Showing 270001 words to 273000 words out of 273152 words

Chapter 91 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72779

kirjinsa sai dariya yake amman yaki bari ta gani.


“Fada min waya kawo ki?”


“Direban gidan”


“Ya kyauta, tashi ki yi sallah ni zan tafi masallaci”


“To”


Ta daga jikinsa shi kuma ya mike tsaye yana sumbantarta.


“Se na dawo”


Ta bishi da kallo tana jin haushinsa daman tun da cikin ya tsofa take ta jin haushin mutane, ko ido aka kura mata sai ya zama laifi, sai kuma takalar cikin take idan bata ji motsinsa ba sai ta hannu ta rika laguda tana takalarsa, idan kuma ya motsa mata da karfi sai tace ya taba mata hanji ta fara kuka tana cewa ciwo.
Haka dai Shattima yai ta fama har ta wuce kwanakin haihuwarta da kwana biyu sannan ta fara nakuda, a nan ta gane ashe wacan ciwon duk sharar fage tai yanzu ne na gaske yake tafe, idan marar ta murda mata sai ta ji kamar ba a duniya take ba, tun kamin ta shiga watan haihuwarta Shattima ya shirya mata komai na haihuwa a gida, har sai idan abun ya garara tukuna ya tafi da ita asibiti, sai dai baya barinta ita kadai idan zai fita hadimai za su zauna da ita saboda bukatu na yau da gobe da kuma gudun wata matsalar.
Ihu babu kalar wanda batai ba tun tana da kuzarin ihun har ta koma ta na ambaton Allah, tana fadin ba zata sake haihuwa ba.


“Ba zan sake haihuwa ba har abada, har abada ba zan sake haihuwa ba”


Shattima ya zo kusa da ita ya kwanto yana shafa kanta


“Pushhhhh”


Sai ta buge masa kai.


“Ba zan yi ba, pushing din ba, ai duk kai ne kai yi kai ka ja min, wayyo uwata wayyo ubana, Wallahi ba zan sake haihuwa ba”


Ya tsorata sosai a lokacin da ya ga ta daina unkurin yin nishin gudun kar ta kashe masa abun da ke cikin cikinta. Sai da yai da gaske sannan ta ni wani karfi ya zo mata daga gurin Allah yai nishi dai yunkuri sai ga kai ya fara fitowa, tanayin na biyu sai Shattima ya saka hannunsa ya janyo baby yana murmushi da hawaye a lokaci daya, ya saka alkamshi ya yanke cibiyar, ita ma a lokacin ne ta samu damar yin kuka mai hawaye domin a can da kukan kawai take ba hawaye, sai ta ji wani shauki yana ratsata babyn dake hannun Shattima sai kuka take tana jin kuka har cikin ranta, Shattima ya lullube ta da zane sannan ya sumbance ta ya kwantar mata da ita a jikinta.


“I love you so much”


Ya fada yana kissing din Fadime, hawaye na sauko masa, ita ma hawayen take tana murmushin da bata san ta ina yake zuwa mata ba, saboda joyful na uwa.


“Wa ta biyo? Mace ce ko Namiji?”


“Mace”


Ya fada yana shafa fuskarta, a tunaninta shikenan tun da ta haihu duk zancen da Shattima yake mata cewar yan biyu ne bata yarda ba a tunaninta yana mata wasa ne saboda ya san tana son yan biyu, sai da ta ji wata nakudar ta taso mata ta musamman, sannan Shattima ya fita ya bada Babyn wa mutanen da suke falo aka fara karba karba ana yabawa, shi kuma ya shiga wani sabon aikin, da taimakon Allah ta sake santalo danta yana kuka kamar yadda mace take. Za ku ga murna gurin Shattima kamar yanzu ne ya fara samun haihuwa.


