Showing 96001 words to 99000 words out of 273152 words

Chapter 33 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72734

yake daman ac motar ya gama ratsa kassan jikinta har ya soma saukar mata ta zazzabi.


“Ka sauke ni a nan... ”


Ta fada muryarta na rawa hakoranta na kasa na haduwa da na sama. Juyawa yai ya kalleta for no reason ya ji ta kara bashi tausayi domin har numfashinta wani sama yake kamar zai bar jikinta, silently ya sauke ajiyar zuciya ya juya ya cigaba da tukin, zuciyarsa bata raya masa ko'ina ba sai gidan Momy. Kai tsaye ya nufi can duk kuwa da kasancewar ba shi da tabbacin tana gidan a irin wannan lokacin kasancewarta likita. A kofar gidan ya faka ya bude motar ya fito ya zagaya side dinta ya bude mata.


“Fito”


Ba musu ta sauko da kafafuwanta sannan ta fito gaba daya tana hawaye kamar ba gobe, ga zafin da goshinta yake mata ga kuma tsoron maganar Mansura sai ta ji abun ya hade mata ya zame mata biyu a lokaci daya.


“Zamu je ciki Momy ta duba ki sai na kai ki gida”


Ya fada mata saitin kunnenta, ita dai bata ce masa komai ba, har ya rika hannunta ya doshi gate din da ita yai knocking mai gadin ya bude ganin Sirleem yasa shi washe baki.


“Ranka ya dade kai ne ka tsaya waje?”


“Bana son bata lokaci na shigo da motar ne, fatar dai Momy tana nan”


“Eh Hajiya tana ciki”


“Okay”


Ya fada yana nasa kafarsa cikin dakin bayan mai gadin ya bashi hanya, a lokacin ruwan sai sauka yake da dan karfinsa sai dai be damu da ruwan ba tafiyarsa yake a natse har ya isa gurin kofar ya kwankwasa kofar falon. Sai da ya ji motsin taba kofar da ake ana kokarin budewa sannan ya saki hannun Falmata. Wani kyakkyawan saurayi ne da ba zai wuce 23-24 ba bude musu kofar, Sirleem ya mika masa hannu suka gaisa.


“Ameer kana nan ashe?”


“Eh Wallahi hutun be kare ba”


Ya fada yana janyewa jikin kofar wanda hakan ya bawa Sirleem da Falmata damar shigowa falon.


“Zauna a can”


Sirleem ya fada yana nunawa Falmata inda zata zauna, shi kuma ya nufi upstairs kai tsaye domin yasan Momy tana dakinta a irin wannan lokacin. Har Falmata ta zauna a inda Sirleem ya nuna mata Ameer da ya koma dinning ya cigaba da cin abincinsa be daina kallonta, be san alakarta da Sirleem but if he can remember ko a farkon ganin da yai mata a gidan Sirleem ne ya zo da ita, and now ya sake kawota jini na zuba a goshinta gashi sai hawaye take tana ta share majina da hijabinta. He don't know why yake ta kallonta ko maybe saboda tana black beauty like his skin ko kuma saboda kukan da take ne he don't know.










__________


Assalamu Alaikum, fatar kuna lafiya ina son nai amfani da wannan damar na ba makaranta littafin Fulani hakuri na jina shiru na tsawon lokaci, hakan ya faru ne sakamakon yanke mana network da akai a garin Gusau saboda matsalar tsaro da muke fama da ita. The sad news is ana saura two days a saki network aka sace min waya, na yi losing komai ciki har da typing din da nai na book din Fulani a lokacin da babu network din. Amman yanzu Alhamdulillah komai ya daidaita da yardar Allah zamu cigaba kamar yadda muka saba. Fatar za a min afuwa.


Thanks.


Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 09:24 - 🤐🤐🤐🤐: 26


*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence to 08036126660*






FALMATA POV.


