Showing 108001 words to 111000 words out of 273152 words

Chapter 37 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72729

mu ne zamu shiga matsala, she's still young”


“Like a baby?”


Ta tambaya hawaye na sauko mata.


“Ina jin kamar ace Nana tana da wata uwar ba ni ba, da yanzu na maida ta hannun mahaifiyarta na gaji da wanne zan ji”


Ta fashe da kuka. Hakan yasa Shattima yaji damuwarsa ta karu, ya mike tsaye jiki ba kwari ya fice daga dakin domin ko kadan baya son jin kukan mahaifiyarsa. Dakin yaransa ya nufa or maybe zai samu peace of mind a can, Luma kadai ya samu a dakin tana ta bachi, kusa da ita ya zauna ya shafa fuskarta a hankali yadda ba zata tashi ba, sannan ya mike tsaye yana sauke ajiyar zuciya ya nufi gurin windows dakin wanda ke saiti da Garden din bangaren Ammy, tsaye yai jikin window yana kallon itacen dake garden din wani iska mai dadi yana bugunsa, hannayensa ya dora jikin window wanda hakan ya bashi damar hango Falmata dake zaune a garden din tana ta kallon wani gurin na dabam kamar mai tunani. A inda take tsaye na kasa baya iya hango na sama sai dai na sama ya hango na kasa.


Hango Sirleem da tai tafe yasa ta mike tsaye tana jiran ya karaso kusa da ita, tun daga nesa yake sakar mata murmushi har ya karaso.


“Naje daukarki Momy tace tasa Ameer ya kawo ki, na shiga bangarenku n karbi takardar maganin wata hadima tace min kina Garden”


“Eh ta bani maganin ma”


“Oh Momy akwai karamci sai da ta siya maganin ma”


Ya fada yana murmushi domin kadan daga halin Momy ne taimako da karamci ga tausayi da son mutane.


Ya kai hannu ya karbi maganin yana dubawa.


“Ta fada miki yadda za ki yi amfani da shi?”


“Eh ina son sai na je gida sai na fara idan zan kwanta”


“Amman dai yau ba zaki kai dare kamar jiya ba ko?”


“Sai yaran sun yi bachi tukuna”


Ya mika mata ledar maganin yana fadin.


“To ya kamata ki samu Mai Napep din da zai rika kai ki ya dawo dake, zan biya shi”


Kallonsa kawai take baki sake tana mamakin yadda yake da karamcin da son taimako har haka. Kamin tace komai yace.


“Ba ki ba ni labarinki ba fa”


Ta yi kasa da kanta, ba dan bata ji domin duk maganar da yake mata yan mata ne cikin daga muryar ta yadda zata ji, ba ita kadai ba har wanda ke kusa da su ma zai iya ji.


“Hey....”


Ya fada yana leken fuskarta. Sai ta dago ta kalleshi, ta sake maida kanta kasa.










HAJIYA BILKI POV.


Hajiya Bilki ta sauke ajiyar zuciya jin abun da Aminiyarta kuma matar Waziri wato Hajiya Talatu take fada.


“Wallahi kuwa”


“Ki ce kina cikin tashin hankali, to wai Waziri lafiya yake kuwa?”


“Ni ina na sani, sai wani fadar yake duk na sake yi ma dan da'uwansa kazafi a bakin aurena, ina zaman zamana zai dauko min wata masifar, wannan duk na Ammy na na sani, shi kuma baya iya musa mata tun da ta shanye shi, daga ni har Maijidda jiya ba mu runtsa ba, kuka kawai take”


“Ai dole tai kuka za akai ta ga halaka, yarinya tana zamanta za a aura mata mutuwa, Wallahi ki tashi tsaye karki yarda sam a kai ki a baro”


“Ai ba zan yarda ba, sai dai ayi wacce za ayi, amman ba zan Waziri ya aurawa Shattima yata ba, ko ana zaune kalar ai ba zan yarda ba balle kuma mutum ya zama maye, idan dama ta ki hagu zan koma, idan ta gwada be yarda ba be janye maganar ba, garin su mutanen nan zanje ayi masa asiri ya janye”


“Ai haka ya dace gaskiya, sai muje tare, kaji min tashin hankali”


“Wai sai fdar yake indai ba Shattima ya fasa ba Wallahi ba za a fasa auren ba, so yake yana aura masa ita ta mutu, waya sani ma ko Ammy ce take cinye masa mata, ko kuma can garin tsafe tsafensu suka kwaso wani mugun abu”


Hajiya ta dade tana magana da Hajiya Talatu kamin ta katse wayar shi M saboda shigowar Nana.




NANA POV.


Tana Fita daga dakin Ammy ta nufi bangaren Hajiya. Tana tura kofar dakin ta shiga sai Hajiya tai wa Hajiya Talatu sallama ta kalli Nana tana murmushi.


