Showing 162001 words to 165000 words out of 273152 words

Chapter 55 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72733

su yi...”


Ta fashe da kuka, ko ba a fada mata ba ta san Zainab ta ji abun da ta fada na zancen maita, domin shi kawai take tunanin zai bata mata rai, ba zancen wacan matar ba data raka zuwa garinsu Wasim, kuma ta san ba za su raga mata ba, baka taba maye ba ma ya ka kare balle kuma ka taba, abu na mu dan kura da kallabin tsire😂


A gafarce ni jiya ban samu na yi ba, bana jin dadi ne yau ma karfin hali ne, fatar za a min afuwa kamar yadda aka saba. Allah kara mana lafiya da abun da lafiya zata ci, ya tsare mu daga dukanin abun cutarwa.




_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:54 - 🤐🤐🤐🤐: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*




Yadda ta rike masa kafa sai ka rantse da Allah idan ta saki kafar wani abun ne zai sameta, ba zuciyarta ba har jikinta ba bakinta mai sakin zance rawa yake. A take ta fara ruwan hawaye da majina, yana kokarin kwace kafarsa ta kai hancinta jikin wandonsa ta goge majinar.


“Ke Malama kafata ce kika share majina da ita”


Ta fada yana kallonta for the first time ta masa abun da ba a taba masa ba.


“To ina ruwana ko ba kai ka barni ina ta zuba ba, ba zaka fada min kace gata nan ta zo ba, kuma ka min alama kut”


Ta yi kwafa domin ta fi jin haushinsa yanzu fiye da kowa. Da me zan miki alama tun da ba gani kike ba? Ya furta a aransa a fili kuma sai ya kai hannunsa ya saka karfi ya banbanre hannayenta, wani irin hargagi tai kamar kyanwa ta kara kame kafar ta rike gam, daker ya yunkura ya mike tsaye, tana jinsa tsaye ita ta mike tsaye tana dafa shi har ta isa daidai kunkurunsa ta rike gam kamar ta samu ice, ta dora kafarta ta dama akan kafarsa ta hagu, ta hagun ta dorata a kafarsa ta dama, ta yadda idan ya daga zai yi tafiya kafafuwanta na saman nashi.


“Wallahi dole ne ka tafi da ni, ba zan zauna ba, ai kai ka bar ni ita ta zuba, baka ko min alama ba, duk ta ji komai, shikenan sai na zauna su cinye ni, ga makanta ga mutuwa aa Wallahi ba zan yarda ba”


Ta fada har da girgiza kai tana kara rike shi, be san lokacin da murmushi yai ma kansa muhalli a fuskarsa ba, murmushin da ya bayyana hakoransa.


“Ina zan kai ki?”


“Ka kai ni garinmu”


“Garinku ba nan kusa ba ne”


“To ka kai ni gidanku gobe sai ka kai ni garinku, ai gidan ku ba mayu ko?”


Yayi shiru sai kallonta yake cike da nishadi. Ya cira kafar daya ya taka tana saman kafafuwansa.


“To sauka”


“Aa Wallahi ba zan sauka kana ganina haka idan na sauka wayo zaka min, sai dai mu tafi a haka”


“Ya za yi na fita dake haka? Kin san waye ni kuwa?”


“Ina ruwana da kai ko waye, kai ka san wacece ni? Hmmm”


Ta kara kankameshi, seriously be san yadda zai yi tafiya da ita ba a haka kafafuwanta saman na shi. And what he hate the most is ka take shi amman ji yadda ta dora duka kafafuwanta saman na shi.


“Ba zan iya tafiya a haka ba”


Yadda yake amsa mata kadai abun mamaki a gurinsa, domin ya tabbatar da ba ita ba ce ta yanzu ya dauke ke ko waye da mari. Jin ya fadi haka yasa tayi kasa da hannunta ta kama rigarsa ta shadda ta rike gam, sannan ta sauka kan kafafuwan nasa.


