Showing 204001 words to 207000 words out of 273152 words

Chapter 69 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72760

dakin kamar tana gani.


“Sannu”


Ta fada mata, sai ta kasa amsawa ta kasa ce masa komai.


“Zo ki kamata”


Daker da addu'a Ataa ta rika hannunta domin ta tsorata sosai da halin da ta ganta a dazun. Aliyu ne ya shige gaba ya bude mata kofar dakin bakin Ataa ta shiga ta ita, Aliyu ya mika mata ledar maganin ya fita ya dauko ruwa sannan ta balla maganin ta bata, ta bata ruwa sai dai komai sai ta ce mata ta yi take iya yi. A dakin Fadime ta kwana a sai da ko da wasa bachi be kusanci idonta ba, tana zaune shiruuuu idan ta gaji da zaman sai ta kwanta, idan jikinta yai mata tsami sai ta tashi, wani irin yanayi take ji mai wuyar fassara, komai ya ki mata dadi a duniya. Misalin 9 na safe Muhseen ya iso gidan sakamakon kiran da Aliyu yai masa, sai da suka yi magana da shi sannan ya shiga dakin ya dakin a hankali. Can karshen dakin ya hango ta zaune, ta abincin karyawarta na gefe bata taba komai ba ta kurawa silin ido idonta har sun fara wani fari fari alamar amakantar na son kamata. Kusa da ita Muhseen ya karasa yana kallonta can kuma ya taba jikinta sai ya ji shi da sanyi.


“Ina ina jina?”


Ta dawo da dubanta ta inda take jiyo sautin muryarsa.


“Yi magana fada min sunanki”


“Ina son na san sunana ina son na san ni wace irin halittace, ina son na daina ganin wannan duhun, ina son na daina jin abubuwan da na ke ji, ka taimaka min....”


Ta fada tana wani irin rirrike shi kamar zata shige a jikinsa sai kuka take ma ban tausayi. Juyowa yai ya kalli Aliyu.


“Zan tafi da ita asibiti”


Aliyu ya daga kafadarsa alamar ba matsala. Daman can ba wani son shigowarsa yake a gidan ba sai idan ta kama dole saboda Ataa a ganinsa har yanzu yana nan da sonta a ransa kamar da. Mikewa yai tsaye sai ita ma ta mike tsaye da sauri ta rike shi gam tana jin kamar ta taba rike wani makamancin haka, a kokarinta na tunawa ta ji kalar dariyar jiya, da muryar yara ana ta mata dariyar cikin kwakwalwa, take ta sake shi ta dafe kan tana ihu.


“Wayyo kaina wayyo ni kaina.... Ku taimaka min..... Dariya na ke ji cikin kaina.... Wayyo ni kaina...”


Ta fada tana wani irin kuka mai ban tausayi hawaye sai sauko mata suke.






_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:59 - 🤐🤐🤐🤐: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*




Har suka isa police station din suka yi abun da za su yi suka gama police su kai wa Fadime tambayoyi bata iya ganin komai sai duhu, ta kasa amsa ko wace tambaya komai jin sa take ya zame mata sabo, sai dai ta kan ji wani kamar ta taba jinsa. Bayan sun kama Ataa ta sake kama hannunta ta sakaa baya Aliyu kuma ya shiga gaba ita ta shiga front seat su ka ja motar zuwa gida.
A nan ma saurare kawai take har suka isa, tana jin karar bude gate din sai ta ji kamar ta taba jin irin karar sai dai a ina? Shi ne abun da ta kasa tunawa. A harabar gidan suka faka motar Ataa ta fita ta bude mata motar ta riko hannunta.


“Fito a hankali”


Ta fito tana jin kamar wani ya taba rika hannunta ta fito daga mota amman ta kasa tuna a ina ne kuma wanene. Tana biye da su har suka shiga cikin katon falon mai cike da kayan alatu, ga sanyin ac da plasma dake ta aikinta. Tana ji muryar yaran da suka yo kan Ataa da gudu.


“Momy ba ku siyo komai ba?”


“Ba mu je ba ne”


Ataa ta fada sannan ta zaunar da Fadime saman kujera, zata zare hannunta daga na Fadime, sai Fadime ta jimke hannun.


“Miyasa na ke ganin hudu? Bana komai sai hudu, haka ke ma kike gani? Duniyar ce a haka? Ko kuma ni ce ba daidai ba?”


Ta tambaya hawaye na sauko mata, sai Ataa ta juya ta kalli Aliyu da fuskar tausayi, kamin ta sake kallon Fadime.


“Ina jin ko dai idonki ya samu matsala ne, amman mu na ganin komai”


Ta saki hannun Ataa a hankali tana jinta a wani yanayi marar misaltuwa, hayaniyar tv da take jin sai ta yi kamar zata tuna wani abu sai kuma ta kasa. Hannayenta ta saka ta dafe kanta ta fashe da kuka.