Sai da ya gyara matarsa ya kwashe komai sannan ya shiga bandakin da ita ta gyara jikinsa ya fito ita kuma Jekadiya ta shiga yi mata nata aikin na kula da jikinta.
Da kansa ya buga ya fadawa Ammy da Inna cewar Fadime ta sauka, Inna sai ta ji kamar tai tsalle ta tafi, tana ta mamakin yadda akai Fadime tai iya karfin halin haihuwa domin ta san yarta da raki, gashi bata da halin zuwa domin Fadime kamar yar fari take a gurinta kuma kunya da al'adarsu ta fulani ba zata bari ta tafi ba, sai dai kenanta aka tura da wata yar uwar Bappa.
Hankalinta be kwanta ba har sai da ta ji muryar yarta a waya tana labarta yadda akai ta haihu.


“Inna da kaina na haihu Wallahi, amman akwai wuya ba zan sake ba, Inna haka kika ji kema”


Inna ta yi murmushi idonta na cika da kwalla. Sai kuma Fadime ta fashe da kuka farinciki.


“Inna na zama uwa... Nima na zama uwa....”


Inna ta lumshe ido hawaye na sauko mata.


“Allah ya baki ikon tarbiyantarwa, ya raya miki su yasa masu jinkanki ne”


“Amin Inna, ke ma Allah ya saka miki da alheri dawainiyar da kika yi da ni da rashin da na yi miki Allah ya biyaki da aljanna”


“Ameen”


Shattima ya shafa fuskar matarsa yana jin kamar ya hadeye ta tsabar kaunarta da yake. Gurin ba da nono sai ido ya raina fata ashe a nan ma akwai wani zafin ba haka nan kurun ake bawa yaro nono ba, sai an yi da gaske sannan take shayar da yaran.
Wani irin kula da tarairaiya ake bata kamar akanta kadai aka fara samun jika a masarautar, domin kwananta daya aka rabota da gidan Shattima aka dawo da ita masarautar, duk yadda Inna ta so ta ki zuwa bata samu hakan ba domin Ammy ta matsa mata kuma ta aika musu da komai na zuwa, ganin Ammy an wuce wannan karnin da ake cewa uwa tana kunya sosai da har zai hanata zuwa bikin yarta, bayan kuma babu abun da ya tafi so a wannan lokacin kamar gatan mahaifiyarta.
Irin wulakancin da akai ma nera a ranar suna sai ka rantse da Allah daga sama ake jefo musu kudi, domin bidi'ar da kai a gurin sunan ba ayi irinta ba a gurin aurensu, namijin aka saka masa sunan Mai Martaba Abdallah, mace kuma ta ci sunan Inna Aisha, sai dai dukansu ana musu lakani da Ameer da Ameera.




ZAINAB POV.