Kanta na kasa har Sirleem ya sauko stairs din tare da Momy dake sanye da kayan bachi, idonta sanye da farin gilashi ya zauna a fuskarta das kana ganinta ka ga likita.
A kujerar dake facing din inda Falmata take zaune ta zauna tana kallonta.


“Me ya samu goshin na ki?”


Momy ta tambaya tana kallon Falmata, Falmata kan aikin kuka kawai take, bata ji abun da Momy tace ba balle har tai yunkurin bata amsa, tun da ta kalli Momy sau daya bata sake daga kanta ba.


“Bata ji sosai ai Momy ko kin manta”


Sirleem ya ba Momy amsa yana kallon Falmata, har cikin ransa yake jin kukanta, daman can tausayinta ya kama shi balle kuma yanzu jini ke mata zuba a kai. Momy ta maida dubansa a gurinta.


“Me ya same ta?”


Shiru yai yana kallon Momy kamar ba shi ta tambaya, tsoron bata amsa yake domin ya san ita ma tana daga cikin mutanen da basa son mu'alarsa da Mansura.


“Mansura ta fasa mata goshi, she thought ko son ta na ke.... ”


“Sai take kishi right?”


Momy ta karasa masa, sai ya shafa kansa ba tare da yace komai ba.


“Sirleem wai miye a jikin Mansurar nan ne? Yarinyar nan ta tsofe ka, Hajiya da kowa ma baya son alakarka da ita then why zaka nace akan dole sai ka yi alaka da ita? Ji yadda ta ci zalin din karamar yarinya, ya ama akai ta ganta”


“Na ganta ta fito a masarautar ne so i thought ko gurina ta zo, muna tare da Mansura bakin titi a lokacin, ita kuma zata je gida ashe aiki take na ga dare yayi ace ta tafi gida a kafa sai nai deciding na sauke ta a mota na....”


Bakin ya tsaya ko be karasa ba, ya san Momy zata iya gane abun da ya faru. Cikin wani irin bacin rai da Momy bata san ta ina ya fito mata ba ta kalli Falmata.


“Ke kuma iyayenki wadanne irin iyayen ne wai? Taya zasu rika wulakanta ki any how? Why? A barki ki tafi gida a irin wannan lokacin babu komai a ransu?”


Falmata ta ji abunda Momy take fada saboda ta fada ne ta sigar fada, sosai ran Momy ya bace ta abun da taji tana samun kanta a irin wannan yanayin a duk lokacin da ake kokarin lalata rayuwar yara musamman mace, wata kila saboda ita bata haihu ba ne ko kuwa saboda tana mace ne.


“Ameer dauko min kit”


Ta fada tana kallon Ameer din tare da cire gilashin idonta. Mikewa Ameer yai daga inda yake tsaye ya nufi wani karamin daki dake facing din dinning room.


“Momy idan zai yi har kunne a duba mana”


“Me ya samu kunnen nata?”


“I don't know”


Ya amsa mata yana daga kafadunsa.


“If you don't know then how will I support to help her? Idan da abun aka haife ta zai yi wuyar wakarwa”


Sirleem dai be sake cewa komai ba sai kallon Falmata yake not knowing what to say, Sai Momy ta kalleta ta aika mata da tambayar da muryar da zata iya jin.


“Ke me ya samu kunnenki?”


“Ba... Baba... Na... Ya.. Mare... Ni sai kunnen ya rufe”


“Kai Subhanallahi... Wannan yarinya kina ganin rayuwa, wai iyayenki ba sa son ki ne? Mu muna neman yaya ido rufe wasu na wulakantawa?”


Momy ta fada tana jin wani irin zafi a ranta, how she wish ace Falmata is her child da taga gata da tarairaya.


“Wannan ai cutarwa ce are they her real parents?”


