Showing 249001 words to 252000 words out of 273152 words

Chapter 84 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72763

tuno da zancen dazun cewar Shattima zai yi aure, take ta koma ruwa tana kukanta kadan kadan ta yadda babu wanda zai ji. Inna ba ta fadawa Bappa komai ba har sai da dare ya raba ta tabbatar a lokacin Fadime ta yi bachi sannan ta labarta masa yadda sukai da Fadime dazun. Bappa yayi murmushi.


“Ai hakan da tai ya taimaka mana, ina tabbatar miki da ace ta san da maganar nan da yanzu an yi garkuwa da mu ance mu kawo kudi, amman a haka sai ya taimaka mana babu wanda ya sani sai dai kwatsan su ji an yi ma Fulani amre”


“Ai haka yafi, daman magana ta yi yawa akanta sai fadar ake bata da miji, ai Wallahi hakan ya min dadi Allah ya bata miji ba karami ba, dan babba mutum kuma babban mutum mai mutunci”


Bappa yayi murmushi jin dadi yana jin wata kima na kama shi zai yi sakuta da sarki.


FALMATA POV.


Hannunsa na lakkame da wuyanta tana karanta masa abun da ta rubuta.


“Mamana, Babana Kakana”


Ya saka yatsansa ya ja kumatunta na dama.


“Ina mijina?”


Ta yi dariya sai ta kalleshi.


“Mantawa na yi”


Yatsan nasa ya saka mata a baki ta fara tsasa kamar sweet.


“Yanzu ki rubuta sunanyen mutanen kuma ki manta da mijinki? Teem Teem?”


Ta yi shiru tana murmushin da har dimple dinta ke lasawa saboda yadda ta samu guri in 3 months jikinta ya fara kyau, daman can abinci mai kyau ne babu da kuma kwanciya hankali.


“Zan rubuta fa sai aka kira sallah shi ne na tafi sallah sai ka dawo”


Ya kai bakinsa saitin kunnensa.


“Ban san ki da karya ba”


Ta saka hannayenta ta rufe fuskarta, sai yai murmushi ya kai hancinss yana shinshinar gashin kanta da ya sha gyara sai kamshi yake.


“Karki sake bari a taba kiki kai, bana son mace da kitso, gashi yana kara min sonki”


“Kai ma karka sake yin aski”


Ya fada tana jin kamar ta kai hannu ta taba shi kuma tana jin kunyarsa har yanzu, shi din ne baya jin kunyar yi mata komai ko kuma yin komai a gabanta.


“Sirleem”


Dayan hannunsa ya saka ya buge mata baki a hankali ta yadda ba zata ji ciwo ba.


“Ban ce ki daina kirana haka ba?”


Dariya tai tana jin kunyar kiransa da sunan da ya rada ma kansa a kanta.


“To Baby...”


Ya amsa daker yana kai wannan karon halshensa ya kai gurin wuyanta yana mata zirya da shi.


“Hmmm”


“Dan Allah Baby, yaushe zan tafi gida?”


“Ba yanzu ba Babyn baby, sai kin shekara”


Ta dan bata rai, domin har ga Allah tana son fitar amman ya hanata kullum sai yace mata sai ta shekara.


“Dan Allah fa”


Ta fada a shagwabe kamar ba ita ba, sai ya dago yana kallonta fuskarta da kadan ya rage hancinta ya taba nasa.


“Idan kin je gida me zaki yi? You know i hate wannan matar dai ko?”


“Ai ba ita zan je gani ba, Babana”


Bakinsa ya saka ya tsose cinin hancinta tass sannan ya dauke bakinsa yana maida numfashi.


“Da dare zan kai ki ganshi, ni kaina ina son na kyautata masa amman wannan matar ke bata min rai, ta fa wahalar min dake, and ji yadda tai ma dan'uwanki”


Falmata ta kalleshi da sauri domin ta san bata taba labarta masa cewar Ameer dan'uwanta ba ne, kuma bata ce masa Tumba ta yi masa asiri ba.