“Miyasa na ke jin abu marar dadi yana ratsa ni? Me yasa bana ganin komai kamar ku? Ina jin kaina kamar babu komai a ciki”


Ta fara taba jikinta domin tantan ita din wace irin hallittace.? Ta mike tsaye sai kuma ta koma ta zauna, kamar an tsikareta sai ta sauka kan kujerar ta zauna kasa, sai kuma ta ji zaman babu dadi gaba day sai ta rasa abun da ke mata dadi a duniya, kwamtawa tai a gurin kasa ta takure kanta jikinta sai rawa yake kamar mazari. Ataa da yayanta dai sai kallon ikon Allah take, Aliyu kam har ya haye sama ya bar su a falon. Ataa ta duka kusa da ita ta kai hannu ta taba jikinta sai ta ji shi da zafi sosai hawaye sai zuba suke mata kamar ruwa.
Wani irin tausayin Fadime ne ya kama Ataa sai ta tuna ta tata rayuwar shekarun baya, wata kila ita ma wahala da azabar rayuwa ne ya saka ta a wannan halin. Mikewa tai tsaye ta nufi upstairs tana share hawayenta, kofar dakin Aliyu ta tura ta shiga, sai ta tsaya daga bakin kofar shi kuma ya dago kansa daga wayar dake hannunsa ya kalleta, be ce mata komai ba ya mika mata hannunsa alamar ta zo, sai ta karasa kusa da shi ta zauna idonta na sake cika da hawaye.


“Hamma zaka duba ta? Jikinta yayi zafi sosai kuma kuka take yi, and i think idonta ya samu matsala”


Rumgume tai sosai ya sumbanci saman kanta.


“Da ace na tsaya dubata cewa za ki yi ina kula ta”


“Ai ita wannan bata gani bata san yadda kake ba balle ta ce tana sonka”


Yayi murmushi.


“Idan kuma idon ya bude fa?”


Ta kai masa dudu a baya, har sai da yai yar kara kamar ya ji zafi da gaske.


“Ni fa ba likita ba ne balle na dubata”


“Yeah na sani, wai ka ga halin da take ciki mana”


Sannan ya sake ta ya mike tsaye, sai ta biyo shi a baya suka fito tare. Ko da suka sauko Fadime ta matse jikin kujerar sosai tana jin kamar ta shige ciki har lokacin jikinta rawa yake hannayenta kuma dafe a kanta tana ta irin kukan kamar na fita hayyaci. Dukawa yai gabanta yana kallonta yanayin da take ciki abun tausayi ma matuka, abunda ya fahimta kamar ta yi losing memory ta ne, and gashi bata gani. Hannunsa ya kai ya taba jikinta ya ji shi da zafi, sai ya mike tsaye.


“Ba mu da magani a gida, and i think Muhseen ya kamata mu kira ya duba ta”


“Okay ka je ka siyo ko kuma ka tafi da ita asibitin ya dubata”


Ataa ta fada tana jin kamar ta fashe da kuka.


“No tafiya da ita asibiti zai dauki lokaci yanzu, bari da a siyo mata wanda zata samu bachi kamin gobe sai mu ga abun da za'ayi”


“Okay bari na kai ta daki”


Ya nufi sama be dade ba ya sauko rike da keys dinsa ya fice Ataa kuma ta kama hannunta.


“Ta zo mu je ciki ki na kawo miki abinci”


Ba musu ta mike tsaye ta bi Ataa ake rike da hannunta.


“Taka a hankali stairs”


Ataa ta fada mata, the way da tai pronouncing stairs sai ta ji kamar ta taba jin wani abu makamancin haka, but she cant remember when and where, sai da ta fara takawa ta sake jin abu na kokarin tuna mata baya, sai da su kai rabi sai ta soma tuna kamar an taba rike hannunta a guri irin wannan and namiji ne ba mace ba, a kokarinta na zufafa tunaninta sai ta jiyo dariya a cikin kanta kamar ta jarirai ga wani uban kara kamar ana rushe gini, da sauri ta fisge hannunta ta dafe kanta ta saka ihu da kuka a lokaci daya.


“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”


Ataa ta fada har sau uku cikin dakiya tana kallon Fadime da ke yin gaba ta yi baya kamar zata fadi.


SHATTIMA POV.


After sallah isha'i ya shigo bangaren Ammy, ko kadan baya jin dadin tafiyar da Fadime zata yi, ji yake kamar sun dade a tare, tuna idan ta tafi ba za su sake haduwa ba ya fi komai taba shi. A karamin falo Ammy ya zauna, doing nothing kuma still yana jin wani irin yanayi babu dadi, and he cant tell why. Yana jin wayarsa na ringing ya ki ya daga har sai da ta kusa yankewa.


