Showing 177001 words to 180000 words out of 273152 words
Chapter 60 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt
din zuwa kisan kai, Nana tace ta ji tana waya tana fadar sai kin shiga damuwa kuma sai rayuwarta ta lalace ba sata ba har abun da yafi sata sai ta yi”
Ammy ta kalli Shattima cikin tashin hankali tana jin kamar kanta ba zai Iya daukar maganar ba.
“Nana bata fada min wannan ba...!”
“Ta ce baki saurarenta ba kina cikin fushi da ita saboda abun da ya faru, wannan kadai ya isa ya saka na yarda da maganar Fadime, tana son a rufewa Nana baki saboda kar ta fadi maganar ne, wata kila kila kuma Sirleem ne take son a saka mata soyayyarsa, ni daman na gani kuma zuciyata ta ayyana min Sirleem ba son Nana yake ba, domin baya bata irin kular da ta dace”
“Allah sarki Yata... Ina ta tsanarta ina jin kamar nai mata baki, saboda irin abubuwan da take, ashe ba yin kanta ba ne, ban taba mata uzuri ba, saboda tana bata min rai...!”
Ammy ta fada hawaye na sauko mata, tana tuna lokacin da Nana take fada mata ta yi satar sarka kuma bata san dalilin daya saka tai ba, ta san be dace tai ba, hannunta ne yake mata kaikayi.
“Tana nuna mata so kamar uwa, har Nana tana ganin kamar tafi sonta fiye da ni... Muna cikin makiya, ina tunani da addu'ar Mai Martaba ya samu sauki amman Hajiya Balki nema masa mutuwa take tare da kai? Ban taba tunanin Hajiya zata iya haka ba, na san bata so, saboda kishi gaskiya ne, nima ina kishinta, amman Wallahi babu hassadarta a raina, ban taba jin kyashinta ba, ban taba mata fatan mugun abu ba, shiyasa ban kyamace ta ba a lokacin da danta ya nemi auren Nana wata kila da wata manufar ne”
Ammy ta dantse bakinta saboda kukan da yake son subuce mata.
“Shiyasa tai wa yarinyar Falmata sheri? Ashe wata manufar ne? Mutum abun tsoro, ita kanta Hajiya Talatu ban zata za ta iya haka ba, balle Jarma da yake kanensa, ashe zai iya cutarda dan'uwansa har a nemi rayuwarsa saboda abun duniya mai karewa?”
Shattima ya kalleta.
“Ammy dan Allah karki saka damuwa a ranki, Allah yana tare da mu, kuma ya ga zuciyarmu babu wannan cutar a ciki, wata kila shiyasa ya bayyana mana komai cikin sauki kuma ta hanyar da ba mu yi zato ba”
Ta rumtse idonta hawaye na sauko mata, kamar ba gobe. Shattima ya kalli agogon hannunsa.
“Karfe 10 jirginmu zai tashi, ina son na koma Katsina na fadawa iyayenta halin da ake ciki, zan bar ta a nan, Ammy sai kin yi hakuri da halinta kuma Idan aka fadi wata magana a gabanta tana recording ne”
Ammy ta bude idonta ta kalleshi still hawaye sun ki daina sauko mata.
“Allah yai maka albarka Shattima, Allah ya kareku daga dukan shari, yai muku mafita, dan Allah ka tsare addu'a sosai da sosai”
“Da bana addu'a wata kila da ban kawo haka ba, bana wasa da addu'a saboda bana son nai nisa da Ubanjigina, kuma inshallah zan kara dagewa... Ammy kar a gaji da ita tana da yawan requesting”
Ammy ta yi murmushi har lokacin hawaye be daina sauko mata ba.
“Karka damu, ko dan abun da tai mana za a kula da ita, balle kuma na lura tana da muhimmanci a gareka”
Yayi murmush ya mike tsaye, Ammy ta bishi da kallo har ya fice. Sai da ya kawo tsakiyar falon sannan ya kalli Jekadiya ya ce
“Fito da ita”
“To ranka ya dade”
Jekadiya ta riko hannun Fadime suka fito daga falon suka bi bayan Shattima.
“Ina zamu je?”
“Shattima ne yace a fito da ke?”
“Ina zai kai ni?”
