Showing 42001 words to 45000 words out of 146065 words

Chapter 15 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

Magajiya shi Mahaifiyar Abu Turab tai amfani gun aika mai da kaya dan gudun kar a gane itace."


To fa? Nan kowa yad'an fara magana kasa kasa.
Abdulmajid ya kalleshi yace " sanar damu abinda ka sani."
Muryarsa na rawa alamar tsoro da dana sani yace " tuba nake ranka ya dade amma abinda Yarima mai jiran gado ya fada haka yake, ranar nazo wucewa Baiwarta wato Lantana ta mikon kaya tace " dan Allah sauri nake dan mikama Abu Turab, basai ka shiga ba kawai ka bada a kofar shiga ka wuce."
Salati mutane suka fara dayawa sun gamsu dan sunsan ba yanda za'ai bawa yazo gaban mai martaba ya gilla karya haka.


Abu Turab yai murmushi sannan yace " Ammm ina Mai bada shaidar nan?"
Bawan yace ganinan Yarima."
Abu Turab yace " ka tabbata duk abinda ka fada gaskiya ne?"
Yace " hakan yake Ranka ya dade, ina ni ina karya gaban Takawa."


Abu Turab yace " haka ne, sai dai nima ina rokon a bani dama namai tambaya."
Mai Martaba yace " inajinka."


Abu Turab yace " inaso ka bani amsar tambaya ta cikin sauri ba tare da kaja min lokaci ba, inaso daga na tambayeka ka sanar dani amsa."
Kai ya daga.
Abu Turab yace " A ina kuka had'u?"
"Gaban Turakar Magajiya."
"Hmm kenan can ta bika saboda tana san ta aikeka?"
Muryarsa ce tadan sarke yace " banida masaniya akan wannan."
Yace " me yasa daka kawo kayan baka ce inji Lantana ba bayan a iya sanina wanda ya kawo kayan ance ya sanar da wanda ya aikosho?"
Inin na ya fara cikin tsoro yace " hmm hmm nima sauri nake hmm shi yasa....."


Abu Turab ya karseshi da cewa " ok na gane, saurin da kakeyi ne ya hanaka sanarwa ko?"
Da sauri yace haka ne.
Abu Turab yace " kenan bayi nane sukai karya tunda sun sanar dani an fada musu wanda ya aiko da kayan?"


Bawan yai shiru, Abu Turab yace " na fahimceka, yanzu tambaya d'aya zan maka, dakai da Lantana wanene yafi wani matsayi a gidan nan?"
Cikin rashin fahimtar zancensa yace " na fita."
Abu Turab yace " Good! Ka fita matsayi meya saka ka yarda ta aikeka?"


Gaban Bawan ne ya fadi ya fara inda inda "hmm dama...."
Katseshi Abu Turab yai yace " dama me?"
Shiru yai dan ya rasa bakin magana, Abu Turab yace " bari na aika a kira Lantana da alama kunada wata ala'aka da ita wanda ba wanda ya sani, dan hakan ne kadai zai sa mu fahimci dalilinka na zuwa aikenta."


Hankalinsa ne ya tashi da sauri yace " wlh ba haka bane ni banma taba magana da ita ba, ina dai gani suna zuwa gun Magajiya amma wlh ko sau d'aya bamu taba magana da ita ba....."


Shiru yai jin ya kauce hanya a zancen sa.
Abu Turab yace " to fa yanzu wace maganar zamu yadda da ita?"
Galadima a harzuke yace " wannan shaidar bamu yarda da ita ba dan ta nuna itadin bakin ganga ce."


Idanu Abdulmajid ya runtse dan bakin ciki.
Wani mugun kallo ya bugama Abu Turab, nan mutane suka fara kananan maganganu, lalai dama ance makaho yanada tasa baiwar da alama Abu Turab akwai kwakwalwa, ganin ne dai da Allah ya d'auke mai.


Kallansa Mai Martaba yai cikin jin dadi, Abdulmajid yace " inada wata shaidar."
Mai Martaba yace " muna jinka."
Wanda ya kawoma Abu Turab doki ne ya shigo, bayan yayi gaisuwa Abdulmajid ya kalleshi yace " sanar damu abinda ya faru."


