Showing 174001 words to 177000 words out of 273152 words

Chapter 59 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72764

na kawo su”


Ta lake kafada.


“Wayonka kenan? Wallahi ni ba zan yarda ba, ka bar ni a wannan gidan Allah kadai yasan zuciyar mutum...”


“Ni ma ba nan zan barki ba ai, masarauta ki zauna tare da mutane”


“Masarauta?”


“Eh”


“Gidan Sarauta kenan fa?”


“Yes”


Ta wara ido kamar tana gani har da sy bude baki jin an ambaci masarauta, sai dai tunawa da Wasim ya kaita gurin mayya yasa ta hade jindadinta.


“Gurin wa zaka kai ni?”


“Ammy”


“Ita ma tsohuwa ce kamar Iya?”


For the first time Shattima ya daka mata tsawa.


“I will slap your mouth, and Ammy mahaifiyata ce, so control your tongue, kuma matar sarki ce karki je kina mata zuba anyhow take zaki ji mari, ba zata dauki abun da nake dauka ba”


Ta kara fito da idonta waje kamar za su fado.


“Kai kenan dan waye?”


“Dan Babansa”


Ta yamutsa fuska.


“Kenan kai agola ne ko?”


Kai ya girgiza be sake ce mata komai ba, ya kai hannunsa ya murda key motar sai ta tashi.


‘Oh’


Ya fada a ransa kamin yai danna horn ya nufi gate, kamin ya karasa mai gadin ya bude masa gate din. Sai da suka hau titi Fadime tace.


“Akwai nisa sosai?”


“Ko mu wuce airport din da motar ta tashi”


Yana fadar hakan motar ta fara fisga tana gaba da baya, take Shattima ya fara addu'a.


“Aa mu dai fara zuwa gidan Sarkin, Sarki fa, gobe sai mu tafi gida, ka daina wannan abun da kake da mota bana so”


Ta turo baki gaba, ya dan wara idonta yana kallonta kamin ya dauke kai yai murmushi yana cigaba da karanta addu'o'insa. Sun isa cikin masarautar lafiya kalau, a harabar Ammy yai fakin sannan ya zagayo ya budewa Fadime ya fito da ita. Sai da ya rufe motar sannan ya kai bakinsa saitin kunnenta ya rada mata.


“Dan Allah karki gisgani a gaban mutane kinji? Zan siya miki kaza da yogurt”


Ta washe hakora.


“To...”


Ya kama hannunta suka nufi hanyar shiga ciki yana daure fuska kamar ba shi ba. Sai da suka fara hawan stairs din sannan tace.


“Me muke hawa?”


“Ciki zamu je, pls ki daina yawan min magana, da tambaya any how a gida ma ina amsa miki ne saboda muna mu kadai ne amman nan akwai mutane, daman can bana son yawan magana sai dole”


“Tsoron mutane kake ji? Ko kuma magana ciwo take maka?”


Ya daga hannunsa kamar ya kai mata rankwashi a ka sai kuma ya fasa, ya shareta kawai suka cigaba da tafiyar, ta kofar fadar Ammy ya shigo hakan yasa shi shiga bangaren kai tsaye, sai dai yana shigowa cikin falon hadiman dake ciki suka fara mika masa gaisuwa daman tun a bakin kofar shigowar wasu hadiman maza dake tsaron kofar suka gaishe shi. Fadime sai ta ji wani girma da kwarjini ya kamata duk da kasancewar bata ganin mutanen kuma bata san da waye Shattima ba. Bata dai ce masa komai ba har sai da taji sun bude daki sun shiga mai cike da sanyin ac ga kamshin turare kamar kamfanin turare.


“Daki muka shigo”


“Eh”


Ya amsa ta dan dole.


“Na ce dan sun ga Mamaka tana auren sarki shiyasa suke ta gaishe ka ko?”


Shattima ya kalli Ammy dake zaune tana cin abinci ita na ta kalleshi sai kuma ta kalli Fadime, be dai ce mata komai ba har sai da ya zaunar da Fadime shi ma ya zauna.