“Wallahi ban sani ba, baiwar Allah”
Ta fadar Ammy Shattima ya bi hakam yasa Jekadiya ta bi bayansa har cikin fadar, tsaye ta same shi yana lasa waya da alama su yake jira. Jekadiya ta tsaya nesa da shi ta duka kasa tana jan Fadime ta duka.
“Jekadiya tafi zan kira ki...”
“To ranka ya dade”
Jekadiya ta mike tsaye ta fice da sauri, Sai da Jekafiya ta fice sannan Shattima ya juyo yana kallon Fadime fuskarsa dauke da murmushi.
“Kana nan Shattima?”
Yayi shiru be ce mata komai sai murmushi yake yana kallonta, wani gefen ta tafi tana lalabe sai ya bi bayanta yaja gyalenta sai ta juyo da sauri ta taba shi, hannayenta ta kai har kan fuskarsa tana lalabe, shi dai yana tsaye kamar hoto sai murmushi yake sakar mata kamar tana ganinta. Yatsanta na fada bakinsa ya cigeta kadan.
“Asshhh”
Ta dauke hannun da sauri. Sai ya matsa kusa da ita sosai yana kallon fuskarta.
“Zan tafi yanzu”
“Karka dade ka dawo anjima”
“Dole sai na kai gobe”
Ya fada a hankali yana kallon lips dinta. Kamar ta san yana kallon lips din sai ta mutsa su a hankali.
“Tau idan ka je sai ka dawo ka dauke ni ko ka zo da su ko?”
“Eh”
Ya kai bakinsa gefen fuskarta ya sumbaci kuncinta na baren dama.
“Ba zan yarda Wasim ya dauke min nishadi ba, kin min da abubuwa da yawa”
Yana fadar hakan ya kai hannunsa ya taba tafin hannunta, a take ta sake jin sanyi, da sauri ta janye hannunta tana turo baki gaba.
“Ni Wallahi bana son ka, Wasim nake so”
Yayi murmushi tare da kai hannun ja labban nata.
“You cute ji labbanki”
“Ka daina taba ni ba kyau tana matar wani”
Kansa ya daga sama yai dariya marar sauti sannan ya sauke kai ya kalleta.
“Me kike son na riko miki idan zan dawo?”
“Ni dai kyale ni”
Ta fada hawaye na cika idonta, maganar da yai sai ta ga kamar gaske ne, ita kuma har ga Allah Wasim take so.
Ta juya da sauri ta tana lalabe, sai ya kai hannunsa a hankali ya kama nata ya ja a hankali ya koma da ita hanyar da ta Jekadiya ta fito da ita, sai da suka kusa shiga falon sannan ya tsaya ya saka hannunsa ya share mata hawaye.
“Daina kuka Kanen mahaifina yayi min mata, wasa nake miki”
“Tau...”
Ta fada tana jin sanyi a ranta, sai ya sake murmushi.
“Kurciyarki na burgeni, i like you serious”
Ta yi dariya, da waya ya kira jekadiya ya zo ta kama hannunta. Sai a lokacin ya tuna da zancen Falmata.
“Ina Falmatan take?”
“Tana nan Falo ranka ya dade”
“Je ki kirata, saki wannan”
“To ranka ya dade”
Ta saki Fadime ta wuce da sauri, tsaye yai yana kallon Fadime fuskarsa da murmushi, haka nan yake samun kansa cikin nishadi da sakewar zuciya.
“Fateema ko?”
Ta yi dariya tare da saka hannayenta ta rufe idonta.
“To ba na zo birni ba”
Yayi murmushi yana kallon fuskarta sai lumshe ido yake, Falmata ce ta shigo tare da jekadiya suka zube kasa, take Shattima ya hade fuska kamar be taba murmushi ba. da hannu yai ma Jekadiya alama da ta tafi, sai ta mike tsaye ta fice.
“Ya sunanki ma?”
“Falmata”
Ta amsa da sauri tana sanda kai kasa.
“Zan tambaye ki wani abu, kuma gaskiya nake son ki fada min”
“To ranka ya dade”
“Kina ganin wata alama a gurin su Labib?”
“Eh wani a farkon zuwana suna zabura, amman da nake musu addu'a sai suka daina har yawan kukan da suke”
“Okay, idan kin kaisu gurin Iya tai musu wanka kina ganin wani abun?”
