Showing 39001 words to 42000 words out of 146065 words

Chapter 14 - KAINUWA (Dashen Allah) Book Complete Document by Ayusher Muhd.txt

sanar dashi abinda ya samu yayanta sai dai a yanda tasan Turab tana ganin in har yasan abinda ya faru dasu to fa lalai tana ganin xai cire wani farinciki a ransa ne ya juya rayuwarsa zuwa d'aukan fansa wanda ita kuma tana san farincikin danta dukda kuwa tasha alwashin hukunta wanda yama yayanta hakan.


Kallanta yai ganin yanayin datake ciki yasa ya runste idanunsa da karfi sannan ya mike yai hanyar fita.


Jiyai tace " shikenan Abu Turab."
Tsayawa yai sannan a hankali ya juyo ya kalleta, ta mai murmushin yake sannan tace " hankalinka ya kwanta?"
Kallanta yai cikin wani yanayi, sannan a hankali ya taka inda take zaune ya tsugunna gabanta yace "Umma do u trust me?"


Kallansa tai tace " me kenan?"
Dariya yad'anyi kadan yace " nufina kin yarda dani?"
Kai ta d'aga mai, ya dan murmusa yace " shikadai nake bukata, yardarki gareni, in har kin yarda dani inaso ki yarda xan kula dake bazan bari wani abu kuma ya samen ba sai dai abinda Allah ya kaddara."


Kai ta jinjina mai tace " nagode Abu Turab, sannan insha Allah ba abinda zai sameka."


Mikewa yai ya mata sallama zai fita.
Mairo wacce ta kawoma Basira gwaza wacce mahaifiyarta ta dafata ta fere ta sa ma kula, taxo shiga taji yana cema Basira do u trust me? Wanda hakan yasa ta koma ta tsaya.
Jin alamun fitowarsa yasa ta juya da sauri zatai waje garin sauri kafafunta suka harde, baya tai luu kamar zata fadi.
Cikin hanzari ya karaso ya tareta.
Idanunta ne suka sauka akan nasa, kallansa tai cikin tsananin mamaki, da sauri ya saketa dan sam ya manta ashefa batasan yana gani ba.


Jikake tim ta fadi a kasa, sosai taji xafin faduwar saboda sam bata zaci zai saketa ba, kallansa tai kamar tai kuka dan bakin ciki.


Hannu yasa yace " sannu faduwa kikai?kina ina?"


Haushi ya kamata ta mike ta matso inda yake tace " yaya fadamin gaskiya, da saninka ka sakeni ko?"


Gefen inda take ya kalla yace " me kike nufi?"


Sake baki tai cikin salon shagwaba tace " inba haka ba tayaya ka taimaken kuma zaka sakeni?"


Murmushi yai dan tabbas yaga faduwar datai yasan taji zafi yace " au so kike in rike ki?"
Kallansa tai tace " yaushe nace haka?"


Iska yadan furzar yace" lalai Mairo da alama aure kikeso."
Ya juya da sandarsa ya fara tafiya.


Takaici ma ya hanata magana, aure takeso? Me yake nufi da hakan?


Kallansa tai ta baya a hankali tace " na tabbata mun fa hada ido dashi."


Tana neman amsar tambayarta taji muryar.



Lantana taji tana cewa " Mairo? Me kike anan a tsaye?"


Juyowa tai ta kalleta idanunta sun dan ciciko, kusa da ita taxo ta ajiye kula tace " kiba Umma."
Ta juya da sauri tai waje.


Abu Turab kam b'angarensa ya nufa yana bud'e gate, bayinsa suka taho da sauri suka karasa bud'e mai kofa.
Ciki ya shiga, yana zama Garzali ya mikomai abu a bakar leda.


Yace "Ranka ya dade gashi an aiko a kawoma."


Yace "Magajiya?"
Garzali yace " a'a wlh bansan waye ba kawai kawowa akai, dana tambaya inji waye sai wacce ta kawo ta juya da gudu."




Ya gane Khadija ce, bai sa hannu ya amsa ba yace " ajiye anan kwanciya nake sanyi."