“Ra'ees”


“Ranka ya dade, transfer ka ya fito an tura maka copy a email”


“Ina suka kai ni?”


“General hospital Yola”


“I think ya kamata na bude nawa asibitin na huta fa”


“Gaskiya ya kama, amman ko ka bude ai ba zakin wannan zaka yi ba, sai ka hada biyu idan ka samu hutu kana asibitinka, ko kuma idan baka da duty”


“No ina bukatar tawa ta kaina, na shiga a lokacin da na ga dama, na fita a time din da na dama”


“Shattima kenan a gurin aikin sai an nuna musu Sarauta, kana da right tun da kana da halin budewa”


“Zan kira ka aje wayar”


“Lafiya dai?”


“Ba komai”


Ra'ees ya yanke wayar kamar yadda ya bukata, Shattima ya mike tsaye yana tuna alkawarin da yai ma Fadime na siya mata kaza da yogurt, murmushi yai ya mike tsaye yana jin ya kamata ya cika mata alkwarinta, a kokarinsa na faranta masa rai zuciyarsa ta raya masa ya tafi tare da ita daga can ya siya mata wasu abubuwan na tsaraba. Fitowa yai daga falon yana wani irin takun kasaita kamar wanda baya son taka kasa fuskar nan a hade kamar be taba dariya ba. A hankali ya kai hannunsa ya tura kofar dakin Nana ya shiga, sai ya hango abinci a kasa kusa da gadon Nana yanayin yadda aka abinci aka raga kadai ya isa ya sanar masa cewar Fadime ce ta ci shi, ga kuma agogonsa da ya bata a kasa kusa da plate din shimkafar, karasa yai gurin ya duka ya kai hannunsa ya dauki agogon yana taba kamin ya dago idonsa kadan ya kalli kofar bathroom din dake bude, maida dubansa yai kan agogon yana shafa shi, ganin an dauki lokaci bata fito ba yasa shi mikewa tsaye ya nufi bandakin, hannunsa ya kai ya kara tura kofar, sai ya ga wayam babu kowa a ciki, dan mamaki yai ya juyo yana karewa dakin kallo. Yana kokarin juyawa Nana ta shigo rike da wata sabuwar jaka sai murna take.


“Ya Shattima yaushe ka shigo?”


“Yanzu ina Fateema”


Ya amsa mata da murmushi. Sai ta nuna inda abincin da Fadime ta ci yake.


“Nan na barta ta na cin abinci ko ta shiga bandaki ne?”


“No bata ciki”


“Ko ta fita? Lemmi ask”


Ta aje jakar a saman gadonta sannan ta fita da sauri zuwa falo. Jekadiya da Inna wuro da wasu hadimai dake gurin ta fara tambaya duk suka ce ba su ga fitowarta ba. Sai ta dawo ta sanarwa Shattima.


“Ki ce jekadiya tace ta dubo ta gurin babanta ko taje can”


“Okay”


Ta juya ta fita, shi kuma ya zauna bakin gadon ya kurawa abincin da Fadime ta ci ido, haka nan kawai yake jin rashin natsuwa. Jekadiya da kanta ta je ta duba bangaren da aka sauke su Bappa ta tambaya ko Fadime na nan suka amsa mata tun da yamma da wata hadima ta zo ta tafi da ita bata dawo ba, bata ce musu komai ba ta dawo ta sanarwa Nana, cike da Mammaki Nana ta shigo ta fadawa Shattima.


“Ya bata can sun ce wai tun yamma da wata hadima ta fita da ita bata dawo ba”


Shattima ya mike tsaye still yana jin rashin natsuwa.


“Bata dakin Ammy?”


“Daga can na fito fa”


Shiru yai yana tunanin inda zata shiga, ba gani take ba balle yace ya fita wani gurin. Fita yai dakansa ya saka Jekadiya da wasu hadimai nemanta, wasa wasa har 10 na dare ba a ganta ba, duk inda ya kamata da inda be kamata ba duk an duba har bangaren Hajiya Babba sai da Shattima ya tura a duba ko tana can, daga baya ya koma yana tambayar waye da waye ya shigo cikin gidan. Duk wanda ya ganta da yamma nan zai fadi cewar ya ganta Jekadiya sai nanata take ita ta kai mata abinci ma kuma bata ga fitowarta ba. Sosai hankali Shattima ya tashi wata kila ko dansa ya bace ba zai shiga wannan tashin hankalin ba, babu abuj da yake ji kamar mahaifinta da ke ta shirin tafiya gobe tare da ita, me zai fada musu? Ya za su kalli abun? Ya za su ji? Anya ma za su yarda da shi?


“Jekadiya”


Jekadiya ta matso da sauri.