Nan yace shidai an aikeshi ne yakai doki bangaren Abu Turab.
Abu Turab ne ya katse Abdulmajid wanda ke shirin magana yace " tabbas muryarka ce naji a lokacin, sai dai tunda ba gani nake ba bazan san kaidin bawan wanene ba."
Kansa na kasa yace " bawan Magajiya ne."
Murmushi Abu Turab yai yace " kenan duk bayin Magajiya ta nemo?"


Abdulmajid ya bugamai kallo baice komai ba, Abu Turab yace " amma ni mai ka sanar dani a lokacin? Wa kacemin ya aiko ka?"


D'agowa yai yad'an kalli Abu Turab, gabansa ne ya fadi, duk da yasan baya gani amma baisan me yasa ba sai yaga kamar yana kallansa, kwarjini Turab yamai dama gashi duk cikinshi ya gama rud'ewa a waje dan kuwa yaji duk abinda ya faru da d'aya bawan.


Shiru yai baice komai ba, Barde yace " zancen banza kenan, tayaya ana tambayarsa ya kasa bada amsa."




Mai Martaba ne yai gyaran murya yace " Kana da wata shaidar? Dan wannan shaidar naga farar kura ce."


Abdulmajid kasa yai dakai a hankali yace " tuba nake ranka ya dade banida wata."


Mai Martaba ya kalli Abu Turab yace " kaifa? Kanada ta cewa?"


Abu Turab yace " ina neman alfarma akan mai martaba ya yafema wanda ya aikata wannan laifin gudun samun babbar matsala garin bincike, dan na tabbata duk wanda ya aikata hakan tabbas bazai yarda a gane shi bane."
Mai Martaba yace " zanyi tunani, amma wad'an nan bayin da sukai shaidar karya inaso a kullemin su."




Da wannan fada ta tashi, kowa yana yaba kwazon Abu Turab.
Hisham kam da Abdulmajid a cike suka isa gun Magajiya, bayan taji komai ta kalli Abdulmajid bai yi auni ba yaji ta wanka mai mari.


Tashin hankali, d'agowa yai cikin tashin hankali dan tunda aka haifeshi ba'a taba dukansa ba sai yau, Magajiya ta kalleshi tace " wannan shine shirmanka na cewa in barma zaka d'au mataki da kanka? Wannan shine abinda kwakwalwarka kawai zata iya karantama?"


Hisham wanda yaji dukan kamar a fuskarsa ya daure yace " kiyi hakuri Magajiya."


Kallan Abdulmajid tai tace " ku bani guri."


Nan suka mike jiki a sanyaye, Hisham na fita yai 'yar karamar kwafa a ransa yace " wlh wannan marin bashinshi kika co kikira d'ana ya hau mulki zakisan kin mareshi."




**********


Bayan sati d'aya.


Abu Turab zaune a gun mahaifiyarsa yanacin abinci sai dai zuciyarsa nata tunanin tun randa yaga khadija bai sake ganinta ba har yau, ko dai ta koma inda ta tafi da ne?


Yana neman amsar tambayarsa yaji sallamar Mairo.
Amsawa yai va tareda ya juyo ba.
Gefensa ta karasa ta gaisheshi sannan tace " Yaya ina Umma?"
Yace "Mairo tana ciki, kwana biyu?"
Murmushi tai tace " na da'uka ko daina zuwa nai bazaka nemanba bare ka tambayen dalili."


Juyowa yai yace " tanan kika b'ulo?"
Tace "Ba haka bane yaya gaskiya ce ai na fada."
Yace " hmm, ina saurayin naki? Ki fada mai fa in har yanasan in ba da ke sai yazo ya kwashi gaisuws."
Fuska ta had'e tace "ni bansanshi ba."


Murmushi ne ya bayyana a fuskarsa wanda har hakwaransa suka fito, daidai nan Basira ta fito, kallansa tai cikin jin dadi tana ganin yanda yake tsokanar Mairo, kana ganinsu kasan suna cikin farin ciki, lalai dolene ta tilastamai auren Mairo.


Yana gama cin abinci yanashan ruwa Garzali ya sanar dashi nemansa da Sabi'u yake.


