Showing 207001 words to 210000 words out of 273152 words
Chapter 70 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt
iya kwalliya a duk garin Yola, kuma wanda zata iya home services?”
“Akwai su da yawa, Amaryar za ayi ma?”
“Yeah yau za ayi Walima a nan, so ina son ta fito ne sosai, na yi magana da mai kaya tace yau zata kawo da rana”
“Amman Sirleem baka ganin Walima a gidan zai haifar maka da matsala? Za a iya gane kai ne fa”
“No ai ba zan bar wata alama ba, ita ma kuma na fada mata kar ta fadawa kowa, daman dai ina son mutanen da basa son cigabanta ne su ga a inda ta tare, that's all”
“Okay ba matsala lemmi ask my Sis ka san su ne yan gari”
“Okay idan ta fada maka sai ku yi magana da ita, ta zo misalin 3pm”
“Ba matsala angon boye”
Sirleem ya sauke wayar yana dariya, kicin ya shiga dakansa ya shirya musu abun karyawa daman duk wani abun bukata tun daga kan abinci har abun sha da kayan amfani ya zuba a kicin din. Sai da ya gama sannan ya shigo ya tashe ta a hankali yana kissing dinta kama ya samu sweet, a saman gado a jera mata abun karyawa yana feeding dinta a hankali, sai ya tabbatar ta taune sannan yake saka mata wani a baki. Bayan sun gama ya shiga yai wanka ya saka kananan kaya ya zo kusa da ita ya zauna yana janta a jikinsa kamar zai shigar da ita.
“Zan fita yanzu, na san kawayenki za su zo ganin daki, ban da fadawa kowa wanene ni pls”
Ta daga masa kai tana jin kamar tai kuka.
“Ki kula da jikinki idan zan dawo zan biyo miki da wani magani okay”
Nan ma kan ta daga masa sannan ya sumbance ta ya fita. Hakan ya bata damar karewa katon dakin kallo tana mamakin ace wai ita ce a ciki.
ZAINAB POV.
Tana zaune falon har akai sallah magariba sannan ta tashi ta shiga cikin domin yin sallah. Iya na ganin haka ta tashi da sauri ta shige dakinta ta maida kofar dakin ta rufe har da makulli, sannan ta nufi wardrobe ta ta bude ta dauko tukunyar kasar nan mai jan kyalle ta kara bakinta tai magana da muryar da ita kadai zata iya jinta, sannan ta kara kunnenta ta saurari abun da ake fada kamin ta maida tukunyar a mazauninta. Ta duka karkashin gadonta ta dauko wayarta ta bude ta dauko kurwar daya daga cikin kurwa biyu da suka rage ta warware zaren da yake kai sai ga wata yar abu ma kamar tsokar danyen nama karami yana numfashi, rufe hannunta tai ta janyo wani bakin mayafi ta rufe hannun dake dauke da kurwa, sai kurciya ta bayyana ta cikin bakin mayafin yana ta fisge fisge alamar lafiyayya ce mai jini a jika, dukawa ta sake yi wata robar ta janyo ta bude ta dauko wata tsohuwar kaya ta saita bayan kurciyar ta bangaren hannunta na dama ta caka mata ƙayar, take kurciyar ta zabura ta sai ta lafe, wanda hakan yai daidai da zaburar Maijidda dake zaune a dakinta tana duba wasu kayan na order da kawarta ta turo mata. Iya ta maida kurwar ta nade sosai sannan ta dauko wani karamin gwangwani ta kunna aci balbal din jiki ta kifa wani kwano ta dora kurwar a kai ta tura gwangwanin karkashin gado ta tura kwanon saitin wutar ta yadda kurwar zata azabtu, ta kara kurwar a kam wuta, sannan ta sake saka kayar ta soka ta gefen tsokar dake nade ta bangaren damanta daga kasa, can kuma ta tashi ta nufi inda tukunyar nan take ta dauko ta kar bakinta, sai da tai kirarin data saba sannan ta fadi kalar ciwon da take son turawa Maijidda.
Gaba daya sai Maijidda ta rasa natsuwarta ga wani uban zafi da ya sako ta gaba, duk ac dake dakin sai ta ji wani irin zafi ya taso mata, haka dai ta daure tana duba kayan kamin idonta ya fara cika da hawaye saboda azabar ciwon kai, aje wayar tai tana tana jikinta da yai mugun zafi kamar kyankyason wuta, ga bayan ta ta bangaren hannunta na dama sai ciwo yake kamar an soka mata abu a ciki, da zafin ya fara mata yawa sai ta gane ba daga dakin ba ne daga jikinta ne, kamar mahaukaciya haka ta fita daga dakin ta nufi kitchen ta bude firiza ta dauko kankaran ta fasa a roba ta dawo ta dakinta ta shiga bathroom ta surka kankarar ta cire tufafin jikinta ta watsa ruwan kankarar tana jin kanta kamar zai bare, daker ta daura zane ta fito da gudu zuwa dakin mahaifiyarta tana kuka.
