Showing 33001 words to 36000 words out of 146065 words

Chapter 12 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

Abu Turab ido lalai ba shakka yaran nan da saninsa.


Suna fitowa ya bi Abu Turab zaimai magana, ya tsaya kusa dashi yace " kai!"


Abu Turab ya kalli gefensa sannan yad'an matso kadan yace " karka damu nikaina bansan waye ya kawo kayan ba."


Yana fadar haka ya juya suka tafi.


Mamaki ya kama Abdulmajid ya bishi da kallo, kallan na kusa dashi yai yace " na fadamai dalilin kiran danamai?"


A'a sunansa kawai ka kira.


Abdulmajid yai dan murmushi yace " wasa farin girki."






*#ABU TURAB🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)






*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*






*Wattpad :-AyusherMohd*

_Kuyi hakuri jina shiru da kukai jiya da shekaran kiya, hakan ya faru ne saboda wani dalili nawa, 👏🏼 nagode kwarai_


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*




*22*




Abdulmajid da sauri ya karasa bangaren Magajiya, ko salama baiyi ba ya fad'a, tana zaune tana duba wasu kaya da tasa aka kawo mata, kayan mata ne aka d'inko kala kala.


Jin shigowar mutum yasa ta d'ago dan ganin wanene.
Abdulmajid ne ya karaso inda take ya zauna ransa a b'ace.
Kallansa tai yace " Yarona lafiya ko sallama babu."


Ya kalleta yace " Umma da alama mun sakema yaran can dayawa."


Ta kalleshi tace "bangane ba? Ni na dauka zakazo cikin murna kamin bayanin abinda ya faru da yaran can, shiyasa naki yardama kowa ya sanar dani nafisan inji daga bakinka."


Abdulmajid yai dan ajiyar xuciya yace " Ai baisa kayan ba, da alama mun sakema yaran nan dan yana makaho shiyasa har yake ganin zai iya takara damu."


Magajiya tamai kallan bata gane ba, nan ya kwashe komai ya gaya mata, wani sansanyan murmushi ne yaga ta saki ta kalleshi cikin murmushin tace " shine kake wannan fushin?"


Kallanta yai cikin mamaki, ta sake wani murmusawa tace " yaro man kaza, karka badani mana Yarimana."


Kallanta yai baice komai ba, tace " yaushe ma aka auri uwarsa, yaushe shima aka haifeshi, yaushe aka daina mai tsarki da wanka? Yaushe ya san kansa?"
Ta sake wani murmusawa tace " ko kamanta haryanzu baisan kalar fuskarsa ba bare yasan na uwarsa bare kuma tamu?"


Abdulmajid ya fahimceta, dariya yai sannan yace "a maida anin kan uwarsa?"


Magajiya tace " in har Mai Martaba ya nemi jin ba'asi to ka tabbatar komai ya koma kan Uwarsa."


Dariya ya saki yace "Allah yabarmin ke Umma Magajiya."
Murmushi tai tace " yaune isowar Khadija fa."
Ya kalli kayan yace " au shiyasa naga kaya kala kala a gabanki? Ashe 'yar d'akinki ce zata dawo."


Cikin jin dadi tace " daurewa kawai nake na rashinta, amma kaga yanzu tunda Inna Lami take akwance sannan ga shi ina tunanin turawa takarda had'in aure zuwa masarautar Kano shiyasa nakesan ta dawo."


Kallanta yai yace " auren wa?"
Tace "auranka mana dolene in nemi masarauta mai karfi in had'a auranka saboda nan gaba ko menene ba wanda ya isa tunanin saukeka daga matsayinka ko kwace ma mulkin ka."
Kallanta yai yanasan magana amma ina bazai iya ba, dan bai taba mata musu ba, kayanta tacigaba da dubawa.
Jiki a sanyaye ya mike yai waje, shikam bai shirya wani aure yanzu ba amma bai isa cewa komai ba, a tsarinsa yafisan yai auren farinsa auren soyayya tunda dai yasan dama shi dolene yai mata dayawa, yana tunanin ina shi ina soyayya da wani bayan an riga an mai aure?


******
Washegari.


Yana fitowa daga d'an nesa ya hangota tana tafiya, tsaki yaja yace " sai na takama yarinyarnan birki."
Kallan na bayan sa yai yace " kiramin yarjnyarcan, ina bangarena."