“Daughter”


“Na'am Hajiya dan Allah wayarki zaki ara min na kira driver na”


“To gashi”


Ta mika mata wayar, Nana ta kai hannu ta karba ta fice daga dakin tana nemo line AA call list din Hajiya domin bata yi saving number ba. Bugu daya ya dauka.


“Hello”


“Sardauna”


“Na'am”


“Ka shirya anjima da 8 ka zo ka kai ni gurin budar kan Amarya”


“Okay”


“Karka wuce 8pm”


“Okay”




**
Ya amsa mata tare da sauke wayar tare da saka ta aljihu sannan, ya marasa cikin gidan yana nade wandonsa.


“Anti wanki da yamman nan”


“To kayan sun yi datti, kai kuma ba zama kake ba”


Hannayensa ya jefa cikin ruwan ya soma taya ta wankin, daman can idan tana wanki ya kan taya ta ko kuma yai mata, kayan su Khaleel da Aymana duk shi yake wanke wa, har girma yana mata idan yan kwarai na saman kai, ko kuma ya mata rabin girkin ita kuma ta karasa. Sai da ya fara dauraye tufafin yana shanyawa sannan ya dauko mata wani labarin.


“Anti ina tunanin komawa makaranta fa”


“Makarantar lafiya? Ni ba ni da kudin biya maka makaranta yanzu, kai kuma ba aikin wahala kake so ba balle ka taimaki kanka”


“Ai wani aikin zan samu mai soka soon, zan gyara gidan nan na masa fenti na saka masa tayis na siyo miki gas, ke har makka sai na kai ki na siya miki mota, su Khaleet na saka su makarantar kudi, komai zai zama normal...”


Kallonsa tai.


“AA baka rabu da yarinyar nan ba ko? So kake ka jefa kanka a matsala ko?”


“Ni fa na rabu da ita bana tare da Ita sam sam sam”


“Ya dai kamata ace idan nai maka magana ka ji, idan na ce ka bari ka bari, ba ka da wanda ta fini a yanzu, baka da gata sai ni, kasan bamu da kowa sai Allah, idan ka shiga wani hali aka kama ban san ya zan yi ba, aje min wankina”


Ya kalleta a sanyeye.


“Ba maganar yarinyar nan ba ne Anti”


“Ni dai ka aje min wankina”


Ya cire hannunsa ganin da gaske take domin babu alamar wasa a maganar ta balle kuma a fuskarta. Wannan abun yake tsoro ya dade yana son labarta mata ko kuma sammata wani abu amman yana tsoron abun da zata fada, domin shi kansa ya san ba shi da gatan daya wuce Antinsa a yanzu, ita ce uwarsa ita ce ubansa ita ce komai nasa.


“Ka rika taka tsantsa da rayuwa AA, neman kudi ba hauka ba ne bana son ka jefa kanka a matsala, na rasa uwa n hakura, na rasa uba na hakura, na rasa miji na hakura, yanzu kam bana jin idan na rasa ka zan iya rayuwa, kai kadai ka rage min, ni ma ni kadai na rage maka, ya kamata ace idan na maka magana ka ji, ka san irin wahalar da muka sha kamin mu kawo yanzu, kasan irin fadi tashin da nai kamin na samu na gina kaina, muna zaune cikin rufin asiri kana kokarin jefa mu a hadari?”


“Idan akan yarinyar nan Allah ya min arziki, ba fa akanta ba ne”


Uffan Anti bata sake ce masa ba, ta san akanta ne tun da har yai ma kansa addu'ar arziki. Ganin yadda ranta ya bace yasa ya tashi ya nufi gindin murhu ya fara saka itace zai hura mata wuta.


“Karka kunna wutar nan”


“Girki zan dora miki”


“Ba mu da abun dafawa kwado zan yi”


Ya kai hannunsa ya taba aljihun wandonsa, yana da kudi amman ba damar ya bata tace ina ya samo ko kuma tace ba zata karba ba. Mikewa yai tsaye ya dawo bakin kofar dakinsa ya zauna yana kallonta, har ga Allah be jidadin yadda ya ga ranta ya bace ba, domin Anti Rabi ita ce a matsayin uwa a gareshi duk wani abu da uwa take yi ma da, Anti Rabi ce tai masa lokuta da dama zata hanawa yaranta abu ta bashi, babu abun da zai nema ta ki yi masa sai idan bata da hali


“Da kin aje wanki gobe na karasa miki”


Ta masa banza, sosai ranta ya bace ta san yadda AA yake da shegen son kudi, ba zai yi sata ba amman yadda ya lakewa yarinyar nan tana tsoro kar ya janyo musu abun da yafi karfinsu. Mikewa yai tsaye ya shige cikin dakinsa ya bude akwatinsa yana duba kayan da suka fi fitar da shi.