“Wa ne dan'uwana?”


Hannunsa ya saka cikin rigarta yana shafa cikinta.


“Ameer mana, Momy ta fada min komai, kuma the way da take ba ni labarin kana ji kasan asiri akai masa, ta ya mutum zai gudu ya bar uwarsa kuma ya kasa nemanta, i wonder ya zai ji idan ya sani”


Falmata ta yi shiru tana tunani.


“Allah sai ya mana shari'a da matar nan, ta cutar da mu sosai”


“Har kike son ki je ganinta”


“Ba saboda ita zan je ba saboda Baba, komai yai min ai shi Babana ne”


Ya kwaikwayi muryarta har da wani juya kai kamar mace.


“To masu Baba zamu je anjima mu gaisheshi, daga nan sai Tumbin ta gan ni ko ya za ta yi?”


Ta yi dariya.


“Zata ce ya akai ka zama yaro, kuma Sirleem, mawaki”


Ya shafa kansa tare da cire hannunsa a jikinta ya mike tsaye.


“Da ne ai wannan, yanzu kuma mu da waka sai dai kallo, Hajiya ta hana kuma na hanu”


Ya nufi upstairs ta bishi da kallo.


“Ba cewa kai makarantar zaka je ba?”


“Wasa na ke miki, wane irin karatu yanzu ina cin amarci? Ki dai iya wanda nake koya miki idan kin haihu sai na saka ki wacan din”


Ta mike tsaye.


“Haihuwa kuma”


Sai ya juyo yana kallonta.


“Yes... Ko ba ki san kina da ciki ba?”


“Ba ni da ciki Wallahi”


“Ki daina rantsuwa ni na san abun da na yi, yan mata fresh irinki suna saurin daukar ciki idan sun hadu da mazaje irin Jaruman nan na gaske, kuma na san abun da na ke yi kullum Hajiyata”


“Ni ban gane ba”


Yayi dariya tare da juyawa ya cigaba da hawa stairs din.


“Anjima zan ganar dake Babyn Baby”


Da kallo ta bishi har ya haye sama sannan ta kai hannu ta taba cikinta.
As he said sai da dare suka shirya daga shi har ita cikin tufafi mai tsada shi yana sanye da shadda sky blue ita kuma lace ja sai mayafinta sky blue, ba karamin kyau tai ba ko ranar da aka kawota gidansa ba tai kyau kamar na yau ba, tufafin jikinta kadai sun isar da kyaut balle kuma kwaliyar da ta sha kamar wanda zata tafi gurin biki. Yana zaune falo yana waya ta soma saukowa da talkamin yan kwakwasa sai amsa amo suke na daukar hankali, dagowa yai yana kallonta sai gashi ya mike tsaye yana kokarin yanke wayar da yake.


“Fadil za su sake kiranka”


Ya katse wayar yana kallonta cike da so da kauna, kusan kullum kara kyau take masa.


“Wow Babyn Baby kin duba madubi kuwa? I swear kin yi kyau over”


Ta yi murmushi, kamin ta karasa saukowa ya iso ya daga ta sama yana juyawa.


“I love this girl, look at you ga pretty face, and heart of gold, ga beauty skin, kai Alhamdulillah”


Ta yi dariyar da ta bayyana hakoranta. Sai ya mika mata bakinsa.


“Kiss me kiss me”


Ya duko bakinsa ta saka cikin nasa, sai da ya tsotse bakinta sannan sauketa ya rumgume.


“Sweet lips”


Runtse idonta tai yana jin kunyar abun da tai, duk da kasancewar ya kusan zame mata jiki, domin kullum sai yayi kissing dinta at any time any how kuma yace shi ma tai masa. Wayarsa ya ciro ya juyo da ita ya soma daukarsu hoto.