“Momy zafi na ke ji sosai, kaina ma ciwo yake kamar zai bare, kuma nan ma ciwo yake min sosai”
Ta nuna bayan kafadarta, ba karamin tashi hankalin Hajiya Talatu yai ba, daman can mace ce mai shegen son yaya balle kuma Maijidda da ta fi kwanta mata a rai fiye da sauran.
“Subhanallahi, me kika sha?”
“Ban sha komai ba, ban ci komai ba”
Ta fada tana lumshe ido tsabar ciwon kan da take ji. Hajiya Talatu ta kai hannu ta taba jikin yarta sai ta ji shi ba zafi.
“Kuma jikinki babu zafi”
“Akwai zafi Momy kaina”
Ta dafe kan tana kuka sosai.
“Yusra, duba driver waje idan baya nan ki kira Haroon yanzu muje asibiti”
Daker Maijidda ta iya saka tufafinta har suka shiga motar Haroon din ya ja su zuwa wata private hospital Annuri, kamin su isa asibitin Iya ta janye kurwar Maijidda jikin wutar wanda hakan ya bawa jikinta damar karbar zafin da kurwar ta dauka, sai zafin ya maye ilahirin jikinta, Hajiya Talatu na tabawa ta ji yayi zafi sosai. Ta samu kula ta musamman kasancewar asibitin wanda ta saba zuwa ce kuma asibiti ce ta masu nera, duk wanda ka gani asibitin babban mutum ne ko kuma dan babban mutum dole a kula da kowa yadda ya dace. Gado suka bata bayan sun tabbatarwa Hajiya cewar taifot ce, allurar suka mata sannan suka saka mata drip, hakan yasa ta dan samu sauki har bachi yai gaba da ita. Sai a lokacin hankalin Hajiya Talatu ya kwanta domin da farko har ta fara jin tsoro tana tunanin ko abun da suka saka ayi ma Fadime ne ya dawo yarta, ko kuma saboda zancen aurenta da Baba Waziri yai ne da Shattima yasa it ma zata leka kiyama.
Zaunawa tai a kujerar dake dakin ta majinyata tana kiran mijinta ta shaida masa abun da ke faruwa, bayan a sauke wayar ta kalli Haroon dake tsaye ta ce.
“Ka tafi gida, ka farawa Yusra da Nazma su shirya komai na kwana sai ka kawo wata a cikinsu ta kawo min”
“A nan zaki kwana?”
“Dole ai, maybe gobe su sallame ta idan ta samu sauki, ka tafi kawai ka fada musu an ba mu gado”
“Okay”
Ya fada sannan ya juya ya fita, fitarsa tai daidai da shigowar kiran Hajiya Babba a wayar Hajiya Talatu, da muryar da za ta karantar da Hajiya Babba damuwarta tai picking call din.
“Hajiya Talatu? Haka aljannun nan suke aiki kamar yankan wuka? Yanzu nan Shattima ya turo a duba masa yarinyar wai ta bata a ganta ba”
Hajiya Talatu ta zaro cikin wani irin jindadi take ta manta da wani damuwar ciwon yarta.
“Alhamdulillahi abun nema ya samu, dauke ta su kai kenan? To ai haka ya fi ba ganta ba balle wata maganar ta fito”
“Wallahi ni ma haka na ce, amman fa tsorona daya kar ta dawo ko kuma ta fadi masarautar nan a dawo da ita”
“Aa haba Hajiya, ai ke ma kin san maganin biri karen maguzawa, ai ba za su kaita inda zata iya dawowa ba, tun da har mun fada musu asiri ne ba ma son ta tonu dole su san yadda za su yi da ita, ni ai murna ta zo min a wani yanayi ga ni a asibiti Maijidda ba lafiya wai tafot ne”
“Subhanallahi Allah ya bata lafiya, agaishe ta da gobe zan shigo na dubata”
“Amin Amin Hajiya na gode sosai”
Ta sauke wayar cikin wani irin farinciki marar misaltuwa.
***
Hajiya Babba na aje wayar ta kalli Jurry da ita ma murmushin jindadi take za ta yi magana sai ga Sirleem yayi knocking kofar sannan ya turo ya shigo. Hakan yasa Jurry saurin mikewa tsaye ta fice ba tare da ta gaishe shi ba, domin ita har yanzu fushi take da shi saboda marin da yai mata kwanakin baya akan Falmata.