Ajiye wa yai ya mike a hankali yai waje.
Yana fita ya kalli ledar, shiru yai yana tuno fuskarta, fuskar daya dade yana san gani duk yanda yaso ya yage ta a ransa ya kasa, dan karamin tsaki yaja sannan ya sa hannayensa kan goshinsa.




Khadija kam bayan ta aikamai da magani gida ta tafi ta shige dakinsu ta fada gado ta kwanta, kuka kawai takeyi tana jin xafin abinda akama Turab.


Duk yanda mahaifiyarta tai akan ta bude kofar taki, ko abinci kinci tai.




*********


Yau kwanan Basira ne, ta shirya tsaf ta nufi bangaren Mai Martaba.




Bayan sun kwanta ne ya kalleta yace " Basira."


Kallansa tai ba tare da ta amsa ba, yacigaba " me kike tunani game da auren Turab?"


Kallan mamaki tamai tace "aure? Takawa ka manta Abdulmajid baiyi aure ba?"


Kallanta yai yace " na sani sarai sai dai inatunanin auran sa zai sa matsayinsa da kimarsa ta karu a gun mutane sannan inasan nemarmasa matar da zata taimakeshi yanda ko ansan yana gani ba wani wanda ya isa ya nemi cutar dashi."


Kallansa tai tace "ban gane ba?"



Yace " me kike tunani game da hadin aure da 'yar sarkin kano?"


Kallansa tai tace " Bilkisu?"
Kai ya daga mata alamar eh.
Kallansa tai jiki a sanyaye tace " amma kana ganin za'a bashi? Na farko shi makaho ne a idan duniya sannan Bilkisu ita kadaice mace a gun Sarki Muktar wato sarkin kano, ni nafi mai sha'awar mairo 'yar gidan Barde."


Kallanta yai yace " Na fahimceki sai dai ina so ki sani Abu Turab ba mijin mace d'aya bane sannan yana bukatar mace kamar Bilkisu saboda taimakamai wajen hawa mulki."


Da sauri ta mike zaune cikin tsananin tashin hankali tace " me? Mulki?"


Kallanta yai ya daga mata kai.


Idanu ta zaro cikin tsananin mamaki, yace " Bilkisu ita Magajiya takesan aurama Abdulmajid in har ya aureta ba makawa sai ya hau mulki, bakya tunanin abinda zai faru da rayuwar ku ke da Abu Turab kn har Abdulmajid ya hau mulki?"


Kallansa tai duk tama rasa ta cewa dan ta tsorata da zancen.


Ya kalleta yace " Abu Turab shi kadai ne wanda ko bayan raina na tabbata bazai wulakanta ahalina ba, bazai wulakanta mutanena ba, bazai rushe rayuwar dana gina a kasa ta ba."




Kai kawai tashiga girgizawa tana tsoron abinda zai faru da wannan sabon lamarin.......






*ABU TURAB TEAM*🤝🏻
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*26*




Kallansa tai cikin tashin hankali tace " mai kake nufi da kalamanka? Nasani ka fini iko da Abu Turab sai dai ina rokonka kabar maganar nan a kan gadon nan, ni zan manta munyi wannan maganar dakai."


Jitai yace " kin taba jin inda akai magana bayan wanda aka fadama maganar yaji sannan yace zai manta maganar? Ai magana ana manta tane in batada mahimmanci."


Kallansa tai tace " dan Allah kabar maganar nan, nafisan Turab ya auri Mairo ya bar gidan nan dan samun farincikin rayuwarsa."


"In kuma kaddararsa ce mulkin fa?" Jin maganar tai batai zata ba, Kallansa tai batace komai ba.
Shima bai tanka mata ba ya kwanta tare da juya bayansa.
Ta dade a zaune tana kallansa kafin ta kwanta.
Idanunsa a bud'e suke tunani yakeyi " bazai iya sanar da ita su Magajiya sune sanadiyyar makantar Abu Turab ba saboda bayasan ya sanya mata damuwa da kuma shiga wani yanayi najin wannan zancen.