Mikewa yai ya sa hannu zai dauki sandarsa, da sauri Mairo ta d'auke sandar ta b'oye tana dariya.
Yace " Mairo nasan kece, mikomin in fita, in kuma baki ban ba zan fita a haka duk abinda ya samen kece."


Da sauri ta mikomai tace " yahkuri yaya."
Amsa yai ya fita baice komai ba.
Kallo ta bishi dashi tanajin wani abu na ratsa ta.


*********
A waje yaga Sabi'u yiyai kamar zai wuceshi, Sabi'u yace " ganinan mutumina."
Ya karasa maganar tare da dafashi.
Abu Turab yace " Badai aiko ka akai ba ko?"
Yace " Mai Martaba ne yace inzo dakai."
Fuskarsa a hade yace " dama nasan bazaka kazo dan radin kanka ba."


Sabi'u yace " Abu turab kaikasan dalilina, kana gani yanda nake sha fada agun Mahaifina na bayasan in ware ga wanda nakeso saboda gudun nan gaba."


Abu Turab yai murmushi yace " da gaskiyarsa, tunda yasan Abdulmajid ne next emperor kaga kuwa yana tsoron kar Abdulmajid ya hukuntaka na shakuwa dani."


Sabi'u yai tsaki yace " in kuma kaine fa?"
Tsaki Abu Turab yai yace " zaka fara ko?"


Sabi'u yace "Allah sau dubu kafi Abdulmajid matsalar ido ce kadai kuma......."
Abu Turab ya katseshi yace " muje dan Allah."



*********
Sun isa gun hutawar Mai Martaba inda yake zaune rike da wasu takardu yana dubawa, bayan sun gaisheshi ne Mai Martaba ya kalli sabi'u hakan yasa ya mike yai baya dasu.


Shiru ne ya biyo baya kafin Mai martaba ya kalli Turab yace " Abu Turab!"


Yanda ya kira sunansa ne yasa Abu turab kallan mahaifin nasa.
Cigaba yai da cewa "Inaso gobe Asabar dakai da Sabi'u ku ziyarci masarautar Kano."


Kallansa yai cikin mamaki, sai dai baice komai ba.
Mai Martaba yace " Zakuje Masarautar ne da nufin ziyara sai dai inaso ka samu keb'ewa da Bilkisu 'yar Sarkin garin."


Cikin mamaki yace " ban gane ba Abba."
Mai Martaba yace " Inaso duk yanda zakai kayi dumin sace zuciyarta."
Mamaki ne yasa Abu Turab ya kasa magana.
Mai Martaba yace " Umarnine na baka ba shawara ba, inaso ka kwana a garin kamar kwana biyu, a wannan lokacin ka tabbatar Bilkisu ta aminta dakai."


Kansa na kasa yace " bazan tambayi dalili ba dan nasan ba kirana kai a matsayi uba ba, ka kira ni ne a matsayin Sarki, zanyi abinda kace sai dai inada tambaya, a makaho xan je mata?"


Sarki yace " wannan na bar maka hukuncin domin ni Sarki ne wanda baisan d'ansa yana gani ba."


Nagode, kawai abinda yace kenan ya mike.
Suna fita daga gun ya tsaya cak, jiyake kamar zuciyarsa zata fashe.
Sabi'u ka dafashi yace "me yasa baka musa mai ba?"


Yace " ta ina zan musamai bayan Umarnin Sarki ne bana uba ba?"


Sabi'u ya kalleshi cikin tausayi yace " amma nifa hadin auren ya birgeni, Bilkisu itakadai ce gun Sarkin kano aurenka da ita zai karama matsayi da kuma daraja agun mutane."


Abu Turab murmusawa kawai yai baice komai ba, Sabi'u ya kalleshi yace "yanzu ya zakai?"
Juyowa yai saitinsa yace " Sabi'u nasan bazan samu abinda zuciya ta takeso ba dan haka banga wani damuwa ba akan auren wata, ban dauki auren nan wani abun ba banda biyayya da kuma raba gado da wata ba."


Dariya ce ta kama Sabi'u yace " raba gado?lalai Turab bakada kyau, taya zaka dauki auren 'yar sarki akan raba gado?"
Tsaki yad'an ja yace " to fadamim, soyayya ce?aminta ce?yan uwan taka ce? Ko kuwa shakuwa ce?"