“Ammy ina kwana?”


“Lafiya kalau an tashi lafiya?”


“Alhamdulillah”


Yana rufe baki Fadime ta mikawa Ammy gaisuwa.


“Ammy ina kwana?”


Sai bayan few sec Ammy ta amsa mata tana ta mamakin inda Shattima ya samo ta daga ganinta dai bata gani.


“Lafiya kalau”


Fadime ta dan jingina jikin Shattima tana masa rada baki bude hakora har kunne tsabar far'a.


“Ita ce matar sarkin ko?”


Shattima kasa ce mata komai yai sai kallon Ammy yai, Ammy ma kallonsa take, yana yunkurin magana Nana ta turo kofar dakin shigo, a dayan barensa ta zauna cike da damuwa.


“Ya Shattima good morning”


“How are you?”


“Im fine, Ya ka ce zaka yi wani abu amman shiru”


“Nana i said i will karki damu”


“Akan Sardauna ko? Ko Hajiya Babba?”


Ammy ta tambaya, Nana ta juya ta kalleta.


“Aa Ammy akan makaranta na ne”


Sai kuma ta juya ta kalli Shattima.


“Ina saurare dan Allah Ya Shattima, kuma Jekadiya tace na fada maka Falmata na waje tana jiranka”


Ya gyada mata kai sannan ta tashi ta fice.


“Ammy...”


“Ina zuwa”


Ammy ta fada sannan ta mike tsaye ta nufi bandaki, budewar da Fadime ta ji an yi sai tai zaton ko Ammy ta fita daga dakin ne.


Sai ta kai bakin kusa da Shattima.


“Ta fita? Wani abu zan fada maka”


“Aa ta shiga bandaki ne”


Ta yi shiru can kuma tace


“Na fada maka wani abu? Wallahi na taba jin sunayen nan Nana, Falmata, Shattima, da wani namiji ko wa ko Jarumi ko waye suka zo gurin boka tare da wata yarinya da wata Hajiya ko wa? Har da sunan wannan maman taka Ammy, kuma da Nana har da Sardauna Wallahi, har aka ce ana son a rufe bakin Nana wai ko kar ta fadi me, ita kuma wannan Hajiyar dayar tace bata son ayi aurenta da wani sai bokan yace mata ai ba za ayi auren ba, har ya bata magani yace ta bawa yarta ta sha wai idan maye ya ci ta ya ci mutuwa, har da wata mai irin sunana Fadime, ita wannan matar sunanta Hajiya Babba, wai tana son a kashe dan sarkin kuma da sarkin... Har da irin sunanka a ciki Shattima na rantse da Allah kau”


Ba Shattima ba har Ammy dake bandaki tana jinta kasancewar bandakin a bude yake. Shattima ya gyara zamansa yana kallonta da mugun mamaki.


“Da gaske? A ina?”


“A gidansu Wasim gurin kakansa boka Wallahi kuwa, har da wani wai saka shi ya so Nana, ka bani kur'ane zan rantse maka, Allah ubangiji yasa Wasim ya zo Wallahi gabansa akai zai ce maka ba karya nai ba, ba a ma dade ba ana gobe Wasim zai maida ni gida, har take cewa ko nawa ne zata kashe kuma ko miye zata yi, kuma yace mata akwai tafiyar da ba dawowa”


Ammy ta fito daga bandakin ta tsaya jikin kofar.


“Wacece wannan?”


Shattima ya kalli Fadime kamin ya kalli Ammy.


“Fadime...”


Fadime ta sha jinin jikinta tunawa da abun da ya fada mata cewar Ammy bata son yawan surutu zata iya jin mari.






_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:56 - 🤐🤐🤐🤐: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


Ammy ta kofar bathroom din ta rufe sannan nufi gadonta ta zauna tana kallon Shattima, kallom dake nuna alamar ta bashi damar yai mata bayanin abun da ya tambaye shi.


“Sunanta Fadime, i meet her first a Katsina....”