“Yeah i think so, maybe yana da yaran da yawa ne, and ta fada ai tana hannun step mom dinta ne”


Momy bata sake cewa komai ba sai kallon Falmata take cike da tausayawa, kamar yadda Sirleem ma yake kallonta. Ameer ya ake ma Momy kit din ya koma kusa da Sirleem ya zauna yana ta kallon Falmata da yake ta jin kamar ya santa. Da hannu Momy tai mata alama da zo sai ta tashi ta matsa kusa da Momy ta zauna tana ta hawaye. Sai da Momy ta fara saka safa sannan ta umarce Falmata ta cire hijabinta ta rika goshinta ta fara gyara mata goshin.


“Wane irin aiki take a gidanku? Kai ka sam mata aikin ko?”


“No na ganta ne ni ma fa a yau she said tana kula da yaran Shattima ne”


Daga haka Momy bata sake ce masa komai ba har ta gama da goshinta, sannan ta dauko wata farar takardar tai rubutu akai ta mika mata.


“Ka siya mata wannan maganin kuma ka kawo ta gobe asibiti na duba kunnen”


“Thank Youu Momy”


Ya fada yana mikewa tsaye, ganin hakan yasa Falmata ta dauki hijabinta zata saka sai Momy ta dakatar da ita.


“No jira, Ameer samo mata wani Hijab a cikin hijabaina ta saka wannan duk ya bace da jini”


Sai da ya kalli Falmata sannan ya mike tsaye ya nufi upstairs, be dade ba ya sauko rike da hijab green ya mikawa Falmata.


“Na gode Allah ya saka da alheri”


Falmata ta fada cikin muryar kuka.


“Amin Allah yai miki mafita”


Momy ta fada tana jin wani irin tausayinta a ranta. Sannan ta sake kallon Ameer dake tsaye kusa da ita.


“Samo mata leda ta saka wannan”


“Momy na gaji fa”


Ya fada yan juyawa ya nufi hanyar kitchen, dan Murmushi Momy tai ta maida dubanta gurin Sirleem.


“Sirleem ya fadawa yarinyar gaskiya, saboda ta cire rai a aurenka tun yanzu, kasan Hajiya babu wanda take son ka aura sama da Nana idan har kana son farinciki a rayuwarka kuma dole ka bi umarninta”


Silently ya sauke ajiyar zuciya yana kallon tsadadden agogon hannunsa kamar ba zai ce komai ba.


“Momy ba ki yi tunanin ya kamata ki taya ni wannan yakin ba?”


“Ba zamu zo ka auri karuwa ba...”


Ta bashi amsa kai tsaye sannan ta mike tsaye ta nufi upstairs ba tare da ta masa sallama ba. Da kallo ya bita har ta haye sannan ya sauke kansa akan Falmata yana dan murmushin da be kai zuci ba? Ta ya zai fasa auren Mansura bayan yayi mata alkawari? Juyawa yai ya nufi kofar fita ba tare daya jira an kawowa Falmata ledar ba. Fitarsa da minti daya Ameer ya fito rike da leda a hannunsa ya nufo inda Falmata take ya mika mata.


“Na gode”


Ta fada tana kokarin karba, ta dauki hijabin ta saka a ledar sannan ta mike tsaye ta nufi kofar ta bude, har ta fita Ameer kallonta yake. A entrance din ta tararda Sirleem tsaye yana jiranta, ganinta yasa ya sauka ya fara takawa ko kadan ruwan dake sauka be dame shi ba, ganin hakan yasa ita ma ta bi bayansa tana tafiya har suka fita gate din. Da kansa ya bude mata front seat ta shiga ta zauna sannan ya zagaya ya shiga side dinsa ya mika mata hannu.


“Ina takardar da Momy ta baki?”


Ta mika masa, sai da ya karanta sannan ya kalleta da muryar da zata ji yace.