“To mu tafi...”


Sai da ya kalli rikon da tai masa sannan ya kalleta.


“Ban san inda zan kai ki ba Wallahi”


“Ko ma ina ne ni ka kai ni”


Ya hade yawu a hankali sannan ya fara takawa tana rike da shi kamar wanda yai mata sata gefen shaddar data rika har ta tamuke. Yadda ya fito cikin falon ba zaka ce shine ya shiga dazun fuska a hade ba, domin a yanzu murmushi da nishadin da be san ta ina yake zuwa masa ba ya wanke masa fuska da zuciya. Har gaban motar ya karasa da ita ya bude front seat.


“To shiga ki zauna”


“Aa idan na shiga wai wata motar ce zaka saka ni sai ka shiga motarka ka tafi ka barni”


Ya sake yin murmushi.


“No motata ce”


“Ce Wallahi?”


Ya zaro ido kamar tana ganinsa, a rayuwarsa ba a taba bashi rantsuwa ba. Shiru yai mata a gurin sai kallon kyakyawar fuskarta yake. Jin shiru yayi yawa yasa ta kai dayan hannunta tana taba kirjinsa.


“Kana nan ai”


“Idan ba zaki shiga ba, sake ni na tafi”


“Sai ka rantse”


“Ba zan rantse ba”


“Ni kuma ba zan sake ka ba”


Ta kara gyara tsayuwa yadda zata ji dadi dadewa a gurin. Kansa ya daga sama ya sauke can kuma ya kalli gate yana mamakin yadda akai be dauke ta da mari ba tun dazun.


“Sai dai mu yi ta tsayuwa a nan har dare, Allah yasa ma ayi ruwa”


Ya wara idonsa yana kallonta like serious ya fada a ransa, ya sake yin murmushi.


“Okay i swear”


“Ka ce Wallahi Motata ce kuma ba zan tafi na barki ba?”


Ya kara zare ido, wai yarinyar nan kuwa ta san waye shi? How on earth zata saka shi rantsuwa again kamar kotu?


“Ka ce”


Ya mata shiru kamar shekararen ice.


“Ya ma sunanki?”


“Fadime”


“Okay, ki tsaya mu yi maganar hankali ni ba zan sake rantse miki ba, idan kin yarda da ki ki shiga kawai bana karya, kuma har garinku zai maida ke saboda iyayenki suna can suna nemanki idan ba su gan ki ba zasu saka ni kotu”


“A ina suka ganka?”


Ta ina zai bata labarin suna tsaye a rana?


“Shiga mota”


“Sai ka rantse kamar yadda na ce ka fada sannan”


“Wallahi motata ce kuma ba zan barki ba”


Tana jin ya fadi hakan ta sake shi ta lalaba ta shiga motar, shi kuma ya rufe yana murmushi sannan ya zagaya dayan side din. Kamin ya zagayo ya shiga motar har ta tsawwala, sai ta taji ya shiga ya zauna har yayi ma motar key sannan hankalinta ya kwanta.


“Kika sani ko ni ma maye ne?”


Ya fada yana murmushi tare da kai hannunsa ya kara gudun ac motar. Cak Fadime ta tsaya.


“Kuma fa?”


Take wani tsoron ya kamata, nan da nan sai kuka kamar ba ita ce ta gama rigima ba yanzu. Da gangan Shattima ya kyaleta tana ta rusar kuka a motar har sai da suka bar gidan suka hau babban titi.


“Wasa nake miki”


Ta ki daina kukan, shi kuma be fasa murmushin daya kusan zame masa dariya ba.


“Haba wasa fa nake”


“Rantse to”


Ta fada cikin kuka, sai ya kalli fuskarta.


“Me zan ce?”