Kamin Falmata ta bada amsa Fadime ta zaro ido.
“Oh ashe yayanka ne Iya take bibiya, ashe ita take cinye maka mata kenan? Ke ma wannan Falmata kin shiga uku Hajiya Babb...”
Bata karasa ba Shattima ya saka hannunsa ya rufe mata baki. Falmata kam kanta na kasa bata son kallon Shattima gudun kar tai laifi.
“Ina jinki”
“Gaskiya idan na musu addu'a idan na kaisu bata karba, kuma daga baya sai ya zamana kamar tana tsoron tabasu ma”
“Shine kawai abun da kika sani?”
Falmata ta yi shiru tana tunani,tana son ta fada masa cewar ta hada goro da furen tufafi ta ci ta ga Iya na gudunta, sai dai tana tsoron kar abun ya wuce nan a kirata kotu ko wani gurin ta kasa maimaita haka.
“Shikenan abun da na sani”
Yayi mata alama da ta fice, sai ta tashi da sauri ta fice daga gurin jikinta na rawa sai mamakin tambayar take. Sai da ta fice sannan Shattima ya dauke hannunsa daga bakin Fadime.
“Falon mu kowa na shigowa har da Iya idan ba ki iya bankinki ba zata ji, kuma Hajiya babba ma tana shigowa, kuma kin san idan ta ji zata ja miki wahala ne, dan haka ki kama bakinki ban da yawan magana”
“Da gaske, dan Allah kace a aje ni daki”
“Tau
Ya fada yana murmushi sannan ya kira Jekadiya a waya ta zo ta tafi da ita. Dafe take da hannun Jekadiya har suka isa cikin falon, Jekadiya ta zaunar da ita kasa kusa da ita, Fadime ta zauna ne kawai ba dan tana so ba. Jin Jekafiya ta tashi sakamakon buga kofar falon da akai yasa ita ma ta mike tsaye tana kallon inda take jim sautin takun tafiyar Jekafiya. Jekadiya ta karasa gurin kofar ta bude ganin Kausar tare da wasu mata uku yasa ta bude musu kofar tana musu sannu da zuwa.
“Ammy na nan?”
Kausar ta tambaya sai jekadiya ta amsa mata da sauri.
“Eh tana ciki, ayi mata magana ne?”
“Eh su Hajiyan Zariya ne za su mata gaisuwa”
“To”
Jekadiya ta juya da sauri ya nufi hanyar dakin Ammy ta kwankwasa mata kofa, sai da bayan minti biyar Ammy ta bata izinin shiga. Sai ta tura kofar dakin a hankali ta shiga ta sanar mata. Ammy ta amsa ba tare da ta juyo ba domin bata son Jekadiya ta ga idonta ya yi ja saboda kukan da ta sha.
“Ina zuwa, a kaisu karamin Falo”
“To”
Ta juya ta fita da sauri. Ta karaso inda suke ta sanar musu Ammy na fitowa.
“Bismillah muje karamin falo”
Fadime ta na jin haka ta kira sunan Jekadiya.
“Jekadiya su waye suka zo?”
Sai da Jekadiya ta kalli Kausar sannan ta amsawa Fadime.
“Kausar ce da baki”
“Ni dai ki dora ni akan kujera, ba Shattima yace ki kula da ni ba? Kuma ya ce ki boye ni kar Hajiya Babba ko Iya ta gan ni”
Daga Kausar har Hajiyar Zariyar da Kawayenta biyu sai da suka kalli Fadime.
“Wacece Wannan?”
“Wallahi ban san sunanta ba, ke amsa kina jin ana magana”
Jekadiya ta fada, aiko Fadime ta kama baki ta tsuke taki tai magana.
“Hajiya Bismillah ku...”
Suka bi bayanta suna kallon Fadime cike da mamakin wacece ita.
NANA POV.
Littafai ne ta zube a gabanta hannunta rike da biro, ta dukufa sai karatu take saboda exam din dake tafe, tun daga lokacin da tai wa AA alkawarin zuwa makaranta ba ta taba fashi zuwa ba, and no matter how zata ga kudi Ammy ko na wani tana kokarin ta hana kanta tabawa, duk wani son kudi da take a yanzu tana kokari ta yaki abun a ranta, domin ko kadan bata son tsaba alkawarin Sardauna a iya ganinta ta haka ne zata saka masa da abun da yai mata. Turo kofar dakinta akai a hankali tana dago kai tai arba da Ammy, dan sauke idonta tai kasa tana tunanin laifin da dai, domin ba kasafai Ammy take zuwa dakin dubata ba sai dai yi mata fada ko saka ta wani aikin. Ammy ta zauna kusa da ita tana kallon littafan dake gabanta.