“Zan bi ta chemist na siye miki maganin”


Ta daga masa kai tana kara kama jikinta, sanyin ruwan sama sai ya hadu da na ac motar ga kuma ciwon da kanta ke yi sai suka sakar mata da zazzabi. Kallonta yai for few seconds sannna ya bude motar ya fita ya zagayo ta gefenta, bude side dinta yai ya kwantar mata da kujerar sannan ya mika hannunsa bayan motar ya janyo jacket dinsa ya lulluba mata saman hijab dinta sannan ya rufe motar ya zagaya side dinsa ya shiga ya tashi motar sai da suka hau hanya sannan ya kashe ac, each and every three minutes sai ya kalli Falmata, rayuwarta yake tausayawa as her age ace bata gida gaban iyayenta a irin wannan lokacin, yanzu idan shi wani mugun mutum ne me zai faru kenan? Gaban wani katon chemist ya faka motarsa ya fita ya bar Falmata a motarta, kamar fitarsa take jira bachi yai gaba da ita har ya siyo maganin ya dawo cikin motar bata sani ba. Sai da ya kalleta sannan yai ma motar key suka hau titi.


“Heyy.... ”


Ya fada yana taba ta a hankali, sai ta bude ido ta farka a firgice, si ya kai bakinsa saitin kunnenta.


“Ina ne unguwarku ma?”


Ta fada masa, sai ya gyada mata kai. This time around ita ce take ta kallonsa har suka isa cikin unguwar da be taba zuwa ba sai yau.


“Ina gidanku yake?”


“Ina gidanku yake?”


“Yana can ciki mota bata shiga”


“Okay, bari ruwan ya rage sai ki sauka”


Daga haka ya kunna wutar motar ya soma nuna mata yadda zata sha maganin.


“Na gode Allah ya saka da alheri”


“Gobe misalin uku na rana ki dauki permission a gurin aikinki sai ki same ni a gidanmu na kai ki Momy ta duba kunnen ai kina so ko?”


Ta gyada masa kai alamar tare da dagowa da sauri.


“Eh ina so sosai”


“Okay gobe ki musu magana sai na kai ki asibitin da take aiki a duba ki”


“Ina ne gidanku?”


“Gidan da kike aiki, amman b bangaren Ammy ba bangaren kishiyarta”


Shiru tai kamar mai tunani, sam bata dauka Ammy na da kishiya ba, sai yau.


“Oh ki fito bakin gate din ku ki tsaya idan uku na rana yayi zan same ki a gurin okay”


“Tau...”


Ta fada tana kallonsa sannan ta shiga kokarin bude motar.


“Ba zaki bari ruwan ya gama sauka ba”


“Zan iya tafiya a haka, idan aka fadawa Babana an ganni a mota zai iya kasheni”


Kallon tausayi yai mata sannan unlock din motar ta bude ta fita sai kuma ta duko ta mika masa rigarsa.


“Gashi na gode”


Ya mika hannu ya karba, ita kuma ya juya ya nufi hanyar da zata sadata da gidansu jikinta sai kamshin turarensa yake.








HAJIYA BABBA POV.


Ta kasa zaune ta kasa tsaye sai tunanin yadda zata bullowa lamarin Falmata take, ba Falmata kadai ba har Fadime da Sardauna so take ta sani, ganin abun da mutanen suka fada ya fara tabbata yasa ta fara jin tsoron.


Wayarta ta dauka ta kira amiyarta Hajiya Talatu, bugu daya ta dauka da far'arta, sai da suka gaisa sannan ta labarta mata halin da take ciki.


“Kin san me Hajiya? Mataki zamu dauka tun yanzu, waya sani ma ko wani hadin kai ne da ita Ammyn?”


Hajiya ta dan yi shiru tana nazari.