“Ranka ya dade”


“Address din da na baki last time, kin gane gidan su Hajiya Karama?”


“Eh an gane ranka ya dade har an kirata”


Ta amsa da sauri.


“Ki je da dogarai ku duba yarinyar a can”


Jekadiya ta mike tsaye da sauri ta fita zuwa aikin da Shattima ya saka ta, shi kuma ya nufi dakin Ammy rai ba ce, yana shiga ya zauna a kan kujerarta yana kallon wani bangare na dakinta.


“Kana tunanin za a sace ta ne?”


“Maybe saboda ta saka rayuwarta a hadari, kuma idan Hajiya Babba ta ji ko Iya ba za su kyale ba, ni yanzu babu wanda na ke ji kamar mahaifinta”


“Bana tunanin Hajiya Babba zata ji, saboda ba ayi zancen a gabanta ba, ko a gaban wani nata, Nana ma ban labarta mata ba, sai dai ko Iya ita ma kuma bana tunanin za ta iya shigowa har cikin gidan nan ta saci yarinyar, amman na san tabbas za ta ji zafin tona mata asiri da tai ga kuma abun na saka aka mata a dazun domin ganewa idan da gaske mayyar ce kuma na tabbatar”


Shattima ya kalleta.


“Me kika mata?”


A natse ta labarta masa komai.


“Yeah maybe ita ta sace ta saboda ta ji zafin abun da akai mata”


Ya ciro wayarsa, ya shiga neman wata number after a few seconds ya aikawa number kira.


“Galadima a duba security cameras da suke gidan nan a ko'ina, a duba idan wata bakuwar fuska ta shigo yau, kuma idan ka ga wani abun da baka yarda da shi ba ka sanar min, wata yarinya ta bata bakauniya ka bincika mana ko'ina”


“Tau ranka ya dade”


Ya sauke wayar yana jin wani karin tashin hankalin na kusantarsa.




SIRLEEM POV.


Sai da rana ta fito sannan ya tashi Falmata, cikin wani irin nauyin bachi da ya cika mata ido da kuma nauyin kunyarsa ta farka ta dan daga idon kadan ta kalleta sai ta sake rufe idon. Murmushi yai ya sumbacin goshinta ta yaye bargon da ta rufa da shi ya saka hannunsa biyu ya dauke ta cak, be sauke ta a ko'ina ba sai bandaki, ita kan gaba daya ma ta kasa kwarran motsi domin jikinta har yanzu yana amsa mata ga kunyar Sirleem da take jin kamar masa ta bude ta shige ciki ta huta. Ruwan zafi ya hada ya gasa mata jikinta sannan ya zuba mata tai wanka ta daura tawul ta fito tana ta kokarin danne kukanta domin har ga Allah bayan dukan da Baba yai mata har ya kusan karya mata kafa bata taba karo da wani abu mai zafi da wahalar da mai rai ba irin na jiya. Ko da ta fito ya shimfida mata carpet ya aje mata wasu tufafinta, yanayin yadda tafiyarta ta canja kadai abun tausayi ne. Ba dan ta so ba ta bar shi ya taimaka mata ta saka tufafin da su kadan suka mata yawa.


“Za ki iya yin sallah a tsaye?”


Ya tambaya yana kallonta fuskarta, tausayinta yasa ya ji kamar ya yayi mata sallah. Kai ta daga masa ta kabbarta cikin karfin hali tai sallah, bayan ta gama kuma ta ji zama na neman gagararta, wani iri zafi da yaji take ji a kasanta kamar an yanka gurin, a hankali a hankali take share hawaye tana ta sauke ajiyar zuciya. Sirleem ya matsa kusa da ita ya jata jikinsa ya rumgumen yana shafata a hankali.


“Im sorry”


Ya fada can kuma ya tsaki yana jin haushin rashin hakurinsa. A jikinsa tai bachi sai maida numfashi take a hankali, abun da bata taba ba a jikin wani, shi ma kuma abun da be taba ba ya rumgume mace har tai bachi kamar yadda yai ma Falmata.
Fuskarta yake ta kallo yana jin wani irin tausayinta da kimarta na kara shiga idonta, yatsunsa biyu ya saka ya shafa fuskarta yaja hancinta kadan.


“Pretty girl”


Ya furta yana murmushin farincikin da be san ta ina yake zuwa masa ba. Tashi yai tare da ita ya kwantar kan gadon ya lullubeta yai kissing din kumatunta sannan ya dauki wayarsa a hankali ya dauke ta hoto, sannan ya fice daga dakin, saukowa yai kasa yana kiran wani abokinsa.


“Bilya how far”


“Good ya kake?”


“Im good very good”


Ya fada yana murmushi.


“Dan Allah wa ka san ta kware a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login