Tun a farkon ganin da yai mata a Katsina har zuwa asibitin da zuwa gidan Iya, sai dai be fadawa Ammy cewar Iya mayya ce ba, ya fada Ammy cewar dai tana tsoron zaman gidan ne shiyasa ta matsa sai ta biyoshi.


“Ban yi zaton zaka dauki kafarka zuwa gidan Iya ba, duk abun ka girmi shi ya kamata ace ka bashi baya.... Matsayinka darajarka ta wuce Iya da Zainab su yi fushi da gidan su bar shi kai kuma ka dauki kafarka ka taka a gidan, me zaka fada musu? Hakuri za ka ba su ko kuma rokonsu zaka yi su dawo nan da zama?”


Shattima yayi shiru for seconds kamin ya hade yawun bakinsa.


“Allah ya taimakeki, agafarce Ammy ban dauka abun zai bata miki rai, Ammy kin sani ni da Zainab akwai kyakkyawar alaka da fahimtar juna a tsakaninmu, na je saboda na yi magana da fahimta da ita, daga baya kuma sai na gane rabon ganin Fadime ne yake kirana shiyasa na tafi amman amin afuwa”


“Shattima kai fa dan Sarki, ba ina fada maka hakan ba ne saboda ya saka ka girmar kan aa, ya kamata ka nisanci wani abu ka fuskancin wanda ya dace”


Fadime ta bude baki jin an ambaci dan sarki.


“Inshallah Ammy, nima ai kin san ba mutum ne mai son irin wannan ba, wannan ma na yarda rabo ne ya kira ni”


Ammy ta maida dubanta gurin Fadime.


“Ita miye alakarta da Iya?”


Fadime na jin haka ta mika hannu ta kama gefen rigar Shattima ta rike, cike da tsoron yadda ta ji yana bawa Ammy girma da ladabi a bayaninsa ta san tsoronta yake balle kuma ita da ya rabo. Ammy ta kalli rikon da tai masa shi ma kuma ya kalli hannunta sai da be janye mata hannun ba.


“I dont know maybe yar'uwarsu ce, ban dai tambaya ba”


A nan bude bakin tai ta zaro ido jin abun da yake fada, gabanta ya fadi kar dai Ammy tai musu dauka daya hakan yasa ta shiga kare kanta.


“Wallahi ba yar'uwar mu bace ai na fada maka komai, Wallahi ajiya aka kawo ni gurinta”


Shattima ya saka kafarsa ya taki kafarta kadan.


“Ni ka daina takina idan ban yi magana ba ai sai a dauka ko ni mayya ce kamar su...”


Ta fada tana turo baki tare da saka dayan hannunta ta taba kafar. Ammy ta kalli kafar sannan ta kalli Shattima da ya rasa inda zai saka kansa, ko kadan baya son Ammy ta ji zancen nan har sai ya gama bincikensa, gashi kuma ta fada a gaban Ammy bayan ta dauko masa wani labari da be san inda ta same shi ba.


“Ban fada miki wacece Ammy?”


Be karasa ba ta tari numfashinsa.


“Ka fada min kace matar sarki ce”


Shattima yayi shiru be sake cewa komai ba tsabar haushi, shi kansa ya san da ba ita ba ce a yau tai masa haka da ba zata sake kai labari ba.


“Ya sunanki?”


Ammy ta tambaya tana tattara hankalinta gaba daya ta maida a kanta.


Wannan karon sai Fadime ta juya gefen Shattima tana tambayarsa.


“Na yi magana?”


“Na yi magana?”


Ta sake tambaya jin ya shareta.


“Ban sani ba”


Ya fada yana watsa mata harara kamar tana ganinsa. Aiko Fadime ta kame bakinta tai gum kamar ba ita ba, ala dole sai Shattima ya bata umarni.


“Da alama dai akwai abun da kake boye min, wanda baka son na sani”


“Babu komai Ammy, gata nan ai aku...”


“Umarninka take jira ai”


Ammy ta fada sai Shattima yai murmushi.


“Ba ta ga damar magana ba ne dai, Fadime ba ki ji Ammy tana tambayarki ba?”