“Karatu kike yi”
“Eh muna da exam Monday”
“Yayi kyau”
Ammy ta fada sai dai wannan yarta take kallo cike da tausayinta.
“Ammy wani abun nai?”
“No kawai na zo na duba ki ne”
Nana ta yi shiru tana dan mamaki, Ammy ta kai hannu ta dauki daya daga cikin littafan tana dubawa.
“Nana ba ki da kamar ni a duniyar, kina da wata damuwa ko kuma akwai abun da kike so, ki fada min kai tsaye na miki alkawari matukar abun nan be fi karfina ba zan miki shi”
“Yaya ya ce miki Wani abu ne?”
“Be fada min komai ba, kawai dai na ga baki da gatan daya wuce ni, na fahimci damuwarki a yanzu, kina bukatar kulawa da soyayyar mahaifiya”
Nana ta dago tana kallonta.
“Wani abu ne ya faru?”
Idon Ammy ya cika da kwalla ta fara kirga yatsun hannunta.
“Ban jidadin rashin saurarenki da nai ba, ya kamata nai hakuri na kai zuciya nesa, amman na kasa, wani lokacin abubuwa suna min yawa a akaina, na kan rasa ta ina zan samu natsuwa, kuma ban taba tunanin ki na yin wasu dabi'u ba ne saboda wasu matsalolin, a tunanina kina yi ne kawai dan ki bakanta min, amman yanzu na gane ki yi hakuri kin ji”
Sai Nana ta ji wani iri ganin hawaye na saukowa a idon mahaifiyarta.
“Ammy ki daina kuka dan Allah, Sardauna yace na daina bata miki rai”
Ammy ta share hawayenta wasu na sauko mata.
“Sardauna yaron da ya cece ki ko?”
“Eh, Ammy...”
Sai kuma tai shiru. Ammy ta kai hannu ta dago fuskarta.
“Fada min matsalarki Nana, ki dauke ni kamar kawa”
“Dan Allah ki taimaka Sardauna ya dawo, yayarsa taceba zata bari ya dawo ba, amman ni ina son ya dawo kuma shi ma yana so”
“So kike ya dawo?”
Ta daga kai.
“Zai dawo Nana na miki wannan alkawarin, kuma zan masa gatan da baki taba zaton mahaifiyarki zata iya ba”
“Ammy da gaske?”
Ammy ta daga mata kai hawaye na sauko mata. Nana ta rumgume ta da sauri.
“Thank you so much Ammy Thank You”
Ammy ya kwantar da kanta kirjinta ta rumgumeta sosai tana hawaye.
“Nana ki min alkawari kullum da safe zaki yi addu'an tsari, akwai husnil muslim a dakina zan kawo miki, ki tsare addu'a safe da yamma, kuma kar Hajiya Babba ta sake baki wani abu ki ci ko ki sha ko shafawa kinji yata?”
“Daman Sardauna yace min na daina zuwa bangarenta ma”
Ammy ta lumshe ido hawaye na sauko mata tana yaba kyautatawar Sardauna a ranta.
03/12/2021, 18:56 - 🤐🤐🤐🤐: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
Sau uku tana mika hannunta da zimmar kaiwa ta bude kofar dakinta sai ta saka saboda kukan da ya ci karfina. A bakin kofar dakinta a zauna tana wani irin kuka mai ban tausayi, da tasa irin abubuwan da Iya zata fada mata kenan da bata bukaci sanin komai ba. A yau sai ta ji ta raine kanta sai a yau ta gane ita din ba kowa bace, daukarar da take da ita ya yawan mabiya a instagram be haifar da mata da komai ba, a yau ta tabbatar da kaskantatun mutane da take rainawa wayo ma sun fita a yau, domin wasu da yawa ta hanyar sunna aka haife su, tsabanin ita da aka haifa ta hanyar zina zinar ma a tasha, sannan tai rashin dacen mahaifiya ta kwarai.