“Ka ce Wallahi wasa na ke”


“Kina ta saka ni rantsuwa fa ba a taba sani haka ba”


“Ni ma ba a taba min haka ba, ka taba ganin an bawa maye ajiyar nama? A kawowa maye mutum har cikin gida ace wai ya aje? Kaddarorine suke ta bina, daman sai da Inna tace Fulani karki je garin nan karki je, amman ban ji ba na tafi, gashi nan naje na ci wuya, kuma na dawo na makance, har an kawo ni ajiya gurin mayu”


Shattima ya bushe da wata kalar dariya da ya manta when last yai irin dariyar, dariya sosai har yana buga sitiyarin motarsa.


“Oh my god”


Ya furta yana kokarin takaita dariyarsa. Kana ya kalleta.


“Waya fada miki cewar mayu ne?”


“Wasim mana”


“Waye Wasim?”


Sanin labari zata bayar yasa ta share hawayenta, ta gyara muryarta dake da kufan kuka.


“Saurayina ne, a lokacin da ya kawo ni sai yace ga ajiya na kawo idan kin ga dama ki cinye idan kin ga dama ki aje, kuma yace mata kin ki amayarda kankarar maitar nan ko? Kin zama daman cikin mutanr kina cin mutane yan uwanki, sai ta ce aa ni banci kowa ba, duk mutanen da nake ci masu shiga ganyata ne su tare min cikar buri, wani mutum nake bibiya, na cinye masa mata yanzu kuma yayansa na ke bibiya, kaga kenan mayya ce ko?”


Shiru Shattima yai yana tunani rage gudun motarsa.


“Waya fadi haka?”


“Ita wannan tsohuwar mai magana kamar gere kyankyankyan...”


Fadime ta kwaikwayi muryar Iya tana matse baki kamar tsohuwa. Shattima yayi murmushi duk da kasancewar yana cikin rudani da tunani. Sai a lokacin tunani ya zowa Fadime, what if shi ma danta ne? Ko Kuma yana da alaka mai karfi da ita?


“Wannan tsohuwar mamanka ce?”


“No”


“Kakarka ce?”


“No”


“Kanwar mamarka ce?”


“Oh...No”


“To miye alakar da ita?”


“Tana zama a gidanmu ne kawai kamin ta dawo nan”


“To yarta fa? Ita ma baka da alaka da ita?”


“Yes”


“Ko dai budurwarka ce?”


“No kin cika tambaya”


“To ina zaka kai ni?”


“Ina na sani, kin zame min kaya”


Can kuma ya kalleta yana murmushi yace.


“Bakin titi ki yi bara”


“Lalala ai ni ba makauniya bace makafi da nakasassu sune suke yin bara Allah ya tsare ni nikam”


Shattima ya faka motarsa gefen titi yana tintsirar dariya kamar ba shi ba.


“To ke micece?”


“Ai ni ba haka aka haife ni ba, kuma idona zai bude, kuma maganar nan ta min zafi”


A take idonta ya cika da kwalla domin har ga Allah ta ji zafin da ya kirata da makauniya har ta furta kalmar bara a gareta.


“Duk matar nan ce da ja min shiga wannan hali, da bata je garin ba da ban bita ba, ni Wallahi yanzu idan na ga wani zai je ma hana shi zan yi, duk bakina na yaje min nace mata na san wanda zai kaita, salo gareni Allah yayi min shegen salo (Banbandanci)”


Shattima ya jingina da jikin kujerAR motar yana dariya.


“Wace mata kuma?”


Ta fara bashi labarin abun da ya faru tun daga farko har karshe.


“To ai ita ce wannan matar wacce muka baro gidanta yanzu, ba a motata kuka hadu ba kika ce mata kin sa gari”


“Haka ne haka ne...ita ce?”


Ta daki kirji.