“Yarinyar nan ma da safe bata bar ni naje gidansu ba balle na kara samo wani abu”


Ya fada cikin jin haushi yana tuna kiran da tai masa dazu da safe ta sanar masa cewar ba zata je makaranta ba.






Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:50 - 🤐🤐🤐🤐: 30.


*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt bank, then send the evidence via 08036126660*


FADIME POV.


kamin su karaso ya Wasim ya kalli Fadime ya ce.


“Karki yi magana kuma komai aka baki karki ci”


Ta daga masa kai wasu hawaye masu zafi na sauko mata. Ganin hakan yasa ya kai hannunsa ya rika wuyan hannunta. Mutane na karaso kusa da shi suka risina masa alamar girmamawa.


"Erregeak zure ahoarekin ikusi behar du"


_Sarki na bukatar ganin tare da bakinka_


Be ce komai yaja hannun Fadime ya fita daga cikin runfar, Zainab na ganin haka ta bi bayansu da sauri, mutanen da suka zo kiransa suka rufa masa baya. Ta inda mutane suka fito ya nufa rike da hannun Fadime wanda ta kasa daina hawayen da take. Ta bayan wani guri wanda yafi kama da kasuwa suka bullo, duk inda Wasim ya dora kafarsa sai an risina masa an dauke ido daga barin kallonsa alamar girmamawa da biyaya. Sun yi tafiya mai dan nisa a kafa kamin su isa bakin wata babbar kofa ta itace an mata gate har da masu gadinta. Wasim na isowa gurim kofar aka bude masa suna risinawa har sai da ya wuce sannan suka tashi. Hakan yasa Fadime ta ji wani girma ya kamata, ko ba komai ta ci alfarmar Wasim ita ma an risina mata, a nan ta kara yarda babu wanda ya isa ya taba ba, kimar Wasim da sonsa suka kara ninkuwa a ranta. Shiga cikin gurin yasa daga Zainab har Fadime suka manta da abun da ya kawo su gurin, wata sabuwar duniya ce, kuma babbar daula mai zaman kanta, babu komai a dayan bangare sai katuwar gona mai cike da manyan itace wanda har baka iya hango cikinta saboda hudu, ta gafe daya kuma kana jin kwarar ruwa alamar akwai korama a gurin. An bi ko'ina na harabar an haska shi da wutar ice wanda hakan ya bawa Zainab da Fadime damar ganin irin kwaliyar da aka yi ma gurin da koren ganye mai yanayi da ganyen ayaba. Sai da suka isa gaban wata kofa sannan Wasim ya cire talkaminsa na fata, ya nasa kafarsa a gurin, Zainab da Fadime kan daman ba su shigo garin da talkami ba. Wata katuwar fada ce da aka shimfida mata gashin farar damisa, tun daga bakin kofar har zuwa inda Sarkin yake zaune kan wata kasaitacciyar kujera da zaka iya rantsewa ba itace ne aka saffara ba. Daga hannun kujerar har jikinta an masa kwaliya da farar azurfa. Ginin fadar kuma an masa kwaliya da fatar zaki inda Sarkin zai dora kafarsa da hannunsa ma kan Zaki ne a gurin. Tsirarun mutane ne a cikin fadar ciki har da Liya dake tsaye gefen Sarkin dake hakimce saman kujera fuska babu annuri.


Nan da nan jikin Fadime ya fara rawa, kafafauwanta suka fara lankwashewa kamar wata musaka. Nesa da Sarkin Wasim ya tsaya ya saki hannun Fadime ya risina da kafarsa daya ya dukarda kansa ya kwashi gaisuwa.


“Barka da wannan lokacin Shugaba”


Ya fada da yarensu, a maimakon Sarkin ya amsa masa sai wata tsohuwa ce mai bakin zane ta amsa masa tana takowa zuwa inda yake tare da jero masa tambayoyi.


“Su waye wannan Shugabana?”


Wasim ya mike tsaye da kyau yana kallon tsohuwar kamar ba zai amsa mata ba.


“Yan garin nan ne, be zama lallai ki san kowa a garin nan ba”


Ya amsa mata da yarensu, kamin Liya ta nuna Fadime data magana da yaren da su kadai suke ji.


“Na san wacan yarinyar, yana zuwa gurinta, a wani gari da yake yamma da garin nan...”


Fadime ta kara fito da idonta waje, duk da kasancewar bata san me Liya take fada ba amman nuna ta take, gashi ta ga Wasim ma a nan shi ya risina a maimakon a risina masa, take mararta ta kara cika da fitsari, hannunta ta kai ta bugu Wasim yana kallonta ta soma masa magana a cikin ranta.


“Fitsari nake ji fitsari”


Ta fada a ranta tana mutsika masa ido tana masa alamar yadda zai gane. Shi dai kam be fahimci komai ba hakan yasa ya maida hankalinsa gurin Liya.


