Showing 210001 words to 213000 words out of 273152 words

Chapter 71 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72776

ruwan tai cikin bakinta da zimmar sha sai ta gagara hadewa tana zubawa a bakin suna dawo mata suna jika tufafinta.


“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Anty Karima zo..”


Kausar ta fada tana fashewa da kuka. Sai Hajiya ta kalleta irin duban nan na me ya faru? Is like kamar bata san ta yi ba. Karima ta karaso gurin da sauri tana kallon Hajiya.


“Me ya faru?”


“Ruwa na bata ta sha yadda ta sha haka yake dawowa a jikinta”


Kausar ta fada cikin kuka da tashin hankali.


“Innalillahi Hajiya”


Hajiya ta kalli Karima amman ta kasa amsawa.


“Taso mu je daki”


Karima ta rika hannunta sai Hajiya Babba ta mike tsaye kamar wata yar yarinya ta bi Karima zuwa dakinta, Karima ta zaunar da ita saman gadonta ta cire mata takalmin yayinda Kausar ta karbi jakarta ta da mayafinta ta aje a muhallinsu.


“Hajiya ki kwanta”


Da sauri Hajiya ta kwanta kamar mai jiran umarni. Karima ya fito cikin tashin hankali ta nufi dakinta ta dauko wayarta ta kira yar'uwarta Jurry ta fada mata abun da ya faru, cikin mintunan da ba su fi talatin ba Jurry ta iso gidan sai wani huci take tama fusata tana karawa.


“Haba ai dole Hajiya ki shiga wannan yanayin, yanzu fisabillahi Ya Sirleem da kansa zai dauki wuka ya daba miki? Da kansa zai jefe ki a wannan halin”


Jurry ta fada tana zaune kusa da Hajiya, Kausar kam sai rusar kuka take, Karima ce mai gaya ta ita ma tana hawaye.


“Wallahi Ya Sirleem be kyauta ba, yanzu ai ya ji dadi mahaifiyarsa tana cikin damuwa, ban san abun da suka gani a jikin yarinyar ba, kuma ko zai aureta ai ya kamata ya fadawa Hajiya ni na san ba zata hana shi ba”


Jurry ta juya ta kalli mahaifiyarta.


“Hajiya ta shi ki ji”


Hajiya ta tashi zaune kamar mai jiran umarni. Hakan da tai ba karamin mamaki ya ba yayanta ba.


“Hajiya karki sa wannan abun a ranki, ki kyale shi ki cire shi daga jerin yayanki, ki manta da rayuwarsa, ki na da mu kuma mun isheki da yardar Allah, na san dole za ki shiga damuwa ace danka ne zai maka haka”


Jurry ta fada hawaye na cika idonta, Hajiya ta kalleta har lokacin bata iya cewa komai bakin ya mata nauyi a gurin kalami, ko numfashi da ace ta baki take yinsa da bata samu damar fitar da shi ba.




FALMATA POV.


Karasawa tai gaban hoton ta kai hannu ta ta shafa fuskar matar da ke jikin hoton idanuwanta na cika da kwalla, sai kuma ta juyo tama karewa dakin kallo, can kuma ta sake maida dubanta gurin hoton hawaye na sauko mata, miya kawo hoton mahaifiyarta a nan? Ta tambayi kanta tambayar da bata da amsar ta, mikewa tai tsaye wanda hakan yai daidai da shigowar Momy a dakin cike da tunani kala, domin ta kasa natsuwa tana son ta ji abun da yake faruwa, hakan yasa ta zabi tambayar Falmata, domin zuciyarta na raya mata ba a daura auren ba Sirleem. Maida kofar dakin tai ta rufe da makulli. Falmata ta juyo tana kallonta hawaye na mata zuba.


“Wai me ya faru ne? Su waye za su zo da Sirleem yace idan sun zo kar na bada ke?”


Falmata ta nuna hoton mahaifiyarta tana hawaye.


“Waye kawo hoton nan a nan?”


Momy ta dan leka bayan Falmata ta hango hoton.


“Me ya faru?”


“Mahaifiyata ce”


“Ma ma..ma...Mahaifiyarki?”


“Mahaifiyarki?”


Momy ta sake maimaitawa.