Daker ta yunkura ta tashi tsaye ta kai hannunta ta bude kofar dakin ta shiga ta bata da mu ta rufe ba ta taka har gaban gadonta ta zauna tana jin kanta na juyawa idonta na nauyi kamar zasu fito, zuciyarta na bugawa ta karfi.
A yanzu ta gane bata yi sa'ar rayuwa ba ta ko'ina, ta kwanta saman gadon tana jin tausayinta kanta, domin ta san wannan sirrin dole wata rana zai bayyana dole ne wata rana duniya zata sa wacece ita, wacece ita na asali ba na daukakar da aka riga aka santa da ita ba.
“Komai ba shi da amfani a gurina asali mai kyau shine komai”
Ta furta wasu hawayen masu zafi na sauko mata.
“Na rasa komai”
Ta sake fada tana jin wani irin tausayin kanta marar misaltuwa. A cikin kowa ce rayuwa akwai faduwa da tashi akwai samu da rashi, kuma akwai jarrabawa a yanzu kam ta yarda wannan ita ce jarrabarwata kuma jarrabarwa da tafi ko wace muni. Ta kwanta ba dan bachi ba domin har dare ya raba bachi be kusanci idonta ba, babu komai a kwakwalwarta sai tunani kala kala a cikin har na zalincin da Iya tai ma Ammy. Domin a iya ganinta be su cancanci a masu masauki a fadar ba amman aka ba su har aka jasu a jiki amaimakon ta kyautata sai ta cutar da Ammy har take bibiyar yayanta. A yanzu ta kara jin tausayin Shattima a ranta sanin gaskiyar abunda yake faruwa, a yanzu ta gane dalilin da yasa Iya take cilasta mata son Shattima, a yanzu ne ta gane dalilin da ya saka Iya bata taba mata fada akan yin ibada ba, bata taba ganin ta yi wata shiga ta kusheta ba ko kuma ta nuna mata kar tai, Ammy ce ko Shattima wani lokacin suke mata fada kan yanayin shigarta, sai a yanzu ta gane dalilin da ya saka Ammy tace kar a sake bari su shigar mata falo saboda Iya ta nemi a hada Shattima da ita, Ammy ta yi gaskiya da ta fada ma Iya cewar kalar zaren ba kalar yadin ba ne. Da tunani kala kala ta washe safiya tana yin sallah asuba ta fito harabar gidan ta zauna sai ta rasa abun da ke mata dadi, ita dai ba tace bata da lafiya ba, ba ta ce lafiyarta kalau ba, haka ba zata iya bayyan yadda take ji a zuciyarta ba for now.
Tana zaune a gurim har rana ta fito tana sanye da kayan bachi tana zaune a gurin sai kallon harabar take, a zuwa yanzu bata san abunda ya kamata tai ba kuka ko dariya? Ko murna? Ko bakinciki ko kishiyarsa? Tama kasa yarda cewar wai ita ce Zainab aka samu ta wannan hanyar, duk irin jin da kanta da take sai ta ji kamar ta fi kowa kaskanci tsakanin jiya da yau.
“Kenan Iya ita ta cinye Auwal?”
Ta fadawa kanta tana jin wani sabin hawaye yana cika mata ido, rabon da hawaye ya kusanci idonta tun jiya da abun ya faru domin ta tabbatar wani abun yafi gaban kuka, a tsakar dare neman kuka tai ta rasa. Ta lumshe idonta kana ta saka hannunta ta dafe zuciyarta tana sauke numfashi a hankali.
“Komai zai wuce zai zama tahiri Zainab, zaki samu farinciki wata rana zaki tuna wannan ki ji ba komai ba, ba ki da laifi ba ki ce a same ki ta wannan hanyar ba, ba ki ce a haife ki a haka ba, ba ke kika saka mahaifiyarki ta zama haka ba...”
Ta fadawa kanta a kokarinta na kwantarwa da kanta hankali. Bata taba sanin hawaye na da zafi ba sai a yau, domin hawaye masu dumi ne suke sauko mata, a take ta ji wani zafi ta taso mata ya baibaye jikinta har saman kanta.
“Zainab har zuwa yaushe za ki daina wannan kukan?”
Iya dake tsaye bakin kofar falon