bata dauka da gaske Wasim yake ba har sai da ya fada kuma suka amince masa cikin sauki, ganin cewar ba tafiya zai yi gaba daya ya bar garin ba, zai tafi a inda zai fi jindadin rayuwa ne fiye da nan, kuma ya karbi addinin da zai fi samun natsuwa da shi fiye da wacan na kakanni da iyaye.
A lokacin da za su bar garin ita ta rika jin kewar garin da mutanen cikinsa, shi kan be ji komai ba domin ya saba yin nisa da garin dama kuma ya san ba wai tafiya ce ta har abada ba. Sai da be nuna musu zai aje tsafinsa ba wannan ya bar shi a zuciyarsa ne kuma a tsakaninsa da Zainab sanin cewar Familynsa za su iya kin yarda domin sun fi girmama tsafinsu fiye da addininsu.
Garin Sokoto shine gari na farko da ya fadowa Zainab tun a lokacin da take tunanin garin da ya kamata ta zauna, bata san kowa a garin ba, amman hakan be hana ta zuwa ba, sai suka sauka a Hotel, iya kar kokari ta yi na ganin ta kare mutuncin addininta hakan yasa ta kama musu daki biyu ko wanne daban dabam. The following day after ta samu ma'aikatan hotel din tana tambayar ko akwai inda zata samu wata kungiya mai taimakawa musulmai haka a garin sokoto? Wasu suka fada mata hukumar zakka dawakafi sai dai yadda aka labarta mata Famwan da irin ayukansu sai ta ji hankalinta ya fi kwanaciya ta da ita, sai da tai magana da Wasim ta fada masa zata je ta dawo sannan ta karbi addiress din inda cibiyar kungiyar take, ta yi sa'a a lokacin shugabar na nan, da ta fadi dalilinta na zuwa sai sukai mata maraba suka karbeta hannu biyu suka gabatar mata da komai cikin har da yadda zata agabarta komai kamar yadda shari'a ta tanada, kana suka jinjina mata, sai dai ta nuna musu bata son kowa ya san abun kasancewar sananniya ce a media.
Duk wani abu da ya kamata kungiyar ta yi mata, aka hada Wasim da manyan malamai da suka gabatar masa da komai na musulunci ya karbi kalmar shahada kuma suka karanta masa cewa ba a hada Allah da wani abu gurim bauta kamar tsafi ko kuma wani ubangijin na dabam. Shi kansa a lokacin sai da yaji wata rahama da natsuwa ta lullube shi da be taba jin irinta ba, natsuwar ruhi da jiki da kamala ta addinin musulunci.
Ita da kanta ta bukaci mutanen da za a hada ta da su ta siya makanta gida a cikin garin albarka garin sokoto, sai suka hada ta da adalilan dillalai akai ta nuna mata gidaje har ta samu wanda ya kwanta mata a unguwar Clapperto road, ta siya gida mai kyau kusan 50million.
Kungiyar ta dauki kudi mai kauri ta bata, da shi Zainab ta kara ta saka duk wani abu da zata bukata a gidan daidai karfinta, washe garin ranar aka daura musu aure a babban masallacin jumma'a na isa talatar mafara. Tun daga lokacin sai Zainab ta koma da zama a gurin daya daga cikin matan da suke fanwan din saboda kula da ita, sun yi mata duk wani hallaci da ya kamata, ciki har da alkawarin samawa Wasim sana'a kasancewar be yi karatu ba.
After a month sa tarewarta ta koma Yola ta saida gidanta ta dauko motarta ta dawo sokoto ta bude shagon kasuwanci na siyarda tufafi da duk wani abu na sakawa kama daga na zama har na mata, katuwar plaza ce ta kama haya ta cika ta da komai na kawa, kuma ta cigaba da sana'arta ta daukar hoto da karbar tallar kamfanona har tai nasara kamfanin Glo suka bata ambassador.
Sannu a hankali Wasim yake koyon komai na addinin, tun yana jin wuyar wasu abubuwan har ya soma sabawa, sunansa ma da ake kiran da shi Muhammad tun a lokacin da ya musulunta sai daga baya ya soma sabawa da shi, da fari idan an kirashi haka baya amsawa sai ya ji kamar ba shi aka kira ba. Sai dai yawan zama da yake a shagon Zainab da ke gawon Nama yasa ya soma sabawa da sunan da kuma mutanen dake kula da shagon, shi kuma yana a matsayin manager ta.
Ba shi kadai rayuwarsa ta canja ba, har da Zainab domin a yanzu ta daina shigar banza da take da magana any how, ga sa'ido akan Wasim da take sosai saboda yadda yan mata suke kawo masa hari idan ya fita, kasancewarsa mai jini a jika gashi kyakkyawa kamar shi yai kansa fari kamar a zaga jini ya fito, sai wani kara fresh yake saboda yana samun hutu da jindadi a yanzu ga safiyayyen gurin bachi da abinci mai kyau ga sutura idan ya saka ya fito sai yai kamar wani balarabe.
Shi kansa yana kishinta kuma yana tayata kare mutumcinta, musamman a yanzu da take kokarin zama uwa, wani abun har shi zai tuna mata cewar addinin musulunci ya hana, domin yana yawan sauraren wa'azi an every night sai ta tafi masallacin dake can kusa da gidan sidi mamman gurin karatu, yana koyar komai a hankali duk da kasancewar ba komai yake ganewa ba, musamman idam yace zai hada harufan arabi ya karanta sai ya ji abu ya masa nauyi but Alhamdulillah tun da yana fahimtar addinsa.