“Mu fa komai ba mu yi ba, ko dan pre-wedding pictures din nan da ake ba mu yi ba, ba dan ma gurin bikin kamfanin mu na sanar ke a matsayin matata ba da har yanzu wasu ba su san na yi aure ba”


“Ai pre-wedding ba shi da kyau a musulunci”


Ta fada sai ya sumbancin kumatunta.


“To ya Sayyada”


Be yarda ta taka ta kafarta zuwa gurin motar ba, daukarta yai har gurin motar ta bude mata ta shiga sannan ya zagaya dayan side din ya shiga, be yi ma motar key ba har sai da ya saka yatsunsa cikin nata ya rike hannunta sannan ya fara tukin. Kamin su isa gida ya biya ta gurin wani katon shopping mall mai tsada na manyan attajirai yai ma Baba siyayya turare sannan ya dawo cikin motar ya sake rike hannunsa suka kama hanyar, kamin su isa sai ta rika jinta a wani yanayi na daban, wai ita ce zata je ganin gida daga gidan mijinta kuma tare da mijinta, so all her sad story ya zama story yanzu, take ta ji idonta ya cika da kwalla saboda canjin da Allah yai mata bayan dubun hakuri da wahalar da ta sha. A hankali ta kalli Sirleem sai shi ma ya kalleta sai turo mata bakinsa yai.


“Kiss me Kiss me”


Hannu ta kai ta buge bakin a hankali sai yai dariya ya kai hannunta saitin bakinsa yai kissing din hannun. Saboda yanayin unguwar yasa yai bakin waje ya dauko glass dinsa ya saka so that yayi badda sau, sannan ya bude motar ya fita ya zagaya bangaren Falmata ya bude mata ta fito, yai saka ma motar lock suka nufi hanyar da zata sada su da gidan yana rike da ledar turarun da ya siyowa Baba. A lokacin da suka isa bakin kofar gidan sai ya tsaya daga waje har sai da tai sallama ta fara shiga sannan ya shigo yana sallama da karewa gidan kallo.
Tumba na zaune bakin kofar dakinta rike da sandar da take dafawa idan zata tashi ko tai tafiya, sakamakon cirewar da kafarta tai sanadiyar natsarin da tai, ba a maida kafar ba saboda jijiyoyin su tsinke, daurin da akai nata a hannu ma ya kumbura sai ruwa yake mata, satin da daya asibiti ta dawo gida saboda babu kudin magani, a lokacin da ta dawo gida sai yan bani na iya suka rika duba mata ciwon suna kara janyo mata aiki, bayan ayi daurin aka dade ba a duba ba ko da aka kwance sai aka ga ya fara ruwa daurin ya lalace, haka nan dai da karfin hali da taimako aka koma da ita asibitin aka sake mata wani nan ma ba a dace ba, ta sake dawowa gida tana jinya, jikin nan nata duk ya zube ciwon ya janyeta har wani tsufan wahala ya taso mata.
Akwai hasken farin wata ga kuma gulof kasancewar akwai nepa amman hakan be wadatar da ita ba sai da ta dauki touch light dinta ta haska Falmata domin tantancewa.


“Falmata ke din ce da gaske?”


Tumba ta tambaya tun kamin Falmata ta karaso inda take.


“Na'am Umma ina wuni”


Ta tabe baki tana jin wani irin bakinciki ganinta cikin shiga mai kyau ga jikinta ma ya fara kyau.


“Hmmm ashe kina tunawa da ni? Ai mutunci da karamci be ce haka fa Falmata, saboda ba ni na haife ki ba, shiyasa kika ji zuwa ganina asibiti ko? Sai yanzu za ki dauko kafa ki taho dan ba ki da kunya, wato tun da mun aura miki tsoho mai nera kina can kina kwantawa a gado mai kyau kina yadda kike so sai ki watsar da mu”


Kamin Falmata ta yi magana Sirleem dake tsaye ya ce.