Ba shakka shikanshi jin wannan zance ya daga mai hankali matuka, kamar wasa d'azu da rana Khadija yar gidan Hisham ta samu barde da sakon Lami akan dan Allah tanasan Mai Martaba ya ziyarceta dan akwai magana mai mahimmanci da takesan sanar dashi.
Ganin yanayin aikin dake gabansa yasa ya aika Barde akan yaje yaji menene.
Zuwan Barde ya taradda ita cikin mugun hali, tana kwance ko mikewa bata iyayi, ba kowa a gunta d'akin banda wari ma ba abinda yakeyi wai a hakan ma zuwan Khadija ne ta gyara mata d'azu.
Barde ya kalleta tare da dubata, ya d'ora da cewa "amma ya akai ke kad'ai anan?"


Tana kwance sai numfarfashi takeyi tace " Barde."


Kallanta yai cikin tausayawa yace " Mai Martaba wani uzuri ya rikeshi shine yace inzo inji menene, bai san jikin naki haka yakoma ba."


Hawayene suka gangaro mata tace " Barde ni tawa ta kare dan banaji ko gobe zan kai a duniya, dan Allah ka nemarmin yafiya agun Abu Turab, Basira da Mai Martaba."


Kallan mamaki ya mata yace " ban gane ba."
Hawayene suka kara kwaranyu mata tace " nice sanadiyyar makantar Abu Turab dan kuwa nice na je gun malami aka makantar dashi, kwanakin nan ko bacci na fara ganin yaro nakeyi ba ido yana tsaye a gabana, na tabbata laifin danai ne yake bibiyata, na sani alhakinsa ne ma ya kwantar dani haka, 'ya'yana da 'yan uwana da nake komai dan faran ta musu rai duk sun gujeni....."


Kuka ne yaci karfinta wanda yasa ta kasa karasawa, jikin Barde ne ya mutu mamaki da tsoron wannan al'amari yasa ya taho daga gidanta ba tare da ya gamajin kalamanta ba.


Idanu mai martaba yadan runtse a ransa yace " bazan taba yafe musu ba."
Babban bakin cikinsa shine a matsayinsa na sarki bashida hujjar hukuntasu, na farko bashida kwakwarar shaida sannan inma yana tunanin Lami zata zamarmai shaida ya tabbata Magajiya juya abin zatai kanta ko za'ai me bazata taba cewa itace sila ba.


Ba shakka sanya Abu Turab a mukamin Sarki ita kadai ce hanyar da zai sa ya hukuntasu ta ruwan sanyi wanda yafi na zafi kuna.


Dolene Abu Turab ya auri Bilkisu dan kuwa wannan shine mataki na farko na cinma burinsa.


Basira ma bacci ya gagareta ta rasa abinda ke mata dadi, itakam ba wata 'yar sarki datake so Mairo takeso ta bashi ko dan farincikin sa na nan gaba.


***********


Washegari da safe Abu Turab ya tafi garden din mahaifinsa wanda a yanzu shike zama agun dan kebencewa daga hayaniya, yana zuwa gun ne a duk lokacin da yake bukatar yin dogon nazari game da wani abu.


A zaune yake akan kujera ta karfe dake gun, shukoki kala kala ne a gun, wanda ya kayata gun, kansa ya kwantar a kan saman kujerar ya lumshe idanuwansa tare da dora hannunsa daya kone akan goshinsa.


Kana ganinsa kaga mai bacci, shigowa tai a hankali gun, tafiyarta takeyi mai sanyi tana tafe tana duba inda yake, cak ta tsaya a yayin data han goshi akan kujera, tunda ya fito ta biyoshi, sannan matsayinta yasa fadawan dake gadin kofar shiga gun basu hanata shiga ba.


Murmushi ne ya bayyana a fuskarta ganin yanda ya ke, ta dauka bacci yakeyi hakan yasa ta tako a hankali tazo inda yake.
Ta bayan kujerar ta tsaya ya zamana tana tsaye saman inda ya kwantar da kansa.


Hannunsa ta kalla gun yayi jaa har yanzu amma bai duri ruwa ba.


Kallansa takeyi tanajin wani sanyi na ratsa dukkan sansan jikinta.
Jin kamar mutum na kusa dashi yasa ya bud'e idanunsa a hankali.
A hankali ya kara maida idanunsa ya lumshe dan ya tabbata mafarki yakeyi, ba wanda ya taba biyoshi gun sannan in ma ana biyoshi mai zai kawo Khadija nan?