“Duba hoton dai da kyau ki gani”


“Mama ta ce Momy, babu inda zan ga mahaifiyata ban gane ta ba, ni ma ina da irin hoto”


“Anya dai? Mahaifiyarki Falmata ko dai kamanni? Wannan ai Safiyya ce”


Falmata ta daga kai tana hawaye.


“Eh ita ce... Mamata ce”


Momy ta sake kallon Falmata da duba na mamaki da al'ajab.


“Wannan fa mahaifiyar Ameer ce... Dan mijina, wannna matar mijina ce ta biyu wanda ya aura tun da dadewa su ka rabu....”


Falmata ta lumshe ido hawaye na sauko mata. Momy ta karaso kusa da ita ta da fa kafadunta tana girgiza ta.


“Ta ya zan yarda da ke? Ta ya zan yarda mahaifiyarki ce?”


“Sunan da kika fadi sunanta ne, kuma ina da irin wacan hoton, mahaifiyata ta ce ta ba ni, ta ce tun tana budurwa ta dauki hoton, a lokacin da samari su ke bawa yan mata kudi su ce su je su yi hoto, ta fada min hoton guda gudu ne wanda ya saka ta dauki hoton mijinta ne na farko ya rike biyu ya bata biyu, kuma tabbas mahaifiyata ta auri wani namijin kamin ta auri Babana, har ta haifi yara biyu da shi mace da namiji macen Maryam da sai namijin Usman wanda ya bata, Maryam din kuma ta rasu...”


Falmata ta fada idonta a rufe cikin kuka mai karfi, lokaci daya Momy ta dauke hannayenta daga jikin Falmata tai baya baya tana kallonta kamar wanda tai arba da wani abun tsoro, tabbas abubuwan da Falmata ta fada haka ne, domin mijinta ya fada mata ya haifi yara biyu da ita dayar ta rasu kuma sunanta Maryam kuma ya fadawa Ameer yadda aka dauki hoton a lokacin da Ameer yake tambayarsa wacece ta jikin hoton da mahaifinsa ya ba Momy yace ta aje masa, sanadin hakan yai kai aka kara gyara masa hoton aka maida shi babba ya saka a dakinsa.


“Hakan na nufin ke da Ameer ....”


Momy ta kasa karasawa sai nuna Falmata take, jin hakan ya sa Falmata ta bude idonta da su kai ja saboda kuka ta kalli Momy.


“Wane Ameer din?”


“Dan...dan...mijina... Allah sarki Ameer... Ashe baka da rabon ganin mahaifiyarka a fili?”


Falmata ta dafa zuciyarta tana tuna waye Ameer din, the first thing da ya fara zuwa mata after tuna shi shi ne lokacin da zai je makaranta ita kuma Sirleem ya shigo da ita cikin gidan, irin maganar da yai mata da kuma yadda ya labarta mata batan mahaifiyarsa da fatan ganinta da yake. Sauri daga kai tai tana kallon katon hotonsa da ke manne a bango ta saka dayan hannu ta rufe bakinta da sauri hawaye na sauko mata. Momy ma hawayen take sai ta juya dafe da zuciyarta ta fice daga dakin, Falmata kan kurawa hotonsa ido tai sosai yayi murmushi yana sanye da suit red, sai a yanzu take ganin kamanin mahaifiyarta a fuskarsa da bakin fatarsa wanda ita ma shi ya haska fatarta.


Tana tsaye a dakin Sirleem ya shigo, yadda yake tafiya kadai da yanayin fuskarsa ya isa ya sanar maka cewar a yau kam ya amsa sunansa na maraya. Karaso yai kusa da Falmata ya saka hannayensa ya jata jikinsa ya rumgume, sai ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi jikinta na karkarwa, abubuwa biyu sun zo mata a lokaci daya, shi ma lumshe ido yai yana maida numfashi a hankali sai hawaye masu zafi suka sauko masa.




IYA POV.