Shi dai be kula ta ba ya zauna gaban Hajiya Babba dake ta yakar hakora kamar wanda akai wa gafara.
“Sirleem sai yanzu”
Ta fada tana kallon yadda fuskarsa ke ta annuri kamar ba shi ba, har wani kyalli yake.
“Barka da dare Hajiya”
“Yauwa, ya jikin?”
“Alhamdulillah”
“Ka je asibiti?”
“Eh sun ba ni magani”
Ta yi shiru har na wani lokaci shi kuma sai sake saken yadda zai shera mata wata karyar yake so that ya samu ya sake kwana a gidan amaryarsa.
“Alhaji Kabir ya kira ni, ya ce ka same shi da maganar ka na son a mika maka ragamar mahaifinka a hannunka”
Ya dan shafa kansa.
“Eh tun kwana bayan nai masa magana, yace min na jira ayi a gaban kowa kuma yace zai hada wasu takardun ya hannata min, ya ma ba ni wasu and i think yanzu ya kamata na rika natsuwa ina duba komai yadda ya kamata, jiya a gidan na wuni duba su sai gashi dare ya zo da fever”
“Ayyah, dole ai saboda baka saba ba, amma da sannu komai zai zama kamar an saba din, ya fada min zai tara kowa saboda a zama shaida, kuma yace na saka ranar da nake ganin ya dace a yi launch din new manager a babban kamfanin mahaifinka, na saka karshen watan nan”
Sirleem ya kalleta da sauri.
“Hajiya karshen watan nan be yi wuri ba? Sai kace abun da za a gudu?”
“Me ye abun sauri a dukiyarka? Shekarana nawa suna juyawa? Sai yanzu da lokacin karba yai za a ce an yi sauri? No karshen watan nan ya wadatar ayi biki a mika maka ragamar kamfaninka a hannunka da ma sauran kamfanonan da gidanjen da komai ma”
“To Allah yasa hakan shi ne mafi alheri, kuma ya bani iko kula da ita yadda ya dace”
“Ameen haka na ke son ji, Allah yai maka albarka”
“Ameen”
Ya fada yana mikewa tsaye.
“Ni zan koma can, Hajiya na fi jin zakewa a gidana gaskiya, ko ba komai zan samu na maida hankali kan abubuwan da suke gabana”
“Rantse min ba Mansura ta zo garin nan ba”
Kamar abun wasa sai ya fara dariya.
“Wallahi Hajiya bata zo ba, Mansura tana Kaduna Wallahi”
“Shikenan Allah ya tsare ka kula da kanka”
“Ameen sai da safe”
Ya fice cikin jindadi, Hajiya ta bar shi ya tafi ne kawai saboda ita ma tana cikin wani farincikin, kuma tana son ya maida hankalin kan abubuwa da ke gabansa kamar yadda ya fada, ba dan haka ba babu abun da zai saka ta kyale shi ya kwana a gidansa shi kadai.
TUMBA POV.
Ko da aka isa da ita asibiti bata cikin hayyacinta, gaba daya hankalinta ya bace, duk wanda zai ga halin da aka shigo da ita sai yayi tasbihi ya kawar da ido, domin kafar da babur ya buga gaba daya ta cire a hannu a ka iso da ita, ga naman fuskarta ya kwaye gaba daya baka ganin komai sai fatar can ciki mai jini wanda bata da kyau gani, hannunta na dama ma ya karye sai dai shi be cire ba sakamakon motar dake bayansu da bugu babur dinsu ita da Mai babur din sukai sama ita ta fada jikin wata motar, wanda hakan ya sa wani mai babur din ya bugeta babur din kuma ya fada kanta, shi kuma mai babur din da ta hau ya fada gefe, sai yai hanzarin tashi da jimuwar da yai, ganin yadda ta Tumba take sai ya saka ya manta da na shi ciwon, da taimakon wasu mutane da kuma jama'in dake kula da titi aka kawo su asibiti, ba dan suna da tabbacin ita Tumba din tana da rai ba, Likitocin ne suke tabbatar da tana da rai sai dai tana cikin mawuyacin hali.
A take aka hau neman yan'uwanta cikin mutane da suka kawo ta, kowa yace be santa ba, yar jakar kudinta ma an dauke tun a can gurin da hatsarin ya faru balle a binciki wayarta ko wani abu da zai bada shaidar inda take, a dole aka koma gurin mai achaban ana tambayar inda ya daukota.