Ya juya zuwa bangarensa.
Yana shiga yaga an kawo mai abinci ga bayin da suka kawo nan a tsatsaye suna jiran isowarsa.
Zama yai baice musu komai ba, umarni ne ya basu dolene in suka kawo mai abinci sai yaci yaji yamai kafin su tafi.


Da sallama ta shigo fuskarnan tata a d'aure tamau, shima fuskarsa ya had'e bai amsa mata ba ya d'ago ya kalleta.
Kanta na gefe, jitai yace " duk ku fita kubarni da yarinyarnan inasan magana da ita."


Nan sukai waje, itakam haryanzu kanta na gefe.
Kallanta yai yace " ke baki iya gaisuwa ba?"
Bata tanka mai ba.
Ya kalleta yace " zo ki zubamin abinci, tunda naga alama uwarki bata isa dake ba, kullum kina hanyar gantali."


Wani mugun kallo ta bugamai sannan tace " ko karuwanci nakeyi meye naka a ciki?"


Hannu taga ya had'a ya fara tafi sannan ya mike ya tako zuwa kusa da ita, idanunta ta kawar tace " malam lafiya?"


Ganin yanda ya matso daf da ita yasa ta fara matsawa, haka ya dinga matsowa har takai jikin bango.
Hannu yasa a jikin bangon ya tareta yace " abinda kukeyi kenan da makahon?"


Kallansa tai ta had'iyi yawu sannan ta daure tace " yaushe raban ma daka ganni a gidan? Wai ni mena tsolema ne?"


Dariya yai yace " na tsani duk wanda yake san makahon can, balle ke harda dadin rashin kunya."


Sauri tai ta sulale ta kasa ta juya da sauri zata fita, hannunta ya fizgo da karfi, ya dawo da ita gabansa yace " me? Bakyasan kwalliyar da kikai ta goge ne ba tare da kinje gunsa ba?"
D'agowa tai takalleshi cikin takaici.
Ya saki murmusawa yace " ahh ya zakiyi? Gashi kuma baya gani bare ya yaba."


Hannunta tashiga kwacewa, ganin yaki saketa yasa tace " wlh zansama ihu, kasani sarai kuma zan iya."

Kafad'a ya d'aga mata alamar ko a jikinsa yace " Go ahead."


Lab'anta tad'an ciza sannan ta kalleshi ta kara hade rai tace " malam sakeni ko?"


Kallanta yai ba alamar yana da niyyar hakan.
Ta kara cewa Malam sakeni ko?"
Yace "Mairo kenan, inhar kinasan in kyaleki dolene ki daina zuwa gun waccan yaran ki dinga zuwa guna duk da nidin bawai sanki nake ba ko burgeni kike ba sai dai inasan yanayin fuskarki da shape na jikinki."


Iska ya hura kad'an a bakinta tace " hakan kadai kakeso."
Gira ya d'aga mata alamar eh, yamai murmushi sannan tace " sakeni to, indai wannan ne kacal.
Nan ya saketa yana kallanta, tace " nagode sai anjima."
Zai sake magana yaga tayi waje.

Hakoransa yad'an had'e yace " na tsani yarinyar nan, bawanda ya rainani kamarta."


********


Mairo kam tana fita ta gyara mayafinta tafiya kawai take amma gabanta sai fad'uwa yakeyi, haka ta isa b'angaren Basira.


Bayan sun gaisa ne, Basira ta kalleta tace "Mairo yanzu sam kin daina zuwa, yauma sai dana aika kizo sannan kika zo."


Kanta na kasa batace komai ba, kai kadauka irin salahan nan ce.
Basira tace " dama so nake ku fita da Abu Turab gari, na tabbata yau yana bukatar iskar cikin gari bawai ta gidan nan ba."

D'agowa tai tanasan tambayarta abinda ya faru, sai dai bazata iyaba.


Tace " To."
Basira ta kalleta cikin kauna tace " bari a kirashi."
Ta kara cewa to.


Abu Turab yana d'aki a zaune yana karatun alqur'ani, nan aka sanar dashi sakon Basira.


Mikewa yai ya bud'e drawer din da kayansa ke ciki dan canzawa.