Ganin tai kamar be kamata ta aikatawar da wannan aikin a yanzu ba, bata da tabbacin burinta zai cika ko aa, idan har Shattima be auri Zainab ba ko da ya zama sarki aikin banza ne a gurinta domin ba zata mori komai ba gashi yanzu ma ta bar gidan.
Daukar zare tai ta nade kurwar ta dukawa ta maida kurwar cikin kwaryar ta sannan ta maida kwaryar karkashin gado, ta gyara komai yadda yake, kana ta dauki kuwarwar Maijidda ta fito da ita daga dakin, kicin ta shiga ta dauko wata robar ta saka ta tabarar a ciki ta fara fige gashin jikin tantabarar da hanunta, bayan ta gama ta kunna risho domin ta fi gane yin girki da shi sama da gas.
Sai da ta yanka naman tantabarar sannan ta zuba shi a tukunya ta zuba mai kadan ta dora tukunyar a risho, bayan yayi zafi ta soma soyawa, sai da ta soye abun ta rumus yadda take son naman sannan ta kwashe ta sauke tukunyar ta kashe rishon ta dauko namanta ta zuba a wata kula ta rufe ta dawo dakinta ta boyeshi a karkashin gado. Sannan ta koma kicin din ta juye man da tai soyar da shi a wani karamin roba ta gyara kicin din ta wanke komai kamar bata taba ba. Kwankwasar kofar falon da ta ji ana yi ne yasa tai saurin fitowa daga kicin din ta je dakinta ta boye man sannan ta fito ta bude kofar, ganin Zainab ba karamin mamaki tai ba.


“Kin dawo kuma?”


Zainab bata ce mata komai ba ta raba gefenta ta wuce cikin falon, Iya ta rufe kofar ta juyo tana fadin.


“Ya akai wai miyasa ya aka rike ki?”


Sai da Zainab ta isa bakin kofar dakinta sannan ta juyo ta kalli Iya a jigace.


“Saboda ke ne, duk abun da ya faru da halin da na ke ciki saboda ke ne Iya, saboda zargin da Shattima yake yi akan mu ya rufe mu a dakin horo, dakin da ko dabba ba zata iya zama a ciki ba, haka na kwana cikin sauro babu abun shimfida balle na rufi, ban taba tunanin zan wulakanta kamar haka ba, ban taba tunani wata rana zata zo da rayuwa zata zame min haka ba, a yau na yi nadamar haihuwata da kika yi, ba ni da dangi, ba ni da kowa ba uba, ga uwa ta zame min wata kala, da wanne zan ji?”


“Ce masa akai ke kika dauki yarinyar nan?”


Zainab ta share hawayenta ba tare da tace komai ba ta wuce dakinta wasu hawayen na sauko mata. Ko kadan Iya bata jidadin abun da Shattima yai ma yarsa ta, cikin bacin rai da tunanin irin abun da za ta yi masa ta shiga nata dakin ta zauna bakin gado tana mamakin yadda Shattima da kansa zai taba mata ya, duk abun da take yi bata taba tunanin taba shi ba, bata taba tunanin yi masa komai ba sai dai taba matansa ko yaya saboda tana masa fatan samun Zainab amman a yanzu ta kaita karshe shi da Ammy, domin a yadda ta fahimta abu ne mai wahala wata mu'alama mai karfi ma ta sake shiga tsakanin Zainab da Shattima, ita kuma a yanzu zama a masarauta yayi mata wahala, ba m masarautar ba har mutanen cikinta a yanzu dole wadanda suka san sirrinta su yi mesa da ita, hakan na nufi ita da Zainab din ba su da makoma. Sauko tai kasa ta zauna ta janyo kular namanta ta bude ta fara ci.


“Shegiyar kurwa ko mai babu”


Ta fada tana cin nama cike da jin haushi, bata tashi ba sai da tai ma naman kat ta cinye komai..






HAJIYA TALATU POV.


Maijidda ta shari bachi iya bachi bata barka ba sai kusan asuba, kamin ayi sallah ta shiga bandakin dake asibitin tai fitsari tai alwala ta fito ta zauna bakin gadonta. Hajiya Talatu sai murmushi take mata tana jindadin lafiyar da ta samu duk kuwa da kasancewar bata da wani sukuni sosai.


“Ya jikin na ki?”