“Har take min wannan wulakancin? Har take ce min na sauka a kujera? Har take min tsawa? Har take min fada? Lallai dan adam butulu ne, lallai wannan matar ba zata ga annabi ba, mayya kawai yar mayya, masu bakin hali da mugun nufi, Allah yasa idanuwana suna budewa nata su rufe, amman ba zan taba yafe mata ba, ai wannan zallumci ne, ko tausayina bata gani? Wayyo Allah”


Kuka take sosai tana jin zafi abun da Zainab tai mata.


“Allah ya saka min a gareta da duk wanda yai sanadiyar haduwa ta da ita”


Shattima ya dago ya kalleta.


“Har da ni kenan?”


Ba dan tana tsoron kar ya sauke ta a hanya ba, da ko amsa masa ba za tayi ba.


“Aa bacin rai ne ya kawo haka, na yafe maka”


Ta fada cikin kuka, ba dan ta yafe masa a zuciyarta ba. Murmushi yai ya ja motar suka koma kan titi. Maganarta ta dazun ce ta dawo masa a rai, cewar wani mutum take bibiya ta cinye matansa kuma tana bibiyar yayansa, me hakan yake nufi? Baya son ya munana tunaninsa, amman har ya fadada tunaninsa mutumen daya fada ba yi kama da kowa ba sai shi! And lastly Ammy ta fada masa cewar ta talla Zainab, miyasa bata ji tsoron kar Zainab din ta mutu ba?


“Bayan haka kin ji wani abu?”


Ya tambaya yana kallonta, sai ta girgiza masa kai domin ba zata iya amsawa ba saboda kukan da take na bakincikin abun da Zainab tai mata.


“Wallahi da na san ita ce, ko tace na sauka a kujerar nan zan ce mata ba zan sauka ba, idan tace matsa can n ace ba zan matsa ba, hala ba saboda ke na samu matsala ba? Wallahi na fita iya iskanci yar daba ce ni idan bata sani ba, har ta isa?”


Shattima ya saka dariya, yana mamakin yadda ta rike abun a ranta ta kasa sakinsa.


“Dan Allah ki bar ni nai tunani, i need to think”


“To think Mr thinker...”


Ta fada cikin kuka, sai yai murmushi ya kai hannunsa yaja dogon hancinta.


“I like you idan ba ke ba ba zai miki haka duk a garin Yola?”


Ya saka dayan hannunsa ya dauki wayarsa ya nemo number Jekadiya. Bugu daya ta dauka tana rangada masa kirari.


“Jekadiya, dan Allah a nemo yariyar nan gobe”


“To an gama ranka ya dade”


Ya aje wayar kamar yadda ya saba ba tare daya kashe ba. So yake yayi ma Falmata wasu tambayoyi he need to confirm something. Ya kalleta har lokacin kuka take.


“Baki gajiya da kuka?”


“Baka san yadda nake ji ba, na taimaki matar nan amman shi ne zata saka min da haka? Ai ko bata san ni ba be kamata tai min haka ba, dan'adam yana da daraja, mu mutanen kauye ba mu san mu wulakanta mutum ba”


“Bata kyauta ba, sorry amman ba ganina nan ba? Zan kai ki gida gobe inshallah”


Ya zari tissue ya dora mata a cinya.


“Share hawayenki da wannan”


Ta dauka ta share ta goge majinar ta mika masa.


“Gashi”


“No kefa shi can”


Ya sauke gilashin motar na side dinta.


“Ina?”


“Gefenki ta gurin da kike jin iska”


Ya mika hannunta ta jefar.


“Ina zaka kai ni?”


Ya daga kafadunsa alamar be sani ba duk da ya san bata ganinsa, not knowing where to take her, yadda take da yawan surutu ba zai iya kaita masarauta a yanzu ba, domin zata je ta basu labarin maita na Iya, and if Ammy ta san yaje gidan Zainab she won't be happy. Bashi da zabin daya wuce ya kaita gidansa kamin gobe, ya sake dauko wayarsa ya kunna data da kansa dan siyen ticket din mutum biyu, shi da ita na zuwa Katsina gobe.