“Ina magana tana magana saboda an daure mata ta yi yadda take so a masarauta, mi zai saka na fadi abun da ba shi ba a gaban Shugaba? Ya zama lallai sai kun san kowa a garin nan ba, amman lallai ne kowa ya san ku”


Ya fada da yarensu yana watsawa Liya wani mugun kallo. Hannu Sarki ya daga sai tsohuwar taja baya ta nufi wani guri daya fi kama da bukka a cikin fadar, bata dade ba ta fito rike da ture wanda ke dauke da soyayyen nama, ta mikawa Zainab.


“Ci”


Ta fada da yarensu, Zainab ta kai hannu ta dauki yanka daya da sauri ba dan ta san abunda ta fada ba, jiki na rawa ta kai bakinta ta tauna ta hade, daga lokacin ne gaban Liya ya fadi ganin ba tai komai ba. Tsohuwar ta matsa da naman kusa da Fadime.


“Ci”


Tana fadin haka Fadime ta kalli Wasim da sauri, sai ya amsawa tsohuwar da yarensu.


“Bata cin nama”


“Na yau ne kawai, kuma umarnin Shugaba ne, ci”


Ta karasa tana kallon Fadime, da sauri Fadime ta kai hannu ta dauki yanka daya tana kuka ta kai bakinta, bata ko tsaya tauna shi ba ta hadiye. A take ta ji wani abu ya taso mata tun daga cikin cikinta ya nufo makoshinta, wani irin kaikayin bala'i ne ta ji a makoshinta, daga Wasim har tsohuwar da Sarkin da Liya kallonta suke.


“Wacan ta mu ce wacan bare ce”


Tsohuwar ta fada tana nuna Fadime, tana yin baya-baya, wani irin ihu Fadime ta saka ta rike makoshin tana kuka.


“Wayyo kaikayi wayyo Allah kaikayi”


Da sauri Wasim ya maida ita bayansa, yana kallon Mahaifinsa, Zainab kam mutuwar tsaye tai a gurin ganin ita ta ci be mata komai ba, amman ga Fadime rike da makoshi wasu yawu masu yauki na mata zuba kamar kubewa sai kuka take tana wani irin tari, tana yagar wuyanta da yatsun hannunta. Murmushin jindadi ne ya fadada kansa a fuskar Liya tana kallon yadda Fadime ke tari tana susar wuya cike da shauki.


“Errugabea da, nire errua da ez dakiela ezer, tira egin nion”


“Bata da laifi, laifina ne bata san komai ba, ni na janyo ta”


Ya fada yana ta kokarin tare Fadime daga kallon da Sarkin ke mata. Hakan da yai kadai ya isa ya karantar da Sarkin cewar son ta yake.


“WASIM...!”


sarkin ya fada yana gyada kai a hankali tare da kara hade rai kamar bakin hadari, Fadime kam faduwa tai a gurin hankalinta na kokarin bacewa saboda kai kayin bala'i da take ji a makoshinta, Wasim ya duka da sauri ya rike ta. Zainab na tsaye a gurin tana shafa wuyanta ba dan tana jin komai ba sai dan tambayoyin da take da su.




NANA POV.


Wani irin murmushi take tana kallon kanta a madubi, ita kanta ta san ta yi kyau matuka red gown din dake jikinta ta haskata, daman can Nana ba mace ce mai son doguwar kwaliya ba, hoda ce kawai a fuskarta sai jan baki data shafa. Mikewa tai tsaye ta dauki purse dinta ta saka takalminta sannan ta nufi kofa tana takawa kamar wata Amarya. Ko da ta fito babu kowa a falon Ammy hakan kuma ba karamin dadi yai mata ba, sai ta nisa ta hanyar da Ammy take hana ta fita, da sauri sauri ta rika tafiyar gudun kar ta hadu da Ammy ta hana ta zuwa budan kan. Tana isa cikin fadar Ammy ta bude kofar ta baya ta fita. Daidai kofar AA ya faka motar, daman tun 7:40pm ya iso ya aika wata Hadima ta fada mata ya iso sai ta umarce hadimar ta fada masa ya dawo ta kofar fadar Ammy. AA na ganin Nana ya fito daga motar yai tsaye yana kallonta, gaba daya ta sake ta masa mugun kyau kamar ba ita ba, abun ka da marar jiki sai sigar ta kama jikinta kamar wata yar tsana. Ita kanta kallonsa take domin yayi kyau fiye da kullum ba zaka ganshi ka ce direba ba ne dan masu kasa haka ya fito. Murmushi ta sakar masa ganin yadda yake kallonta, sai shi ma ya mayar mata da murmushin ya bude mata gidan baya, saukowa tai a hankali


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login