Kurama d'ankwalim dake ajiye a gaban kayan ido yai, baice komai ba sai dai ya dade a tsaye yana kallan d'ankwalin.
Kafin ya jawo wani kaya,har ya rufe kofar ya bud'e ya janyo d'ankwalin yardashi yai a kasa sannan ya sura kayansa, ya kara kallan kasa sannan yai waje.
Ya rasa dalilin dayasa yakejin zuciyarsa ba dadi bayan ya yarda dankwalin, sai dai menene dalilinsa na ajiye kayan yarinyar da tunda ta tafi ko sakon gaisuwa bai kara samu ba? Wata zuciyar tacemai wa zata aika? Bayan duk ba sanka suke ba? Shikam ya rasa me yasa yakejin zafinta bayan ya tabbatar ba laifinta bane.


Haryakai kofa ya koma d'aki ya d'au d'ankwallin ya maida cikin drawer din sannan yai waje.
Yana shiga yaga Mairo a zaune, karasa wa yai ya kara gaida mahaifiyarsa.


Mairo ta gaisheshi ya amsa.
Basira tace " tunani nake ko zaka fita gari yawo."
Kallan gefenta yai yace " gari kuma?"
Tace " eh, kullum kana gida a zaune shiyasa nai tunani ko zaka zaga gari dukda ba gani zakai ba amma ina ganin zakaji dadin hakan."


Kai ya jinjina alamar gamsuwa yace " bari na sanar ma....."
Da sauri tace " ku fita kai da Garzali da Mairo kawai."
Kallanta yai yasan me take nufi, dan dama ya dade da sanin so take wata alaka ta shiga tsakaninsu da Mairo.
To.
Abinda yace kenan ya mike.
Mairo itama ta mike ta musu sallama.
Garzali na bayansa ita kuma tana d'an kusa dashi kadan, shikuma yana tafe rike da sanda.
Sun shiga gari ta gefen ido yana ta kallan yanda mutane suke haba haba, ba shakka wannan shine burinsa ya zauna cikin mutane kamar yanda kowa yakr yi bawai gidan sarauta ba.


Jitai yace " Mairo yanzu anbar rigima dai da alama."
Kallansa tai tace " lalai Yaya sai kace wata yarinya?"
Yace " ah lalai ashefa kin girma."
Baki tad'an turo tace " shekarata fa 1."


Yace "16? Amma bakiyi aure ba?"


Fuska ta d'an had'e tace " ba mijin ne."


Ya d'an juyo kadan yace " wanda rannan ya biyoki fa?"
Tsaki tadan yi tace "rashin aikinyi ne yamai yawa."
Yace " da alama dai akwai wanda kikeso ne shiyasa."


Kallansa tai a ranta tace "sosai ma."
Ta d'auka a zuciyarta ta fada sai jitai yace " da gaske?"
Kallansa tai tace " wasa nake."
Murmushi yadanyi yace " kar ki tsaya ruwan ido ki samu saurayin da yake sanki ki aura, bawai wanda ke kike so ba."


Kallansa tai zuciyarta ba dadi tace " kamar yanda haryanzu baka manta da Khadija ba?"


Tsayawa yai cak, ba tare da ya juyo ba, matsowa tai inda yake tace " karka damu Ya Turab ba wanda yasan hakan, ko ince ba wanda zan fadawa."


Bai san sanda ya kalleta ba, yace " me kike nufi? Ko kin tabaji da bakina na fada miki haka?"


Murmushi tamai tace " wani sa'in sai inga kamar kana kallona."
Fuska ya had'e ya juya kai yace " amsarki nake jira."
Daurewa tai tace" a lokacin da Khadija ta tafi bafa yarinya bace ni yaya, ban manta abinda ya faru a lokacin ba, sannan duk sanda muka zauna dakai zancenka kenan khadija tace kaza, ko khadija tayi kaza, a lokacin bansan me hakan yake nufi ba, sai dai daga baya na fahimci meke faruwa."


Abu Turab ya juya yace " banasan wannan maganar, sannan ni khadija banaji ko ganinta ma in nai zan iya ganeta."
Yana kaiwa nan ya cigaba da tafiya."


