Showing 216001 words to 219000 words out of 273152 words

Chapter 73 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72712

da yayanki”


Iya ta fada tana zaro manyan idanuwanta masu mugun ja da mummunar fuskarta da bata da kyau gani.














WASIM POV.


Ya mike tsaye yana kallon Kakansa.


“Har tsawon wane lokaci za ka dauka kamin ya bar yarinyar can ta samu lafiya?”


“A kullum fata na ke mata na samun lafiya, ku dai zan tambaya sai yaushe za ku kyaleta ta samu lafiya?”


“Sai ranar da k yardar ka bi umarnin mahaifinka, kuma ina mai tabbatar maka tana daf da rasa idonta gaba daya, domin mutumen da aka hannatawa ita daf yake da taba idonta, kuma ka san makomar hakan matukar ya taba idon ba za su taba dawowa ba, hakan kuma ba zaka mu bar ka ka aureta ba, domin ba zaka taba auren wanda ba jininmu ba”


Wasim ya koma ya zauna hankalinsa a tashe, domin ya san dukan abun da Kakansa ya fada masa abubuwan da ya riga ya gani ne.


“Kana wahalar da ita ne kawai, domin tuni ta taba hannun wacan dan Sarautar da yake haukan nemanta kuma ta ji sanyi”


Wasim ya dafe kansa da mugun karfi kamar zai cire kan daga jikinsa, zuciyarsa ta shiga bugawa da karfi, daman abun da yake gudu kenan shiya saka shi kasa taba hannunta tun a wacan lokacin, tsoronsa daya kar ya taba bata ji sanyi ba. Ya daga kansa ya kalli kakansa hawaye masu zafi na sauko masa.


“Kaka ka sani ina son ta”


“Kana sonta kake bari tana cutuwa? Ka nisanta da iyayenta? Ka kaita inda aka gusar da hankalinta? Kuma ka saka take kokarin rasa idonta? Wanda kake so za kai masa fatan samun farinciki ko kuwa farincikinsa na nufin bakincikinka ne”


Ya lumshe ido yana jin wani irin kalar yanayi da be taba jin irinsa ba, yana tuna kalaman Zainab.


“Wani lokacin dole ne mu sadaukar da farincikin mu saboda wadanda mu ke so su samu farinciki...”


Kansa ya daga sama sai ga hawaye sun sauko masa ta gefen idon, wani irin zafi da radadi yake ji idan yai yunkurin tunanin rabuwa da Fadime.


“Rabuwa da Fadime ba shi yake nufin na auri Liya ba, kuma ba zan taba barinta ta samu farinciki ba”


“Kana da damar auren wanda kake so matukar jininmu ce, amman wacan yarinyar idan za ka kashe maza dubu ka zata yi mu'amala da su, ba za ta taba aurenka ba”


Hannunsa ya daga sama ya daki tsakiyar kansa da dukan karfinsa ya rufe ido yana girgiza kai. Mikewa yai tsaye yana wani irin huci kirjinsa har wani sama yake kamar sai yi tsalle.


“Zan rabu da ita, amman sai na taba mutanen da suka taba ta, sai sun shiga kunci fiye da ita”


“Wannan kuma aikin duna ne, zan zan nemo shi... Na ka aikin ka tafi gurin shugaba ka fada masa ka yarda da dokinsa, ni kuma zan bude idanunta”


Kakansa ya fada da yarensu, sai Wasim ya kalli inda Fadime ta ke yawan zauna a lokacin da ta zauna dakin kakansa. Matse hannayensa yai yana jin rabuwa da ita kamar fitar rai ne daga jikinsa, kai ya girgiza ya koma ya zauna.


“Ba zan iya ba, wata kila ka fada min haka ne saboda ku cin ma burinku a kaina”


Kakan yayi murmushi.


“Lallai kana sonta sosai tun da har ka iya karyata ni, amman bari mu gani daga nan zuwa jibi idanuwanta za su bude ne ko kuwa za su tabbata har a bada a rufe? Amman ka sani daga lokacin ni da kai babu abun da zamu iya yi domin dawowa da idanuwanta....”