_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:59 - 🤐🤐🤐🤐: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
Sai da ya koma cikin gidan sannan ya shiga cikin gidan da tunanin Hajiya Babba tana nan har lokacin amman be tararda ita a falon da aka bari a bude, dakinsa ya shiga ya dauko kudi ya sallami mai Napep din sannan ya sake kowa ya dauko makullinsa motarsa ya fito ya shiga motar, sai da yai mata key sannan ya fara tunanin da wani ido zai kalli Hajiya? Me zai fada mata? Taya zai fara mata bayani? Anya ma zata fahimce shi? What if ta cilasta masa sakin Falmata? Haka ya bar motar kunne ya rasa abun yi tafiya ko zama, can dai ya ja motar ya fice daga gidan yana tukin kamar wanda baya son tafiyar.
Tsakanin gidansa da masarautar tafiya ce mai dan nisa amman sai dai a yau sai ya ji tafiyar ta masa sauri sosai, a maimakon yai fakin a inda ya saba sai yai fakin daga bakin gate din kamar wani bako ya fito yana tafiya gumi na keto masa kamar wanda yai sata, sai a yanzu yake jin cewar ya aikata wa Hajiya Babba laifi, sai dai ya san ida ya fada mata ba zata amince ba, a ganinsa shi mijin mace hudu ne zai iya auren Nana da wata ma.
Kamar wani marar gaskiya haka ya shigo cikin katon falon na Hajiya, idanuwansa duk sun wani fito kamar wanda aka ciro daga rame, ganin babu kowa falon yasa ya nufi dakin Hajiya Babba, yana turawa sai ya samu Karima da Kausar a zaune saman kujera sun kurawa Hajiya Babba ido. Ita kuma tana zaune saman gadonta har lokacin tana yafe da mayafinta da jakar da ta fita da ita duk suna hannunta har talkamin ba ta cire ba, Wardrobe dinta kawai take kallo, ko kyabta idon ma sai an dade take yi. Sirleem ya karasa kusa da ita ya duka a kasa, Kausar da Rima kan kallon mamaki kawai suke masa, Rima ba dan ta ji da kunnenta ba kuma ta gani da idonta ba da ba zata yarda ba ko waye zai fada mata haka karyatawa za ta yi.
“Hajiya....”
Sirleem ya kirata sai ta juyo a hankali ta kalleshi. Shi kuma ya sunkuyar da kai ya rasa abun da zai fada mata.
“Yaya ba a yanzu ya kamata ace ka gane ka aikata kuskure ba, tun kamin ka aikata ya kamata ace ka gane kuskure ne kake kokarin aikatawa, fisabilillahi me zaka yi da yarinya kamar wacan? Kuma ka san Hajiya ta zaba maka Nana a matsayin matar aure? Ko da baka son Nana be kamata kai aure a boye ba, mahaifiyarka tana raye mu ma kanenka muma nan danginka kowa yana nan...”
Karima ta fada cike da jin zafin abun da dan'uwanta ya aikata. Sirleem dai be ce komai ba kuma be dago kansa ba, gaba daya ya rasa abun da zai yi. Murmushi Hajiya Babba tai irin murmushin da kana ganinsa ka san ba na farinciki ba ne, wasa wasa ya kwashe kusan 3 hours a dakin, tun yana jin nauyi da kunyar yi mata magana har ya kai yana rokon tai magana.
“Hajiya ki ce wani abu mana, ki furta wani abun, na san ban yi daidai ba ki fada min ki ce Sirleem baka kyau ba”
Ya fada idonsa cike da hawaye domin har ga Allah ya san ya saka mahaifiyarsa a damuwa. Haka ya gaji da rokomta ya gaji da magiya ya mike tsaye ya fice tana ta innalillahi.
Cikin motarsa ya koma ya zauna ya dafe kansa ya rasa abun da zai yi, ya rasa inda zai saka ransa ya ji, ya rasa abun da zai yi ya samu sassauci. Kunna motar yai ya juya kanta ya fice daga gidan gaba daya.
Sai da ya fita sannan Hajiya Babba ta tashi ta fito daga dakinta ta zauna a falo, ta maida hankalinta gurin tv tana kallo, ba dan babu plasma a dakinta ba, sai dan jin da tai dakin ma ta fita daga kanta gaba daya, gashi ta kasa cire talkaminta ta kasa aje jakar balle kuma mayafi komai da ta fita da shi yana nan jikinta.
Plasma take kallo sai dai ina damuwar da take ciki ta hana ta gane mutane ne a tv ko aljanu ko kuma cartoon? Kallo kawai take saboda ta gusar da abun da ya tsaya mata a zuciya, amman ta kasa abun ya shiga zuciyarta sosai ya danne mata komai ciki har da kalamai da take jin kamar ta kai wa'adinsu.
“Hajiya ga ruwa”
Kausar ta mika mata ruwa a kofi cike da damuwa. Hannu Hajiya ya mika ta karbi ruwan ta kai bakinta kwarara