Idanunta ne suka ciciko a hankali tace " yanzu fa bazai ganni ba ko?"
Idanunsa ya kara budewa ya daurasu a kanta, itama kallansa tai.
Da sauri ya mike zaune ya dan maze yace "akwai mutum anan ne?"


Khadija batace komai ba, jin yayi shiru yasa a ranta tace " da alama bai san dani ba."
Dawowa tai ta gabansa ta tsugunna tare da tagumi kallansa kawai takeyi, ba shakka su Magajiya da Mahaifinta sun bata mata rai sosai wannan wace irin muguntace?


Abu Turab yana ganinta amma sai yai kamar bai ganta ba.
Sunfi minti talatin a haka kafin daga bisani ya mike rike da sandarsa.
Yace " na dauka nayi magana akan wanene anan ko? Ko dan bana gani an dauka bana jin motsi da numfashin mutum?"


Idanu Khadija ta zaro itama ta mike tsaye, juyawa taga yayi zai tafi da sauri ta sa hannu ta rike rigarshi ta baya.
Tsayawa yai va tare da ya juyo ba, yace " wanene?"


Shiru tai batace komai ba, rigarsa ya fizge ya fara tafiya da sauri ta sa hannu batasani ba ta riko hannunsa.
Tsayawa yai sai dai wannan karan ya juyo.
Hannunta ta kalla da sauri ta sakeshi tace " Yaya nice."
Fuskarsa a d'aure yace "kece wa?"


A hankali tace " Khadija ce."
Gani tai ya sake juyawa zai tafi.
Gabansa tasha da sauri, shikuma yai kamar bai ganta ba ya taho ya dauka in ya taho zata matsa ita kuma bata taba tunanin zai zo daf haka ba.
Jikinsu ne ya hadu da juna wanda tsoro yasa ta rike rigarsa tai baya da sauri, shi kuma rike rigarsa datai yasa ya fada kanta suka fadi tare?


Idanunta ta rufe saboda tsananin kunya, shikam kallanta yai sosai dan bai taba kallanta daf da daf ba sai yau.


Idanunta a rufe tace " Ya ka d'agani!" Cikin shagwaba tai maganar kallanta yai yace " da wayace ki yarda ni?"


Tace " ni kuma? Yaushe?"
Mikewa yai tare da sa hannu ya d'agota hannu tasa ta rufe fuskarta.
Juyawa taga yayi zai tafi sai alokacin ma abin yazo mata to ma in taji kunyarsa inama ya gani?

Daurewa tai tace "Yaya kayi hakuri."
Yace "game da me kenan?"
Tana tsaye a bayansa tace "game da komai ma."
" niban fahimci hakurin da kike bani ba ai."


Hawaye ne suka fara zubo mata, cikin kuka tace " na konewar da kai wanda su Umma Babba suka ja ma."


Fuskarsa a had'e yace " wannan kuma menene naki a ciki? Meye naki na bada hakuri?"


Kallansa tai ta baya tace " taya zaka ce haka Yaya?"
Cikin bacin rai ya Juyo ya kalleta yace " kukan me kike kuma?"
Cikin kuka tace " ni kaina so nake hawayen su tsaya."
Dan karamin tsaki yaja yace " abinda ya kamata kuma nakesan naji kin ban hakuri akai da alama ma bakisan shi ba, bana bukatar kukan ki ba kuma na neman ban hakurin ki."
Juyawa yai kamar zai tafi.
Rigarsa ta sake rikesa amma hanzu hannun rigar ta rike, a hankali ta furta "Yaya kayi hakuri tafiyar danai ba tare da nama sallama ba."




Jikinsa ne yai sanyi, bai juyo ba, ta kara share hawayenta zatai magana ya juyo cikin bacin rai yace " kinsan kwana nawa nai ina jiranki? Awanni nawa nai ina nemanki? Lokuta nawa na bata ina tunanin dawowarki? Zaki tafi menene inkincemin zaki tafi? Hanaki zanyi? Ko dan Kinga na dogara da zuwanki a koda yaushe? Sai dai inaso ki sani na dade da mantawa da ke da jiranki."