*AFTER FIVE YEARS...*


Hakika rayuwar dan'adam tana cike da kalubale na rayuwa kala kala, wala'alan kana cikin jindadi ne ko akasin haka, dole ne akwai daci akwai bakinciki a wata rana, sai dai idan an yi hakuri da sannu komai yake wucewa, kuma duk abun da yai farko dole ne cilas tai karshe, sai dai be zama lallai karshen yai dadi ba, kuma ba dole ne karshen ya kasance marar dadi ba. Waya tsammaci rayuwa zata kawo Zainab da Wasim a haka? Balle Falmata da Sirleem? Haka ma Shattima da Fadime? Ba su kadai ba har Aliyu da Ataa Muhseem da matarsa suna gurin, Mama Fulani ma tana cikin yan'uwanta.
Babu wanda yai tsammanin wata rana zata zo da sukansu za su hadu akan abu daya, ita kanta Zainab ta cire rai daga waiwayar rayuwar Shattima da Ammy, sai dai yadda suka samu labarinta suka kira a waya suka nuna mata nuna tare da ita har yanzu sai ya sa ta ji sanyi ta wani bangaren, shi kansa Wasim be tsammaci wata rana biki zai hada shi har ya ga Fadime da yaranta ba, ita ta ganshi da yayansa har biyu, kamar yadda bata tsammaci wata rana zata zauna a kujera kusa da kusa ba ita da Falmata. Dukamsu sun ci ado kamar ba a mutuwa, kallo daya za ka musu ka san suna cikin farinciki da kaunar junansu, gaba dayansu hankalinsu ya tafi gurin tafin da ake sakamakon fitowar amarya da ango cikin takun kasaita, Nana ce tana sanye da doguwar riga da farin mayafi dan karami kamar yadda rigar jikimta ma take fara sol. Sardauna kuma na sanye da tsadaddiyar shadda sky blue wanda ta karbe shi ta fito da kyaunsa, tsakanin shi da Nana sai ka rasa waya fi wani kyau da murmushi. Tafiya suke kamar wadanda basa son taka kasa, har suka isa gurin da aka tanadar musu suka zauna. Sannan kowa ya mike tsaye har su akai national anthem, kana Mai Martaba ya fara zaunawa Ammy na gefensa, gefenta kuma matar gobna ce, sai Governor da kansa a gefen matarsa, sai kuma manyan mutane da wakilansu.
Mc ya mike tsaye yana ta gabatar da komai, ba ayi wata riya ba, sai dai bikin ya kayatar domin ayi gayyato masu nishadantar kala kala suka kayatar da bikin. Sai kusan 11 aka rufe taron da addu'a sannan kowa ya nufi gida wadanda aka tanadarwa masarauki kuma suka sauka a masaraukansu.
Washe garin ranar ya kama Sunday ranar za a kai Amarya Nana dakin angonta Sardauna, daman sun Friday aka daura auren Saturday akai Walimar dare bayan ayi sauran bukuwan da mata suke yi kuma bukukuwan al'ada.
A hankali take saukowa da shirinta tana kallon mijinta dake dafe da waya a kunne yana dariya, kana gani kasan yana cikin nishadi.


“Da wa kake waya?”


Ta tambaya bayan ta zauna kusa da shi, a lokacin da ya gama wayar.


“Mansura..”


Dassss ta ji gabanta ya fadi.


“Mansura fa ka ce?”


“Yes”


Ya fada try to kiss her neck sai ta ture shi.


“Miye hadinka da ita?”


“Easy easy Mom Nu'ayn ta fa yi aure har ta haihuwa”


“Yaushe?”