“Alhamdullah na ji sauki”


“Allah kara lafiya, ni ai da farko na tsorata sosai Wallahi, ko da muka kawo ki asbitin nan ba ki san inda kan ki yake ba”


Ta dan yi murmushi tana kallon yatsun hannunta. Hajiya Talatu da kanta ta tashi ta hada mata tea da kayan tea da aka kawo mata tun da dare, ka dan ta sha ta zauna jiran sallati, ana yin kira ta karbi hijabin Hajiya Talatu ta saka ta gabatar da sallah azuba, bayan ta gama ta mikawa Hajiya Talatu sai ita ma ta gabatar da tata sallah. Misalin takwas aka kawo musu abun karyawa, a nan Hajiya ce tai hidimar zuba mata ta bata a plate sai tea a wani karamin kofi ta mika mata. Gaba daya sai ta Maijidda ta ji komai ya fita a ranta dan kwan kawai ta ci ta sha ruwan shayi kadan ta aje.


“Lafiya? Ko wani abun kike so a girka miki”


Hajiya Talatu ta tambaya


“Aa bana jin cin abinci ne, jikina ina jinsa kamar ba nawa ba”


“Ciwo kike ji?”


“Bana jin ciwo komai kawai dai ina ta jin wani yanayi na dabam”


Hajiya Talatu ta aje kofin shayin da ke hannunta.


“Kamar ya?”


“Ban san ya zan misalta ba, ina ta jin kewarku Momy, ina ta jin kamar zan tafi na barku”


Ta fada idonta na cika da hawaye har wani ya fara sauko mata, bata taba jin irin yanayin da take ji a yanzu ba bata taba jin kewar kowa kamar yanzu ba, gashi ta rasa yadda zata misalta yanayin da shi ba na ciwo ba ba kuma na lafiya ba, ba na dadi ba ba kuma na bakinciki ba.


“Kin gani Jidda bana son maganganun nan na banza, daga ciwo sai ki fara wani zancen mutuwa wane irin magana ne wannan dan Allah?”


“Wallahi Momy ina jin wani yanayi na dabam, ni dai dan Allah ki yafe min ko da na mutu”


“Ba ma za ki mutu ba, sai kin yi aure kin haifi yayanki na gani da yardar Allah, Allah dai ya baki lafiya ya yaye miki ko minenen”


“Ameen”


Ta amsa tana kwantawa saman gadon sai kallon dakin take, ta yi shiru kamar ba ita ba, motsin ac da hayaniyar mutane da take ji a waje sai ya zo mata a wani yanayi na dabam, can kuma ta juyo ta kurawa Hajiya Talatu ido tana ta kallonta irin kallon na bankwana, irin kallon nan da kake ji kamar kar ka tafi ta bar komai na ka. Hajiya Talatu kam hankali ya tafi gurin wayar da take sai dariya take.
Misalin 9am da yan mintuna Hajiya Talatu ta fita waje saboda masu gyara dakin da suka shigo su yi mopping, kamar fitar Hajiya Talatu ake jira sai wani bachi mai dadi ya fara kewayar Maijidda tun tana hamma har ta fara jin jikinta ya zama very weak ko hannunta ta gagara dagawa, nan da nan bachi yai gaba da ita bachin da babu farkawa, bachinta na karshe a idan duniya, bachin daga shi zata farka ta ji a dakinta na gaskiya.
Mai shara ta yi tai gama tai mopping ta fita ta rufe dakin, Hajiya Talatu bata dawo dakin ba sai da Haroon ya shigo tare kanwarsa.


“Bachi take”


Hajiya Talatu ta fada ganin tana jan numfashi tana maidawa a hankali, har zata tashe ta sai Haroon ya hana ta.


“Ki kyaleta kawai idan na shigo anjima sai na dubata”


“Tau ba matsala”


Sama sama su kai fira da Hajiya sannan ya fice ya bar kanwarsa Hajiya na Fadin.


“Allah yasa da sun zo su sallame mu, tun da tace jikinta ba ya mata ciwo komai yanzu zaman Asibiti ba dadi”


Ta fada tana gyara zamanta, wani irin zabura Maijidda tai daga cikin bachin da take ta matse hannunta tai wani abu kamar zata tuma sama daga kwance da take sai kuma tai lamooooo babu motsi.


“Subhanallahi jidda”


Hajiya Talatu ta fada tana mikewa tsaye ta isa gaban Maijidda din, hannu ta kai ta taba ta tana kokarin tashinta.