“Yanzu ma Baba muka zo gani, ina fatar yana nan”


Falmata ta kalleshi da sauri jin abun da ya fada, Tumba kuma ta sake daukar fitilarta ta haske shi.


“Wanene wannan? Kanen mijinki ne ko dansa?”


Falmata ta kalleshi sannan ta kalli Tumba ta ce.


“Mijina ne”


“Wannan...?”


Tumba ta tambaya da karfi har zawo na kubuce mata, ta sake haska fuskarsa da sauri tana ganin kamar ta taba ganinsa.


“Ke Falmata kalli fa wannan ki gani, mu da muka aura miki tsoro? Na shiga uku ko aljani ne dai”


Cewar Tumba sai wani maida numfashi take cikinta na murdawa.


“Wallahi mijina ne Umma shi ne kuka aura min”


Falmata ta fada, tana kallon Naja da ta shigo gidan da sallama, at first kallon mamaki ta fara yi ma Falmata, sai Sirleem ya cire glass din idonsa so. that Tumba dake haska shi ta tantance ko waye. Naja na kallom Sirleem dake tsaye tai baya baya, bata san lokacin da ta daka tsalle ta daki kirji tana fiddo.


“Umma Sirleem Sirleem M2 Wayyo na shiga uku Wallahi Sirleem M2”


Ya fada cikin rikicewa mai kama da hauka ganin celebratie a fili kuma a cikin gidansu, abun da ba ta taba tsammani ba.




_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:59 - 🤐🤐🤐🤐: *Khadeeja Candy*


*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


A harabar makaranta yake tsaye, yana sanye da bakin wando sai rd T-shirt da black shoes, a saman T-shirt din ya dora rigarsa sanyi irin mai kaurin an hannunsa sanye da safa kansa ma sanye hula, waya ce makalle a kunnensa sai faman murmushi yake kana ganinsa ka san yana cikin farinciki.


“Yanzu kun yarda ku yi a Yola kenan?”


“Eh dolen mu ai, because most of us iyayenmu ba su yarda ayi a Abuja ba”


“Good hakan ya fi duk da na san kuna da family a can amman dai kara komai ayi a gaban iyaye”


“To yanzu ai karatu zanje India a gabansu zan yi?”


“Wannan yana da banbanci, kuma idan sun barki kin je hakan na nufin sun yarda da ke kenan kuma hakan ba zai baki dama ki yi rayuwar da kike so ba, kuma ita fatar ba za ki ba mu kunya ba”


Ta yi murmushi yana juyawa saman gadon da take.


“Zan yi karatu sosai, kuma ba zan yi wani abu da zai tsaba tarbiyarta ba, ba zan ba ku kunya ba”


“Thank You”


“Ur Welcome”


“Bari na barki yi bachi saboda na san nan dare ne ko? Nan kuma rana”


“Yeah 1am ma ta kusa”


“Oh Wow kai ki kwanta kar Ammy ta ji kina waya da ni”


“To sai miye ai ta san muna waya, ta san ina kiranka ai kuma kana kirana”


“Yeah zata san muna gaisawa ai”


“Gaisawa kawai?”


Yayi murmushi.


“Yeah gaisawa kawai, domin bana jin idan ta san akwai wani abu a tsakaninmu zata bar mu mu cigaba da mu'amala”


“Saboda me?”


“Saboda yanayin rayuwata da taki ba daya ba ne, mu'amalarmu ma ba daya ba matsayinki yana da nisa da ni, kuma kina sama da ni sosai a komai n rayuwa idan aka cire shekaru”


“Shikenan?”


“Yeah”


“Hmmmmmm sai da safe”


“Goodnight...”