Dariya Sabi'u ya sakeyi baice komai ba.


********


Acan gidan Waziri kuwa Hisham kuwa tunda Khadija ta dawo zazzabi ya rufe ta yau sati d'aya kenan tana fama da zazzabi da ciwon kai.




Wannan kenan


*ABU TURAB TEAM 🤝🏻*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*28*


B'angaren Mahaifiyarsa ya nufa, tana zaune gefenta kuma Lantana ce, daga bayanta kuma a tsaye Mairo ce take mata kitso, jiki a sanyaye yai sallama.
Dukansu suka amsa nan ya karasa ya zauna a kasa tare da lankwashe kafafunsa.
Basira ta kalleshi sai dai batace komai ba, d'agowa yai yace " Umma gobe zani Kano."
Gabanta ne ya fadi dan kuwa tasan me zaije yi kanon.
Sam ta manta da Mairo dan kuwa hankalinta ya tashi, ta kalleshi tace " ka amince da ganin yarinyar ne ko kuwa har auren?"


Idanu Mairo ta zaro cikin tsananin tashin hankali, kallan Abu Turab kawai tayi, shima jin kalaman Basira yasa ya d'ago ya kalli Mairo.
Ganin yanda idanunta sukai yasa ya kalli Basira kansa na kasa yace "Mairo bamu guri."


Jin haka yasa Basira ta juyo da sauri ta kalleta, ganin yanda kwallq ta ciciko mata yasa tace " Lantana shiga da ita d'aki
"
Mikewa Lantana tai ta ja ta ciki, suna shiga ta zube a kasa tare da hade kanta da gwiwarta, ba kuka take ba sai dai yanda takeji a ranta tabbas taso ace ma kukan takeyi.


Tana iya jiyo muryar Basira sama sama tana cewa " Abu Turab nifa wannan hadin auren bai kwantamin ba, nafisan ka auri Mairo ko dan samun nutsuwarka da kuma kwanciyar hankalinka."
Dan murmusawa yai yace " Umma kinaso ne na karya umarnin Sarki ko me? Abba ya kiranine a matsayin Sarki bawai a matsayin Uba ba, sannan maganar Mairo nicewa tai tana sona ko kuwa nice nace ina santa?"
Shikam yasan tana sansa sai dai yayi hakan ne dan sa Umma ta saduda, ya cigaba da cewa " itama ta kanon xan dai jene kawai inbi Umarnin da aka bani amma tana 'yar sarki guda d'aya tilo mai zatai dani? Makaho?"
Basira cikin bacin rai tace " Da farko amsarka xan ba, na tabbata kai kanka kasan Mairo tana sanka, sannan kaima nasan haka, sannan na biyu shi mai martaba cewa yai kaje a Makaho?"


Gaban Mairo ne ya fadi, Lantana jin haka ta taso fa sauri daga inda take a d'akin tace " tashi ki shiga can ciki."
Mairo ta kalleta tama kasa magana mikewa tai a hankali ganin yanda ta tsaya kamar me shirin faduwa yasa Lantana ta riketa, ji sukai Abu Turab yace " yace inje a duk yanda naso, nima haryanzu ban tantance a me zanje mata ba."
Jitai kanta yayi wani irin sarawa, cikin rawar murya ta kalli Lantana tace " meke faruwa?"

Lantana ta kamata suka fara tafiya, sai data kaita canciki sannan ta kalleta tace " ba abinda ya faru nikaina bansan me suke nufi ba."


Mairo ta kalleta tace " amma dai ba kina nufin in yarda da kalamanki ba ko?"
A makaho xakaje mata? Ta maimaita maganar da Basira tai sannan tacigaba da cewa " me hakan yake nufi? Duk wanda qwaqwalwarsa take aiki na tabbata xai gane magana ce aka yita mai ma'ana biyu, a makaho zakaje mata?ko da ido?"
Lantana ta kalleta cikin tsoro, Mairo ta mike ta tsaya gaban Lantana tace " zan gyara tambayar dana miki d'azu, Yaya yana gani?"


Idanu Lantana ta runtse batace komai ba, Mairo tace " zan kara gyara tambaya ta, Lantana meyasa yake pretending din baya gani?"