HAJIYA BABBA POV.


“Amin wa'alaikissalam”


Ta amsa sallamar da Hajiya Zariya tai mata a yayinda ta kara kunnen a wayarta.


“Hajiya ina yini ya gida ya Mai Martaba da jikin”


“Alhamdulillahi”


Ta amsa cike da kasaita kamar ba yar'uwarta ba.


“Hajiya na ce ko Sirleem yayi aure ne ba a fada mana ba”


“Wane Sirleem kuma?”


“Sirleem dai na ki, na wuce ne jiya ta gaban gidansa da yake nan kusa da mu na ga mutane na fitowa na tambaya aka ce min walima ake wai Amarya aka kawo, shi ne abun ya ba ni mamaki na ce to ko anyi bikin ne ba a sanar mana ba”


Hajiya Babba ta aje farantin dankalin jos dake hannunta.


“Aa ai ke ma kin san ba zai yiyu ba, Sirleem yai aure ba ki sani ba, ko da ba a fada miki ba ai duk garin nan sai ya dauka, shi kadai ya rage min fa namiji, kuma aurensa da yar sarautar ai dole ne ma duniya ta sani”


“Ni kaina na yi mamaki, tun jiya abun ya tsaya min a rai ina ta son na kira dai ban samu dama ba, mutanen ma da na ga suna fitowa daga gidan ba wasu na azo a gani ba ne, ko dai haya ya bada gidan ne?”


“No gidansa da ke kusa da unguwarku ai yafi ko wane gida nasa kyau da tsaruwa, ba zai bada hayarsa ba, kuma bana jin zai arawa wani, Amman kin shiga cikin gidan kuwa?”


“Aa wannan dabarar bata zo min ba, ban yi wannan tunanin ba”


Shiru Hajiya Babba tai tana nazari.


“Zan bincike shi idan ya shigo”


“To Hajiya sai an jima a gaishe da su Kausar”


“Za su ji”


Hajiya ta sauke wayar cikin tsananin mamaki, anya ma kuwa gidan ne? Ta tambayi kanta sai dai bata jin Hajiyar Zariya za tai kuren fahimta domin ta san gidan ba ita kadai ba ma yawancin mutanen unguwar sun shaida gidan saboda tsaruwarsa gashi farin gida mai bakin gate sai daukar hankali, sai dai ba kowa ya san cewa na Sirleem ba ne sai daidaikun mutane yan'uwa da kuma wadanda suke kusa da shi sosai.
Tunawa da tai da zancen da yai mata shekaranjiya na cewar zai kwana a can saboda baya jin dadi da kuma jiya da yace mata yana son komawa can so that ya samu damar maida hankali kan harkokinsa yasa gabanta mugun faduwa. Har ta dauko wayarta ta kira shi sai kuma wata zuciyar ta hana ta, da sauri ta mike tsaye ta nufi inda mayafanta suke ta dauko farin gyale ta saka ta nufo gurin da aka jekara takalminta ta saka ta dauki jakarta tare da wayarta ta fito falo.


“Juwairiyya”


“Jurry bata nan”


Karima ta amsa.


“Ke tashi ki kai ni gidan Sirleem da ke 300 houses yanzu nan”


“Okay, amman Hajiya lafiya?"


“Ita na ke son na tabbatar”


Ganin yadda hankalin mahaifiyarta yake a tashe yasa tai saurin dauko mayafinta ta fito rike da makullin motarta, har suka saukon ta shiga motar mamakin abun da ya faru take, ko dai minene ta san abu ne da yake son sirri shiyasa ta zabi ta kaita a maimakon direbobinsu da suke gidan.
Suna isa unguwar Hajiya ta saka tai bakin nesa da gidan sannan suka fito suka taka da kafa har gaban gidan, Karima ta kwankwasa gate din sai mai gadin ya leko. Karima za tai magana Hajiya ta tari numfashinta


“Amarya na nan?”