“An dade tun a lokacin da na haihu ta ce ta fahimci da gaske ba zan aureta ba, maybe ta yi duk abun da zata yi ta kasa ne, yanzu haka tana garinsu ma”


“Amman kake waya da ita kasan matar wani ce? Amman ni nan har fada min kake ko malamai na baka yarda nai musu magana ba sai da babban dalili, ashe ba dadi”


Yayi dariya yana rungumota.


“Eh kuma kika wasa sai na hana karatun gaba daya, dan ba zan yarda ana kalle min mata ba ana magana da ita ana jin zakin muryarta”


“Amman kai kake yi da matar wani?”


“Wallahi ban taba kiranta ba ita take kirana, kuma zan daina dauka daga yau inshallahu”


“Da dai yafi maka”


Ta fada a fusace tana jin wani bakin kishi na turniketa. Sai ya riketa yana dariya ya rumgume.


“Kin yi kyau, jiya kin ga yadda ake kallonki wai? Gaskiya idan za'ayi bikin su Kausar Hijabi za ki saka”


Ta watsa masa harara.


“Amman kai da akai bikin Rima da yan mata suna kallonka ai zuwa kai ka fada min wai yan mata sai kallonka suke”


Ya saka dariya yana kara rike a kokarin da take na ta zame daga jikinsa.


“To ai ni namiji ne, hudu aka ce na yi, ke kuma kin auru”


“Au haka ma zaka ce? Shikenan bari Allah ya kai mu bikin kaga yadda zan yi ado, ai yanzu Aymana da Nu'ayn suna gurin Momy ba mi case ko gyale ba zan saka ba, kuma duk wanda ya tare ni tsayawa zan yi”


“Aiko da da an yi bu**uba... Ni din za a tari matata a kwana lafiya a Yola?”


Ta yi dariya tana Kwantowa jikinsa kamar yadda shi ma yake dariyar.






END....!




Ni kuma na yi murmushi na ce Alhamdulillah da Allah ya nuna min farkon da kuma karshen littafin Fulani lafiya, Allah ya yafe min kuraren da nai darasin dake ciki Allah ya ba mu ikon amfana da shi.


Na sadaukar da littafin nan ga mutane uku masu daraja.
Safiyya Dan Jumma (Ummul Falsak)
Asma'u Badamasi (My Asmee)
Salma Gidado (Salwees)
Ina sonku ina kaunarku har cikina raina, Allah bar mu tare har aljanna, kada Allah ya ba shaidan damar shiga tsakaninmu.


Ba zan manta da ku ba, Mama Aisha Samaru uwata ta kaina uwata maganin kukana i love you. Mamana
Maman Hafiz, Mama Hajiya Zainab Kano, Aisha Maccido, Hadiza Mai Fata. Rahama Kabir, Mrs J Moon (Mu ne yan uku lol).


Godiya ta musamman gare ku wadanda suka siya littafin nan, har muka kawo yanzu i love you irin sosai din nan idan babu ku babu ni.


Sai kuma idan mun sake tarayya da ku a littafi na gaba, idan mai komai mai kowa ya yarje mana mai suna BAƘAR WASIƘA. ina rokon yafiyar wanda na batawa rai cikin ganganci ko rashin sani, ayi hakuri a yafewa Candy dan'adam ajizi ne.




*** *** ***


*BAƘAR WASIƘA...!*
_Mai farin rubutu_




Ban ce tafiyar mai sauki ba ce.
Ban muku alkawarin zallar soyayya ba.
Ban ce babu farincikin ba.
Kunci, bakinciki da damuwa, sune abubuwan da suka taru suka tare farincikin AMINATU, kalubalen rayuwa bayan wata rayuwar, tabbas akwai kuka akwai damuwa da bakinciki.



Labarin Tafida, Rafi'a, Laila Sudais da kuma Aminatu. Labarin BAKAR WASIKA, labari ne da zai tabo wani bangare na rayuwar mace, kuma wani bangare na rayuwar al'ummarta da iyayenta...
Ina fatar zaku karbe


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login