“Jidda Jidda...”


Haka Hajiya Talatu tai ta kiranta tana motsata, amman bata motsa ba, kuma ba ta amsa kiran ba, sai Hajiya Talatu ta kwantar da kanta jikin Maijidda tana sauraren numfashinta. Nan ma bata ji alamum tana numfashi a razane ta dago tana kallon Afra.


“Afra je ki kira likita yi sauri”


Sai tai rasa akan gaba domin tana rufe baki, likita ya turo kofar dakin ya shigo tare da nurse yana dariya da alama wata maganar suke. Tsakanin Hajiya Talatu da Afra sai ka rasa wane ya fi saurin sanarwa likitan abun da yake faruwa, da sauri likitan ya karasa inda Maijidda take kwance yana dubata, fita yai da sauri ya kira wasu likitocin biyu suka shigo cikin hanzari suka hau bata taimakon gaggawa amman ina mai kira yayi kira rai yai halinsa Maijidda ta bakunci lahira...
Dayan likitan ne ya fitar da Hajiya Talatu waje ita da Afra, sai ta tsaya bakin kofar tana kuka hankalinta a tashe, gaba daya ta rasa abun yi ko zama ta gagara yi. Bayan wadansu mintuna likitoncin suka fito ko wanensu fuska babu annuri hakan ya sanarwa Hajiya da Afra cewar sun rasa Maijidda rashi na har abada, Maijidda ta yi bachi da babu farkawa a duniya, ta tafi inda ko wane mai rai ke tsumayin zuwa.


“Hajiya... Ku yi hakuri”


“Ban gane na yi hakuri ba likita kamar ya na yi hakuri? Me kake nufi?”


Ta tambaya cikin kukan tun kan a sanar mata.


“Hajiya kin san duk mai rai mamaci ne, ki yi hakuri Allah ya karbi abarsa”


“La'ilaha illahu innalillahi, wayyo ni Allah na Maijidda”


Cikin wani irin fitar hayyaci da ihu da kururuwa Hajiya Talatu ke fadar hakan ta nufi dakin da Maijidda take ciki sai likitan ya riketa, Afra kuma ta zube a gurin tana ta borin iska, aljanunta na son tashin.






FADIME POV.


Misalin sha biyu na rana direban Mama Fulani ya isa da Fadime asibitin da Muhseen ke aiki. A harabar asbitin ya fara motar sannan ya fito ya zagayon bangaren da Fadime take ya bude mata ya rika hannunta ta fito, sannan ya rufe motar yaja ta su kai gaba, ita dai tafiya kawai take tana sauraren hayaniya da kuma irin hanyar da suke bi, idan ta ji wani tunanin zai zo mata sai tai saurin kawar da shi.


“Kai dan Allah duk kana ganin mutanen nan?”


Direban ya kalleta sai ya ji tausayinta ya kamashi sanin cewar bata ganin komai, a lokacin ne ya gane lalli ga ni da ji wani babban ni'imace da Allah ke ma bayinsa.


“ina gani diyata”


Sai tai shiru ta cigaba da saurare tana ayyana yadda surar kowa take a ranta, a haka har suka shiga office din da Muhseen din yake. Ba su tararda shi cikin ba hakan yasa dole sai da suka dan jira ya dawo.


“Sai yanzu tun dazun na ke ta jira fa, likitan ma ya kusan tashi”


Muhseen din ya fada yana karasa gaban teburinsa.


“Ina kwana?”


Fadime ta fada sai ya wara ido da mamaki.


“Wow gaisuwa dai?”


“Eh ita wannan da kace mamata ce ita ce tace na rika gaishe da mutane, wanda ka ce dan'uwana ne ya zo tace na gaishe shi, kuma na gaishe da matarsa duk na gaishe su, tace ina kwana ake cewa da safe da rana ina wuni...”


Kai tsaye ta labarta masa wannan tana kallon saitin inda yake tsaye kamar tana ganinsa, kara bude ido yai da mamaki, sai ya ji ta burgeshi. Ya kalli direban


“Am za ka iya tafiya, idan an gama zan maida ita gida ko na kira ka kawo ka dauke ta”


“To ranka ya dade”


Direban ya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login