“Eh suna nan Hajiya Bismillah ku”


Ya bude musu gate din, suka shiga ciki hango motar Sirleem da Hajiya tai ya fi komai kayar mata da gaba, Rima kam tana gefenta da mamakin jin abun da Hajiya ta fada, suka nufi hanyar shiga falon zuciyar Hajiya sai bugawa take kamar zata fasa kirjinta ta fito, sai da ta fara tura kofar ta ji ta a rufe bata ko tsaya duba inda door bell din yake ba ta kwankwasa. Jin shiru ba a bude ba yasa ta sake kwankwasawa. Sirleem ne ya bude kofar yana sanye da jallabiya milk color.


“Hajiya....”


Ya fada kamar wanda ya rude. Tura kofar falon tai ta wuce ciki falon, sai tai arba da abun da bata yi zato ba, wato Falmata tana sanye da doguwar rigar atamfa hannunta rike da dankwali, daga bakin Hajiya har hancinta da idonta kallon Falmata yake with shock, can kuma ta juyo ta kalli Sirleem baki sake ta nuna shi da yatsa, sai kuma ta kasa magana, ta sake juyowa ta kalli Falmata ta daka mata tsawa idonta na cika da kwalla.


“Me kike yi a nan?”


Falmata ta kasa cewa komai jikinta sai rawa yake, Sirleem yayi saurin nufar inda take yana kallon Hajiya.


“Sirleemmmmmm.....”


Hajiya ta kira sunansa daker sannan ta ce


“Dadiro kuke yi?”


“No Hajiya Subhanallahi, she's my wife”


Wife wife wife wife wife wife wife wife wife.... Haka kalmar tai ta maimaita kanta a kunnen Hajiya, nuna shi tai ta nuna Falmata sai kuma ta nuna kanta kamin ta fadi kasa zaune saman tile din. Sirleem na ganin haka yai saurin kama hannun Falmata suka fice daga falon cikin sauri, motarsa ya nufa da ita Rima ta bi su da kallon mamaki ido bude. Sai da ya taba motar ya ji a rufe, sai ya rasa yadda zai yi baya son komawa ciki saboda zuciyarsa na raya masa Hajiya zata iya cewa sai ya sak Falmata a take. Hannunta ya kama be ko kula da dankwalinta dake hannunta ba suka fice daga gidan gaba daya, Falmata kuka kawai take jikinta na rawa kamar mazari. Suna fita su kai sa'a da Napep, cikin sauri Sirleem ya tare Napep din dake tare da wata mata suka shiga, yana fada masa inda zai kaisu.


Sai da suka bar unguwar sannan Falmata ta lulluba dankwalin da ke kanta, mai Napep kam sai mamakin wanda ya dauko yake a zahiri dai fuskar Sirleem yake gani fitaccen mawaki sai dai ba shi da tabbacin shi din ne ko waninsa. A gaban gidan Momy ya sauke su Sirleem ya fito yana fadin.


“Jira ni ina fitowa”


Ya buga gate din gidan mai gadin na budewa yaja hannun Falmata suka shiga ciki, yana isa bakin kofar falon Momy ya buga kofar da mugun karfi, hakan yasa Momy tai saurin budewa hankali tashe. Ganin Sirleem da Falmata ya bata mugun mamaki.


“Sirleem”


“Momy dan Allah ki boye min yarinyar”


“Lafiya?”


“Dan Allah ki boye min ita yanzu yanzu, zan dawo ki saka a daki ki kulle dan Allah kowa ya zo karki fito da ita”


Momy ta nuna Falmata da mamaki.


“Wannan ba Falmata ba ce?”


“Ita ce Momy please ki boye min ita”


Ya fada cikin tashin hankali, saurin kama hannun Falmata tai ta shiga da ita ciki shi kuma ya juya ya koma, upstairs Momy ta nufa da Falmata da ke kuka ta bude dakin Ameer ta saka ta ciki ta rufe ta makulli ta sauko kasa da mamaki kala kala.
Bakin kofar dakin Falmata ta zauna ta fashe da wani irin kuka marar misaltuwa, sai ta ji kamar bata taba fuskantar tashin hankali irin wannan ba, kuka take sosai tun tana yi ba sauti har sautinta ya fara fitowa, kuka tai bana wasa ba har sai da idanuwanta suka fara kumbura, hawayen suka daina zubo mata. Mikewa tai tsaye tana goge idonta da dankwalinta, kamar ance mata juyo ki kalli gefe, tana juyowa sai tai arba da wani tsohon hoton mahaifiyarta, an fadadashi har ya kusan tsawonta, an ajeshi a tsaye yana fuskantarsa, mutuwar tsaye tai tana kallon hoton with shock.