“Ai kai kace idan nai mata surutu da yawa zata iya dukana, shiyasa nake tsoron magana, Sunana Fateema amman a kauye ana ce min Fadime, a birni kuma Fateema”


“Me na ji kina fada dazun?”


“Yaushe?”


“Akan Hajiya Babba da Nana”


Fadime ta gyara zama tana jin an tabo mata inda yake mata kaikayi.


“Eh Eh, a lokacin da najr garin su Wasim to a garin daman garin matsafa ne, to kakansa babban boka ne, yana bada magani kuma yana tsafi sosai, shine wata rana wasu mutane suka zo neman magani gurinsa wasu hajiya biyu dayar ce Hajiya Babba sai wata Hajiya na manta sunanta, sai wani namiji daya sunanshi Jarumi, da wata budurwa, har ina boya bayan Wasim sai na ji tana cewa wai ayi mata magani Nana ta so wani mutum, kuma ta fadi sunan Shattima da wata Fadime har tana cewa a fada mata Fadimen, kuma tace tana son a daure bakin Nana kar ta fadi magana, kuma wai a kashe Sarki a kashe dan sarkin wai kuma a kare aiki da Ammy ta yi wai tana son ta mallake komai, labarin yana da yawa da yawa ne kuma shi bokan ya bawa Hajiyar da suke tare wani magani yace a daba a nama a bawa wata ta ci, yawwa na tuni ita wannan guntuwar Hajiyar tace wai tana son a lalata auren da za ayi da yarta da wani, kuma yace musu akwai tafiyar da babu dawowa, kuma tace wai a raba wani ko waye? Na manta sunanshi da Falmata, Wallahi zan iya fada ko a gaban waye, kuma idan Wasim ya zo a tambaye aji”


Gaba daya jikin Ammy sai yai sanyi, zuciyarta ta shiga bugawa da mugun karfi, Shattima ma shuru yai yana mamaki, ya san Fadime ba zata shirya karya ba, domin bata san zata hadu da shi ba, kuma abun da ta fada yayi daidai da wasu abubuwan.


“Jarumi ko kuma Jarma?”


Ammy ta tambaya tana ta tunanin maganar.


“Ko ma dai waye ne, sunan da J yake farawa, har da wata yar lauka lauka marar jiki, ko ni na fita albarka, na tuna har da cewa tai tana son asa Nana ta lalace kuma wai a saka ta ta zo wani, kuma wai a taba Falmata da wani mutum, kuma akwai Sardauna a labarin, har yace ta yi latti kuma Wallahi a kira matar agabanta ma zai maimaita haka”


Shattima ya kalleta.


“Ke kin san inda kike kuwa? Kin san wacece Hajiya Babba?”


“To ina ruwana, ai gaskiya ce ko a kotu zan fadi haka, idan ba ku yarda ba ku ba ni qur'ane na rantse”


“Bayan wannan kin san wani abu?”


Ammy ta tambaya


“Aa ban san komai ba”


“Idan kika min zan saka ayi miki mummunan hukunci”


Take hantar cikin fadimr ta kada hankalinta ya tashi, ta fara lalaben inda zata samu hannun Shattima ta rike.


“Wallahi ban miki karya ba, gaskiya na fada Allah shine shaidata, ko Shattima?”


Shattima ya kasa ce mata komai sai tunani yake, shi kansa ya tsorata da labarin bare kuma Ammy da ta kasa boye tashin hankalinta.


“Bayan shi fa?”


Fadime ta yi shiru tana nazari abun da zata fada jin ance za a yi mata mummunan hukunci.


“Akan Hajiya Babba ko akan Iya?”


Ta tambaya gudun kar ta dauko wani zance ta saba.


“Me Iya tai?”


Ammy ta tambaya daman bata manta zancen na dazun ba da take fadar wai kar a dauka ita ma mayya ce kamar iya.


“Iya ita kuma mayya ce, kuma ita uwar Wasim ce”


“Ya akai kika san Iya mayya ce?”