**********


Tunda suka taho a hanya take kwance kamar mai bacci sai dai zuciyarta fal take da tunani kala kala, Ya Turab!
Abinda zuciyarta take fada kawai kenan, anya zata iya ganeshi? Dan ita kamanninsa ma harsun fara bace mata.
Ba shakka tasha wuya sosai bayan komawarta kano, sai datai sati biyu tana zazzabi zancen ta kenan a maida ta gun Ya Turab kai kace shine ya haifeta.


Yaran gidan har tsokanarta sukeyi suke cemata Aunty Turab.


Duk sanda zatai addu'a kafin ta fara rokon komai sai tamai addu'a, ita har mamaki ma take da haryau bata taba mantawa da addu'ar ba in har tai sallah.


Ko zai ganeta? Dan wani zuwa da Abdulmajid yai shekarar data wuce data tambayeshi Abu Turab cemata yai wai soyayya suke da Mairo, sannan gwara ma ta cire wani lamarinsa, dan shi kam ya ma manta da ita.


A da bata taba tunanin wai san shi take ba, itadai a matsayin yaya ta d'aukeshi sai dai ganin ta kasa cireshi a ranta yasa Aunty Nana wato babbar yarinyar gidan ta fada mata soyayyace bawai 'yan uwantaka ba."


Kanta ta kara kwantarwa jikin motar, ya zatayi in har yama kasa ganeta?
Dama gashi iyayenta nema suke su had'ata da wani yaron babban d'an siyasa a garin kano yake.


Ajiyar zuciya tai sannan ta kara lumshe idanta.




*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)






*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*






*Wattpad :-AyusherMohd*



*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*




*23*




A hanyarsu ta dawowa ne wani ya biyo Mairo da gudu, yana kwalla mata kira.
Abu Turab yanaji ganin taki tsayawa bare amsawa yasa shima bai tanka mata ba, sai dayazo daf dasu yanata haki na gudu yace "Mairo kina jina?"
Kallansa tai tace " nibanji ka ba, lafiya?"
Ta fad'a tana kallan Abu Turab daya cigaba da tafiyarsa.
Leda ya miko mata yace " gashi."
Cikin fada tace " nameye shi kuma?"
Kai ya sosa yana shirin yi mata magana, yana d'agowa yaga bata gun, kallanta yai yanda take dan sauri.


Da sauri itakam ta karasa gun Abu Turab tace " Yaya ba jira?"
Yace " har kin gama zancen?"
Tace "zance kuma?"
"ki koma dan muma gida zamu wuce, sai da safe."
Abinda ya fada kenan ya cigaba da tafiyarsa.
Turus tai agun idanunta suka d'an ciciko, meyasa Abu Turab baya ganin yanda ta damu dashi?


Shikam ko a jikinsa har suka isa gidan.
Yana shiga daga bakin gate yaji ankira sunansa.
Yasan muryar waye, fuskarsa yad'an saki kadan ya juyo saitin inda yaji kiran.


Sabi'u d'an gidan galadima ne ya karaso gunsa, cikin farin ciki yace "Ranka ya dade daga ina haka?"
Abu Turab ya d'an murmusa kadan yace " naje ganin gari."
Sabi'u ya kalli Garzali yace "dafatan ba abinda ya faru?"
Garzali zaiyi magana Abu Turab yai saurin cewa " ba abinda ya faru, sannan inhar ka damu da ni nan gaba inzan fita kazo ka d'aukeni."

Dariya Sabi'u yasa yace " Angama Ranka ya dade, nima daga gun Mai Martaba nake akan maganar binciken abinda ya faru yau."
Fuska Abu Turab ya had'e yace "kai akaba aikin binciken?"
Fuskarsa d'auke da mamakin ganin yanda Abu Turab yai yace " eh, da wani abun ne?"
Abu Turab ya girgiza kai alamar a'a sannan yace " ka koma gida ka kwanta kace bakada lafiya, inyaso zuwa gobe sai ka turo fada a sanar da rashin lafiyarka."

Sabi'u yace " saboda me? Ni ai ina ganin nine na dace da binciken saboda sanar ma Mai Martaba gaskiya abin."