_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:59 - 🤐🤐🤐🤐: *Khadeeja Candy*




Da farko ya tsorata sosai zuciyarsa ta raya masa aljanunta ne suka taso, a hankali ya kara karanta mata ayatul kursiyo yana tofa mata a kai a hankali, sai ta zabura ta mike tsaye tana ta kalle kalle baki har kunne can kuma sai ta rufe idon tana dariya.


“Yasmin?”


Ya kira sunanta a hankalin bayan ya mike tsaye, sai ta bude idon ta juya bayanta ta ga wanda ake kira da Yasmin din, ganin babu komai a bayanta sai gina yasa ta juyo kalletashi, sai ya sake kiranta.


“Yasmin”


A nan ma juyawa tai kamar dazun ta duba bata ga kowa ba, sai ta juyo tana ta taba jikinta da fuskarta, A tunaninta ko ta canja kamanin ne.


“A ina nake?”


Ta daga kai tana karewa dakin kallo, a nan ta fahimci asibiti take.


“Taba min idon akai? Ai dai Wasim yace kar a taba idon, yace idan aka taba ba zai bude ba har a bada na shiga uku”


Ta fara kirkira kuka, a tunaninta aiki akai mata idon ya bude, shi dai Muhseen kallonta kawai yake ba dan ya fahimci yarenta ba, ba wai hausar ce baya ji ba, no the way da take maganar ne be gane komai ba.


“Waye kai? Waya kawo ni asibiti?”


Ta tambaya tana jin kamar ta dade tana bachi. Ya nuna mata kujera.


“Zauna”


Sai ta zauna tana murzar idon dake mata kaikayi, kuma tana jin kamar haske ya mata tawa.


“Ya sunanki?”


“Fadime a kauye, a birni Fateema”


Dan mamaki ne ya kama shi sai ya gane da gaske a hayyacinta take, amman abun mamakin dawowar tunaninta da idanuwanta a lokaci daya kuma a take kamar abun aljanu.


“Ina ne garinku?”


Ta yi shiru tana kallonsa, sai kokarin tuna abun da ya faru take.


“Laaa na tuna daga na gama cin abincin zan wanke hannuna sai na gan ni a nan me ya faru to? Waye kai? Ina Shattima da Bappa?”


Ya daga kafadunsa yana mata kallon ban fahimce ki ba.


“Daga wani kike?”


“Katsina, a katsina a kaita, a kaita a garin, kaita a bandalo, amman wani sarauyina Wasim wadan yake a garin Garuk ya kawo ni a garin Yola gurin wata mayya yace ta ga ajiya nan na kawo miki idan kin ga dama ki cinye idan kin ga dama ki aje....”


Shi dai kallonta kawai yake ba dan ya fahimce wani abun ba, sai ta sake komawa can baya ta dauko asalin yadda komai ya faru ta fada masa har zuwan su Bappa da tafiyar da za su yi a gobe.


“So Shattima na Yola kike magana kenan? And Iya mahaifiyar Hajiya Karama kenan?”


“Aa ba Hajiya Babba ba, ita wacan Zainab ne sunanta ai”


“Eh haka ake kiranta”


“Kuma na je zan wanke hannu sai kawai na gan ni a nan, amman dai wani abun kuka min nai bachi ko?”


“Aa wani brother na ne ya tsince ki a titi yana tare da matarsa, Aliyu da Ataa”


“Minene Ataa? Tsuntsu ne?”


Ta tambaya a bakin gaskiyarta domin ita bata fahimce mutun ne Ataa ba. Muhseen be san lokacin da dariya ta zo masa ba.


“Matarsa ce, sunanta Aisha Ataa i think sunan buzaye ne”


“Okay to yanzu kenan ba waya kawo ni asibitin?”