Juyawa yai ya fara tafiya, tsugunnawa tai kawai tasa kuka.


"Ba laifina bane yaya, ba laifina bane nikaina banso tafiya ba, ba laifina bane."
Abinda kawai take fada kenan.
Yana jinta yai waje shikanshi kukanta har jikinsa yake ji.
Yana fita ya jingina da jikin kofa ya dade a haka kafin ya sa sandarsa ya fara tafiya.


********




Mairo ce zaune tana wanke wanke tanayi tana 'yar karamar mita dan itakam ta tsani abinda ake mata, mahaifiyarta su biyu ne, kishiyar babarta sam bata sa nata 'ya'yan aiki amma ita kullum ita ake sawa aiki kuma tanayi ba a gode mata sai tai magana mahaifiyarta tace batada hakuri.


Sa'arta ta gani ta gun kishiyar mahaifiyarta ta kalleta tace " nikam Karima wai nikam sai yaushe zaku biyani kudin wata?"


Karima ta kalleta tace " kudin wani watan kuma?"
Mairo ta harareta tace " na albashin aiki da kuka daukoni mana."
Karima tace " ban gane ba"
Mairo cikin masifa tace " nifa bazan laminci wannan rainin hankalin ba ehe, sai kace wata 'yar aikinku?"


Muryar maman Karima taji a bayanta tace " to bazasuyi ba kedin meye aikinki? Tunda kinki aure?"
Mairo tai dariya tace " dan ma dai bani kadai bace banyi auran ba."


Karima tace " da wa kike?"
Mairo tace " wanda ya tsargu, haka kawai tunda mai taya mu aiki tai tafiya kullum ni nake aiki ni ba 'yar aiki ba bakuma baiwa ba?"


Jitai an dada mata duka a bayanta ta juyo da nufin masifa, mahaifiyarta ta tagani, ta kalleta tace " Mairo bana hanaki ba?"


Turo baki tai batace komai.






*ABU TURAB TEAM 🤝🏻*
.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*


*Wattpad :-AyusherMohd*


*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*


*27*




Garzali ne ya biyoshi suka nufi fada dan yanzu aka aiko akan yaje saboda Abdulmajid zai sanar da binciken dayai.
Bayan sun zauna ne Abdulmajid ya dawo tsakiya sannan yace " Ranka ya dade na gama bincike."
Galadima ne yace " to munajinka."
Abdulmajid yai d'an gyaran murya sannan yace " bincike ya nuna mana cewa ba kowa bane ya jawo wannan abin ba sai mahaifiyarsa."


Jin wannan zance yasa mutane suka fara kananan magan magan, Abu Turab kam wani murmushi ya saki kansa na kasa a ransa yace " they take the bait."


Kallan Abdulmajid kowa yai, Mai Martaba ya kalleshi yace " meye hujjarka na fadar haka?"
Abdulmajid ya gyara zama yace " Mahaifiyarsa tanasan asan shi wanene, ma'ana asan shidin d'an sarki ne, sannan tayi hakan ne dan mutane su farga susan akwai wani magajin sarkin bayan ni."


Mai Martaba yace " wannan ita kadai ce hujjarka?"
Kai ya girgiza alamar a'a yace " tayi abu kala biyu, na farko in har yasa mutane zasu sanshi saboda kayansa da kuma yanayin dokinsa, na biyu kuma ba wanda zaiyi zarginta sai dai kowa yai zargin Magajiya, kunga ta jefi tsintsu biyu da dutse d'aya."


AbuTurab ya d'ago kai yace " Bravo! Ba shakka wannan ma abin dubawa ne."
Mamaki hakan yaba Abdulmajid ya dauka abin zai tadamai hankali.
Barde ne ya katse mai tunaninsa da cewa " shaidu fa?"


Abdulmajid ya juya yace " shigo."
Nan wani bawa ya shigo wanda kowa ya sani bawa ne wanda ke kula da al'amuran Magajiya na waje bana ciki ba.


Daga can bakin kofa ya zube ya gaidasu, Abdulmajid yace " wannan bawan bawa ne ga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login