Abu Turab yace " shine dalilin dayasa ai banasan ka amshi wannan aikin."
Kallan Mamaki Sabi'u yamai, Abu Turab ya sa hannu alamar yana nemansa, da sauri Sabi'u ya rike hannunsa yace "ganinan"


Hannunsa ya rike yace " Sabi'u ka manta wacece Magajiya ne? Ina tsoron karkaje daga bincike ta juyo da rashe kanka, dan na tabbata bazata taba bari a gane itace ba, saboda haka ka barni da ita ni zansan wanda ya kamata yai binciken."
Sabi'u ya fahimceshi kwarai hakan yasa bai musa ba yace " shikenan zanyi yadda kace."
Nagode.
Abinda Abu Turab ya fad'a kenan.


********


Tare suka shiga cikin gidan suna tafe suna 'yar hirarsu.


Yazo yin kwana inda zai shiga b'angarensa, wata budurwa ya hango a tsaye a jikin katangarsa, kanta na kasa da alama ba shiga zatai ba kuma da alama basan barin gun takeba.


Harya dauke idanunsa ya kuma maidasu kanta, baiga fuskarta ba sai dai kallo d'aya zaka mata kasan 'yar wani ce.


Sabi'u ne shima idanunsa suka kai kanta, daidainan ita ma ta d'ago, suka had'a ido.
Da sauri ta juya ta shige ta baya.
Sabi'u yai murmushi yace " yau kuma wa na samu?"


"kai da wa?"
Kansa yad'an shafa yace " wata ce da alama biyoni tai sai sai kunya ta hanata tsayuwa."


Kai ya girgiza yace " kana fama."


Tana tsaye ta lungun ta zuro kanta kad'an, idanunta ne suka ciciko da kwalla a hankali wani zazzafan hawaye ya taho mata, kallansa kawai takeyi tana mamakin yanda zuciyarta ta kasa mantawa dashi, har yanzu baya gani? Abinda zuciyarta ta fada kenan.


Hawaye ne suka cigaba da zubowa sosai sai dai sam ta kasa tsayar dasu.


Har suka shiga tanannan a gun ta dade sosai kafin ta juyo ta fara tafiya.


B'angaren Magajiya ta shiga.
Da sallama ta shiga.
Magajiya ta mike cikin tsananin farinciki ta rungume ta.


"lale lale da zuwan Khadija ga, Uwata barka da zuwa."
Mamaki sosai bayinta suka shiga yi, hatta Abdulmajid yayi mamakin ganin Uwarsa ta mike tsaye saboda taro wani ba sarki ba.


Khadija cikin farinciki tace " Nasameku lafiya Umma?"


Magajiya ta saketa ta jawota suka zauna, kallan bayinta tai tace " ku kawo mata abinci."


Tsugunawa tai tagaida Magajiya sannan ta kalli Abudulmajid ta gaisheshi.


Kallan ta yai shima cikin farinciki ya amsa sannan ya d'ora da cewa "inakika tsaya bayan tun dazu aka aiko akan kin shigo?"


Kanta ta sunkuyar batace komak ba, Abdulmajid ya hade rai cikin kuluwa yace "badai Gun......"


D'agowa tai fuska a had'e itama tace " bangane ba?"


Zaiyi magana Magajiya ta katseshi da cewa " Yarima banasan haka, akan me zaka takurawa Uwata daga zuwanta? Na tabbata nan ta fara zuwa."


Khadija ta d'auke idanta daga kanshi, shikam ido ya kura mata yana zargin anya kuwa ba gun waccan yaran taje ba?


Abinci kala kala aka shiga jerawa, Magajiya tasata a gaba tana ci suna hira, bayan ta gama ta sa aka d'auko mata jakar kayan datasa akadinka mata, Khadija cikin jin dadi tace " nagode sosai Umma."


Magajiya ta kalleta tace " yaushe zakije duba Inna Lamin?"
Khadija tace " zuwa gobe, amma ya jikin nata?"


Abdulmajid yai dan kasa da kai yace " jiki fa ba sauki tana nan dan ko fitsari a kwance take, 'ya'yanta duk sun kama gabansu ba mai kula da ita, hmmita kam wannan gwara ma ta mutu ta huta."


Magajiya ta d'an tabe baki, khadija ta kalleshi tace " ko ma menene Yaya bai kamata ka fadi haka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login