Lantana ta girgiza kai tace " nima bansan komai ba, da sauri tabar d'akin tare da janyo kofa."


Mairo tai shiru tana tunani, me yasa yaya yana gani yake nuna baya gani? Wani irin abu ne yau takeji haka? Abubuwan da sukai ta faruwa dashi yana yari ta tuna, kai ta girgiza tace bazai yiwu ace pretending yakeyi tun da ba sai dai in warkewa yai."


A can bangarensu Basira kuwa, kallansa tai tace " Abu Turab harga Allah zaka cemin baka san Mairo tana sanka ba?"
Kallanta yai yace " Umma!"
Tace " ni mahaifiyarka ce nasan abinda zai taimakeka gun samun farincikinka, Mairo zata kula dakai, zata taimakeka ni aguna ita kadaice zata dawoma da farincikinka."


Idanu ya runste yace " nifa Mairo kanwa tace ban taba tunanin zaman aure da ita ba."
Jiyai tace " sai ka fara yanzu."
Mamaki ne ya kamashi yace " Umma nawa nake? Shekarata kwatakwata nawa? Taya zakumin zancen auren mata ba d'aya ba har biyu a rana d'aya wanda kuma duk cikinsu ba alakar soyayya dake tsakaninmu?"
Basira tace " Ba takura maka zanyi ba sai dai inaso ka duba ra'ayina ka kuma ba shawarata lokaci mai yawa."
Sunyi shiru kafin tace " tashi kaje."


Mikewa yai ya fita, d'akinsa ya shiga ya kwanta akan gado yana kallan sama.


Mairo ce ta fito kana ganinta kasan tana cikin wani yanayi, Basira ta kalleta tace " Mairo jeki gida zansa a karasa min kitson."
Kai ta girgiza alamar a'a tace " a'a Umma bari na karasa miki."
Basira tace " jike Mairo, ninace kije ai."
Jakarta kawai ta d'auka ta mata sallama tai waje.
Tafiya kawai takeyi amma zuciyarta fal take da tunani kala kala tama rasa ta inda zata samo amsoshin tambayoyin.


Jitai an fizgo hannunta, a tsorace ta juyo, janta kawai taga yayi soron kusa da gun ya sata a ciki.
Hannunta ta shiga fizgewa ta hada cewa " Malam meye hakan? Sakarmin hannu ko?"
Baisake ta ba ya d'ora da cewa " da dan rashin mutunci kina ganina kika wuce ni?"
Kallansa tai cikin takaici tace " Malam sakeni dan Allah, ni ba muharamarka ba zaka wani dinga rikeni? In magana zakamin kamin da baki."
Murmushi taga ya saki yace " Karki damu saura kiris ki zama matata dan na kula shi kadai ne yanya mafi sauki da zan daidaita miki sahu."


Kallansa tai cikin takaici tace " in zama matarka? To ko nidin baiwa ce banaji kamada damar yanke hukunci akaina bare kuma....."
Katseta yai tare da sakin hannunta yace " kin dai san nidin waye kin kuma san matsayina a garin nan, ko Mahaifinki bai isa in yanke hukunci ya canza min ba."
Dan karamin tsaki taja sannan ta kalleshi ido cikin ido tace " Abdulmajid kake ko wa?"


Idanu ya zaro ya kafeta dasu, tacigaba " Zan maka kashaidi xa gargadi na farko kuma na karshe, in har zamuyi magana dakai ka kiyayi min abubuwa guda biyu, na farko kada ka kuskura ka kara rikeni ko ka taba ni ko da kuwa hijab din jikina ne, na biyu kuma kada ka kuskura ka dinga sako iyayena in muna magana, ni yanzu banda lokacin ka abinda ke gabana yafi karfin na tsaya ina bata lokacina."
Matsawa tai da nufin wucewa, fizgota yai da karfi ya bugata jikin bango yace " ke harkin isa ina magana kina magana, har kina da matsayin da zaki kira sunana gatse gatse har kice zakimin gargadi?"
Ajiyar zuciya tai tace " in kaji haushi inji sammaci."
Tana gama fadar haka ta ture hannunsa tai waje.
Kallan bayanta yai cikin kuluwa yace " mu zuba mu gani, ina tausaya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login