“Ni ne”


“To ina Shattima?”


“Nan ba Yola ba ne, kina Abuja ne, and you got lucky Shattima is my cousin”


“Abuja kuma? Na shiga uku? Waya kawo ni Abuja kuma? Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un”


Ta dafe kanta.


“To ko Wasim din ne ya sake kawo ni? Ina ne Abuja ma?”


Kamin Muhseen ya ce mata komai wayarsa tai ringing, sai ya nufi wayar dake saman tebur ya dauka, at first ya dauka Mama Fulani zata tambaye shi ya jikin yarinyar sai dai yana picking sai ya ji wani mummunnan labari.


“Muhseen yanzu aka kira ni, wai Maijidda ta rasu”


“Wace Maijidda?”


“Yar wajen Waziri Diyar Hajiya Talatu”


“Innalillahi Wa'inna ilaihirraji'un, yaushe?”


“Yau, ni ma yanzu Ammy ta kira ni sai kuka take”


“Allah ya mata rahama, yaushe za ki je?”


“Gobe tun da safe Inshallah”


“Allah ya kai mu, ni ma gani nan zuwa yanzu”


Ya sauke wayar cikin rashin jindadi daman can sanarwa mutuwa ba ta yi ma mai hankali dadi.


“Dan Allah ka kira Shattima ka fada masa ya fadawa Bappa ina nan su zo su tafi da ni”


“Rasuwa akai musu ba zan iya kiransa a yanzu ba”


“Waya rasu? Allah yasa ba Iya ba ce ta sake cinye wani”


Muhseen ya mata kallon tsaf ita ko ta sako masa ido tana son jin amsarsa idonta kamar za su yi magana.


‘It can be possible, kai no... Be kamata ya yarda da zancen yarinyar nan ba, daga ganin yadda take da surutun nan za ta yi karya’


Ya fada a ransa.


“Dan kawai kin ji labari haka sai ki ce Iya mayya ce kin san shekarunta a idan nan?”


“Ko ma dai wacece Wallahi mayya ce, kuma ka tambayi Shattima idan baka yarda da ni ba shi ya yarda da ni”


Be ce komai ba ya zauna yana ta kallonta wata zuciyar na raya masa duk yadda akai aljanu ne suke dawainiya da ita ko kuma ma aljanar ce maybe. Baya son kiran Shattima a irin wannan lokacin amman ya zame masa dole ba dan ya labarta masa komai ba sai dan ya tambaye shi. Few seconds wayar tai tana ringing ya daga ba tare da yace komai ba, domin har ga Allah yana cikin damuwar da idan ma ya dauki wayar be san abun da zai fada ba.


“Shattima”


“Muhseen”


Ya kira shi yana shafa fuskarsa cike da damuwa.


“I know mun rasa Maijidda be dace na zo da new thing ba yanzu, amman tambayarka kawai zan yi”


Shattima yayi shiru be ce komai ba, wanda hakan ke karantar da Muhseen cewar ya ba shi izinin magana kenan.


“Wata yarinya muka tsinta day before yesterday, tace sunanta Fateema kuma ta... ”


Muhseen be gama ba Shattima ya mike tsaye da sauri rike da wayar.


“A ina kuka ganta? Tana kusa da kai? Bata wayar”


Shattima ya fada har kalaman na hade masa, Muhseen ya saka wayar a speaker ya mikawa Fadime, sai ta ta so ta amsa ta kai a kunnenta.


“Hello Assalamu Alaikum”


Shattima ya lumshe ido tare da saka hannunsa yana taba hancinsa.


“Shattima Fadime ce...”


A hankali ya hade yawun bakinsa sannan ya ce.


“Fateema ina kika je?”


“Ni ma ban sani ba, shi wannan mutumen...”


“Muhseen”


Muhseen ya katseta tare da fadar sunansa.


“Muhseen ya ce wai ina nan Abuja kai ka kawo ni?”


“Ba ni na kawo ki ba”


“Amman ai yace shi dan'uwanka ne”


“Ba ni a kawo ki ba, nemanki kawai mu kai mu ka rasa but


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login