'in nan yace " Ya za'ayi? dan nasan in Magajiya tace abu tofa abun ne sai dai ni kuma in nace abun nan ya isa to fa dolene ya dakata."
Ya karasa hannu ya kad'emai d'aya bangaren yace " Ka tabbatar ka sanarwa Ummanmu kalamai na sannan auran Mairo?" yai dariya yace " ko a mafarki kama daina dan baka isa kasa baiwar Allah cikin kunci da bakin cikin auranka ba." ya juya yai gaba ransa a b'ace, da alama an ma Ummansa wani abun, Idanu ya d'an rufe kad'an yashiga fad'in _Innalilahi Wa Ina Ilaihi Raji'un_












**********
Har yaje sai shiga bangaren Umma sai kuma ya fasa yai b'angaren Magajiya.


Batai mamaki ba sam da aka sanar mata da zuwansa dan dama tasan in har ya iso to da dole ta ganshi.


Kara gyara fuskarta tai ta kalli wacce ta sanar da ita zuwan nasa tace " Muna bukatar abu mai sanyi."
Nan ta amsa da to sannan ta juya.


Magajiya ta zura takalminta mai kyau sannan ta kalli kanta a madubi kawai sai gani nai tayi wani murmushi, sannan tad'an cije lab'anta ta kara murmusawa.


A hankali ta tako cikin izarta ta iso kilisarta.


Abu Turab na zaune ya had'e hannayensa guri d'aya.


shigowa tai cikin takama ta zauna, sannan ta kalleshi tace " Bakaga shigowar mahaifiyarka bane?"


Kallanta yai sannan ya d'aga gira yace " Au banji shigowarki ba, sannan yai kasa dakai ya gaidata."
"Me ya kawo ka?"


Kallanta yai yace " zuwa nai na gaidake na kuma sanar dake abubuwa biyu a matsayinki na Uwata."


Kallansa tai batace komai ba.
Yace " Sarkin kano yace yana jira daga bangaren mu, na tabbata kin san me yake nufi, sannan abu na biyu ki fadama d'anki ya janye auren......"


Wata dariya ta saka sannan tace " Turab? da alama bakaje ka gaida wacce ta haifeka ba ko?"


Kallanta yai cikin shakka yace " Na'am?"


Dariya ta kara sawa tace " me yasa ne nikam na girma amma haryanzu nakejina kamar yarinya? fatata bata canza ba sam."
Ta karasa maganar tana kallan hannunta, kallanta yai cikin tashin hankali idanunsa suka kada sosai, yace " me kikana Umma na?"
Baiwar nan ce ta shigo d'auke da tire da jug da kofuna ta ajiye sannan ta zubama Turab ta kuma zuba ma Magajiya.
Magajiya ta amsa sannan ta kurba tace " sha akwai sanyi dan ka d'auko rana."


Kallanta yai sannan ya kalli kofin, yarinyar ta fita.
yace " me kikama Ummana?"


Yai maganar cikin kakkausar murya.


Kara kub'a tai sannan tace " ta yaya zan sani?"


A harzuke ya mike yai waje cikin tashin hankali.
Me tama Umma haka? da yake ganin tsantsar confidence a idanunta???








🤝🏻 *TEAM TURAB*
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*








*53*


Har ya murd'a kofa sai yaji tace " Ahh na manta ashe akwai wacce kake so?"
Tsayawa yai cak sai dai a hankali ya juyo zuwa kallanta.
Murmushi ta saki tace " Hmm na kula da gaske ne, dama Khadija ce ta sanar dani akwai wacce kake so, nayi mamaki da naji haka da alama san mulki ne yasa ka ture wacce kakeso zuwa auran Gimbiya."


Idanunsa ne suka kad'a sosai Khadija?
Da karfi ya bud'e kofar ya fita cikin b'acin rai.


Magajiya ta bishi da harara tace " Mairon yakeso da gaske? Ko kuma akwai wata a kasa? Dama hakan ne yasa batace Mairo ba kai tsaye saboda tanaso taga yanda zaiyi, sai dai ta kasa ganewa."


Abu Turab tsaya wa yai a waje yai shiru, wata zazzafar iska ya fitar daha bakinsa yana kokarin juyawa ya ga Khadija ta taho.


Kallanta yai sau d'aya ya d'auke kansa, kalaman Magajiya ya maimaita na game da wacce yakeso, kenan kila na Khadijan har fada musu tai ita yake so? Wato gaba gaba amfani zasuyi da san da yake mata su cutar dashi? A da yana tunanin Khadija bazata tab'a cin amanarsa ba amma a yanzu ya cire wannan abun a ransa, bai san ta iso inda yake ba.
Sai jiyai cikin muryar tausayi tace "Yaya."


Kallanta yai fuskarnan tasa a d'aure tamau, ta d'auka jin abinda ya faru ne yasa shi cikin wannan hali, a hankali tace " Yaya kayi hak........"


Katseta yai da cewa " Alhamdulila banaji a yanzu zanyi kokwanto akan hukuncin da zuciyata zata yankemin, a da ina tunanin halin da zan sakaki, nagode kwarai da kika nunamin ke jinin Magajiya ce."


Yana kaiwa nan ya wuceta.
Sam ta kasa ma magana saboda ta kasa fahimtar abinda yake fad'a.
Ita datazo dan yima Abdulmajid magana da kara bashi baki akan ya janye maganar nan, me Turab yake nufi?


***********


B'angaren Mahaifiyarsa ya nufa, a zaune ya ganta ganin yanayin datake yasa yaji idanunsa sun ciciko, shiga yai ciki ya zauna sannan ya gaisheta.


Fuskarta d'auke da murmushin data kakaro tace "Turab akacemin ka dawo, nayi mamaki sosai ganin ba yau ne kace zaka dawo ba."


Mikewa yai jiki a sanyaye ya karaso inda take a hankali ya kwantar da kansa a kan gwiwarta idanunsa sun ciciko yace " Ba sai kin b'oye damuwarki ba a gabana Umma, na sani akwai babban matsala data kunno miki kai, ki sanar dani Umma ko na nemanr mana mafita."


Jitai hawaye na neman zubo mata da sauri ta mike tsaye ta juya mai baya tace " Ba komai Turab kawai dai jiya na d'anyi zazzab'ine shi yasa ka ganni haka."


Mikewa yai shima ya kalleta sannan yace " Me Magajiya take nufi da inzo ki sanar dani?"
Basira ta juyo tace " Haka tace ma?"
Kai ya d'aga alamar eh sannan tace "Maganar Abdulmajid ne da Mairo bayanshi banaji akwai wani abu."


Kallanta yai sai dai bai gamsu ba ya dai fahimci batasan yasan ko menene.
Juyawa yai yace "bari na koma ita ta sanar dani."
Cikin tsawa tace " Turab dakata."
Juyowa yai ya kalleta cikin yanayi na tausaywa yace " Umma kin manta wahalar da mukasha a rayuwa ni da ke? Kin manta matsala da tashin hankalin da kika fuskanta? Ta yaya zakiso ki b'oyemin wani abu?"


Idanu ta runste tace "Turab muna cikin tashin hankali, in har abinda Magajiya ta sani ya bayyana banaji zamu kara samun kwanciyar hankali a gidan nan."


Cikin shakkun kalamanta yace "Umma badai tasan maganar lahanin da aka miki ba?"


Kallansa tai hawayen dataketa dannewa suka zubo tace "Turab ya zamuyi? In har maganar nan ta fito ban san yanda mutane zasu kallemu ba, ba kuma naji za'a yadda da kai."




Idanunsa ne suka kad'a sosai lalai Magajiya bala'i ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login