Sweetheart, ya karasa a zuciyarsa sannan a sauke wayar yana kallon hotonsa dake screen din wayarsa, babban yatsansa ya saka yana shafa screen din sannan ya daga kansa yana karewa makarantar kallo, ya sauke ajiyar zuciya yana murmushin wai shi ne yau a uk yana karatu cikin turawa abun da be taba mafarki ba. Duk iya fatan samun kudin da yake da misalin arzikin da yake karatunsa da burinsa a Nigeria ne, but look at him a kasar waje da sunan karatu karatun da zai inganta rayuwarsa. Tafiya ya fara yi yana tuna yadda rayuwa ta kasance musu before now, but komai ya canja cikin kankan ne lokaci.


“Arziki kashi...”


Ya furta yana kara yarda da kalmar nan da hausawa kr cewa idan Allah ta so ka tsinuwa zai baka, kuma dare daya Allah kan yi bature, lokuta ta dama ta inda baka yi tsammanin abu ba yake zo maka, domin be taba tunanin sanadin Nana zai samu haka ba, a iya tunaninsa zai samu yan kudaden a hannunta ne sai ya taimaki kansa da yar'uwarsa sai ga shi sanadinta an masa komai kuma an yi ma yar'uwarsa, farinciki na farko da ba zai manta da shi ba shine kudin da Shattima ya saka masa a account one million, a daren ranar kasa bachi yai yana ta ganin kamar karya ne one million in his account! Shi da ko 100k be tana ajewa a ciki ba, dai gashi an masa kyautar 1m. Daman tun da Nana ta fada masa ya tura account din yakr rike da wayarsa ko kara yaji sai ya duba sai ya ga sakon mtn, kudin be shigo account dinsa ba the following day, a ranar kasa yadda yai a farke yake, ya tisa Anty a gaba wai ta mare shi ko zai yarda.


“Wane irin mari kuma?”


“Dan girman Allah ki mare ni Anty”


Anty tai tsaye tana masa kallon mamaki.


“Sardauna ince dai ba wani abu ka sha ba?”


“Ni dai ki mare ni dan Allah”


Shiru Anty tai tana kallonsa kamin ta matsa baya.


“Gaskiya akwai abun da yake damunka Sardauna”


“Kai Anty dan Allah ki mare ni”


Ganin ba marinsa za tai ba yasa ya juya kamar zai fita sai kuma ya juyo.


“Anty yau yau ce? Ba mafarki na ke ba? Shiyasa na ke son ki mareni na tantance”


Anty na jin haka ta san kudin ne suka iso domin ta san da labarin izuwarsu, sai ta matsa kusa da shi ya ware hannunta iyakar karfinta ta zabgamar mari mai dan karen zafi, har sai da yaji wani shockin kamar na wutar lantarki, a nan kam ya yarda ba mafarki yake ba gaskiya domin da mafarki ne da yanzu ya farka.


“Na rantse da Allah da abokina ne yai min wannan marin yau sai mun yi dambe da shi”


Anty ta saka dariya domin ita kanta da tai marin ta ji zafi balle shi da aka mara.


“Ai dan ka tabbatar ba mafarki bane gaske ne miliyan sun shigo”


Sai gashi yana murmushin ya duka yai ma Allah sujudar godiya, tun a ranar ya rabawa abokansa da yan uwa 100k ya bawa Anty 500k ya rike 400k. A week later Ammy ta saka Nana ta kira shi ya zo ta hada shi tare da mutanen da Mai Martaba ya wakilta suka kai shi million quarters aka nuna masa gidan da Mai Martaba ya bashi, sai ya rasa bakin godiya, ba tabbatar da gaske ba ne sai da aka ba shi keys din gidan da takardu, ba shi kadai ba Anty ma kuka ta rika shi ganin katon gida mai gate da manyan dakuna da falo, ko'ina an gyara furniture ne kawai ba a saka ba, daman duk wanda ya san unguwar ya san yadda gidanjen unguwar suke da kyau da tsaruwa, ba su da wani girma sosai sai dai an musu tsari mai kyau ta yadda kowa zai


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login