“Shi Wasim din daya kawo ni sai yacw ga ajiya nan na kawo miki idan kin ga dama ki cinye idan kin ga dama ki aje, kin ga kenan Mayya ce ko? Kuma yace kin ki amayar da kankarar maita kina cin mutane sai tace har yanzu bata ci kowa ba sai wanda ya shiga gabanta ya hana ta cikar burinta, tace wani mutu take bibiya ta cinye Matansa yanzu kuma yayansa take bibiya, har tana ta jin tsoro tana cewa an min aike ne yace a a, kuma har da wannan muguwar yarta tare suke maitar, kuma fa wannan Zainab din ashe ita ce na kai garin su Wasim, ta dauko hotuna saboda ita na makance fa, amman Wallahi Ammy baki ga wulakancin da take min ba”


“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”


Shine abun da Ammy take ta fada tana dafe da kirjinta sai Fadime ta kara rike kame rigar Shattima ta rike. Ammy za ta yi magana Shattima yai mata alama da tai shiru da hannunsa sannan ya rika hannun Fadime.


“Tashi muje n kai ki gurin Jekadiya ta kula da ke zamu yi magana da Ammy”


“Ita ta kwarai ce, tsoro nake ji dan Allah karka kai ni inda zan cutu kaji?”


“Ta kwarai ce na santa na san halinta”


Yaja hannunta suka fita, falo ya fito da ita.


“Jekadiya”


Jekadiya ta mike tsaye da sauri ta nufo inda yake.


“Ga bakuwa ku zauna da ita a nan a kula da ita, duk abun da take so ayi mata”


“An gama toron giwa, Allah kara maka lafiya da imani”


Ta kama hannunta, Fadime ba dan ta gamsu da ita ba ta sake ta sai dan babu yadda za ta yi. Juyawa yai ya koma ciki, wannan karon a tsaye ya samu Ammy hawaye a sauko mata a ido.


“Shattima yarinyar nan mutum ce?”


“Mutum ce Ammy, zaki iya tuna lokacin da kika fadawa Ra'ees ya nemo min mata?”


“Ita ce yarinyar, ni ma ban san haka ba sai a haduwar ta farko, Ra'ees ya fada min ke kuma kika kara fada min”


Ammy ta zauna bakin gado tana kallon danta.


“Shattima muna cikin makiya, Me ka fahimta game da abun da take fada?”


“A zancen Iya yayi daidai da labarina mutumen da take bibiya wata kila ni ne”


“Ba wata kila Shattima kai ne ma, shiyasa ta tallata maka yarta, saboda ta san ita take cinye maka mata? Kenan ita ta cinye su Luma? Amman matar nan bata da imani”


Ammy ta lumshe ido sai ga hawaye ya sauko mata, daman gudun shiga irin wannan halin yasa shi boye mata sai gashi Fadime ta tono komai.


“Ashe akwai abun da Allah ya gani ya hana zuciyata natsuwa da ita, shiyasa tun farkon zuwanta na kasa samun kwanciyar da ita...”


Hawaye Ammy take babu kakkautawa, Shattima ya dawo kusa da ita ya zauna.


“Gudun sakawa kanki damuwa yasa ban so kika ji maganar nan ba”


“Irin wannan abun ba a boyewa Shattima saboda abu ne na daukar mataki, kana tunanin ido za a zuba mata tana cinye matanka da yayanka a kyaleta?”


“Hukunta ta zaki yi Ammy? Kina da wata shaida ne akan hakan? Maganar Fadime kadai bata isa hujja ba, kiran dana ayi ma Falmata ma ina son na kara bincikarta ne, idan ta tabbata hakan na san irin hukuncin da zan dauka ta cikin ruwan sanyi”


“Muna zagaye da makiya, daga kai sai Nana Allah ya ba ni, kuma ake son a hana mu samun farinciki a kawarmin da kai alala rayuwar Nana mi nai wa Hajiya Babba? Me na tsare mata? Miyasa zata min haka? Ba ni kadai ba har da Mai Martaba? Mijinta uban yayanta?”


“Nana ta fada jiya, a lokacin da aka rufe Sardauna ita sa aka juya case


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login