“To ni yanzu ya zanyi? Tsoro nake kar mu mata asiri ta tona mana asiri”


“Ai dole shi za'ayi idan ba haka ba taya zamu koreta a gidan? Dole sai da asirin nan”


“Kika sani ko abun da zai saka aikinmu ya wargaje kenan? Ni fa tsoro nake ji, ki samu lokaci ki shigo gobe mu yi shawara abun da ya kamata wannan maganar bata waya bace”


“To kenan Hajiya zan shigo gobe idan Allah ya kaimu”


Daga haka ta aje wayar, zuciyarta na raya mata yi ma Falmata asirin da zata bar gidan ta dayan bangaren kuma tana jin tsoron kar ya zama na ko tana da aljanu da za su tona mata asiri su fadi abun da tai. Mikewa tai tsaye ta fara safa da marwa, tunanin yadda zata bullowa lamarin take, wannan karon sai da ta kai karshen dakinta sai kuma ta juyo da sauri ta dauki wayarta number yarta ta lalabo ta aika mata kira, Jurry dake kwance saman gadonta ta mike tsaye tana kallon kiran mahaifiyarta.


“Hello Hajiya”


“Juwairiyya kina ina?”


“Dakina, lafiya dai”


“Dakina lafiya dai?”


“Ba lafiya ba, zo ki same ni yanzu nan”


“Okay”


Ta aje wayar tare da mikewa tsaye gaba daya ta fito daga dakinta ta nufi dakin mahaifiyarta, daf da zata shiga dakin Sirleem ya turo kofar falon ya shigo tufafinsa a jike shakaf da ruwa.


“Ya Sirleem ina ka fito haka?”


Ta tambaya ganin yadda ya jike bayan ta fi kowa sanin yayan nata baya son ruwan sama ya taba shi.


“Somewhere...”


Ya amsa mata ba tare da ya kalli inda take ba, ya nufi corridor da zai sada shi da dakinsa. Tsayawa kallonsa tai sai da ya shige sannan ta tura kofar dakin Hajiya Babba ta shiga. Bakin gado ta samu Hajiya zaune tana ta faman sauke ajiyar zuciya.


“Hajiya lafiya dai?”


“Ina fa Lafiya? Juwairiyya muna cikin matsala, abun da mutanen nan suka fada ya fara tabbata”


Jurry ta zauna tana yi ma mahaifiyarta kallon rashin fahimta.


“Ban gane ba...”


Sai da Hajiya ta tunasar da ita abun da bokan nan ya fada n cewar Falmata Fadime and Sardauna za su lalata musu shiri sannan ta dora da..


“Kuma yarinyar nan tana cikin gidan nan tana aiki, ita take rainon yaran Shattima...”


“Bakuwa ce amman ko?”


“Nima haka nake tunani bata dade da fara aikin ba”


“To yanzu ya kenan?”


“Mafita nake nema na rasa yadda zan yi, gana daya kaina ya kulle, tsoro nakr kar na shiga malamai ta tona min asiri ban sani ba ko tana da aljanu ne, gaba daya hankali ya kasa kwanciya, gashi a ba a bangaren nan take ba balle na koreta”


Hajiya ta karasa tana dauke numfashi kana ganinta kasan a tsora ce take sosai.


“Ko ba a nan take ba, zamu iya yin abun da zai saka a koreta mana”


“Me zamu yi me zamu yi Jurry ace mun saka ido akan yarinyar da bangarena take ba? Daga nan ai wani tsonon asirin ne kuma”


“Ni na san abun da zan yi Hajiya, yanzu yarinyar tana ina?”


“Tana bangaren Ammy zaki ganta wata baka haka bata ji sosai ba zata wuce sa'ar Nana ba”


“Bana shiga bangaren Ammy amman zan ganta gobe inshallah, na san abun da zan yi”


“Me zaki yi?”


“Na san me zan yi Hajiya ai ba komai ne za'a tsaya ace sai an yi asiri ba, sometimes we need to work with our brain”


“Kar ki yi abun da zai kara jefamu cikin matsala fa”


“Ki yarda da ni Hajiya bari dai, na fara ganin yarinya yanzu”


Hajiya ta sauke ajiyar zuciyata ba dan ta natsu da abun da Jurry take fada ba duk da bata san abun da zata aikata din


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login