FALMATA POV.


Sai da tai kamar ta koma cikin gidan ta fadawa Jekadiya cewar tana son ta cigaba da aikin kamar yadda ya bata dama, sai kuma wata zuciyar ta hanata, sai ta nufi gate din kai tsaye da zimmar ficewa, a tunaninta cigaba da aikin karin wata barazanar ce a gurinta, domin zata iya shiga wata matsalar kuma bata san abun da zai kara biyowa ba, wata kila ma yafi wanda ta shiga a baya. Bata karasa gate din ba motar Sirleem ta kunno kai cikin gidan, yana kawowa daidai ita ya tsaya ya sauke gilashin motarsa, bata lura da shi ba har sai da ya kira sunanta.


“Falmata”


Ta kalli motar ganin shi ne yasa ta tsaya ba tare da ta ce masa komai ba, hannunsa ya mika ya bude mata dayan side din.


“Zagoyo nan”


Ba musu ta zagaya tana dingishi, shi kuma ya bita da kallon tausayi har ta shiga motar ta zauna.


“Rufe”


Ta mika hannu ta janyo ta rufe.


“Ina wuni?”


“Lafiya kalau miya samu kafarki?”


“Faduwa nai”


“Wannan ba faduwa ba ne, karya kuma ba halinki ba ne, Teema...”


Ta dago ta kalleshi ji irin sunan da ya kirata da shi.


“Baba ne ya dake ni”


“Saboda me?”


Bata boye masa komai ba, bata rage ba balle ta kara. Ajiyar zuciya ya sauke idonta ya cika da kwalla, for the first time ya ji ya tsani Babanta.


“Teema akwai wani abun da zan iya miki? Kina son naje na fadawa babanki baki son auren mutumen? Ko kuma kina da wanda kike so na je na yi magana da shi?”


Ta girgiza masa kai hawaye na zubar mata.


“Aa, ka min komai na gode”


Ya lumshe idonsa ya bude ya kalleta.


“Me kika zo yi nan?”


Ta fada masa.


“Bari na kai ki duba Momy ta duba kafarki”


Ta yi shiru bata ce komai ba sai hawaye take, ribas yai ya juya da motar suka fita, tafiya suke bata ce da shi komai ba shi ma be ce mata ba sai kallon fuskarta yake.


“Na rasa dan'uwana, 3 days back shi ne kadai dan'uwa namiji da nake da shi ya rasu sanadiyar hatsarin jirgin sama, ni kaina tun ranar dana bar ki a gidan Momy ban sake zuwa ba”


“Allah ya jikanshi”


Ta furta tana share hawayenta, yayi shiru be sake cewa komai ba, sai dai har ga Allah yana jin sauka hawayenta a zuciyarsa.
A harabar gidan Momy ya faka motarsa, sannan ya bude ya fita tana ganin haka ita ma ta bude ta fita, ta bi bayansa, knocking yai after few seconds aka bude masa kofar falon, sai yai ma Falmata alama da hannu cewar ta fara wucewa.
Bata masa musu ba ta saka kafarta cikin falon tana dingishi.


“Subhanallahi wani abun ne kuma?”


Momy ta fada tana kallon kafarta, Falmata ta mika mata gaisuwa ba tare da tace komai ba.


“Wannan Step Mother din ta ce ta gano an koreta daga aikin shine tasa Babanta yai mata wannan dukan, and lastly wai ta ji yana maganar zai maida aurenta nan da sati daya!”


“Auren wa?”


Momy ta daki kirji tana kallom Sirleem da yai mata maganar. Sai da zauna ita ma ta zauna sannan ya labarta mata zancen auren kamin ya biyo mata da abun da ya faru.


“Mai napep din ya dawo ya fada min ya daina ganinki zai je ya tsaya ya jira amman ba zata fito ba, yana fada min haka na raya cewar wata kila sun gano ne, ko kuma kin fada musu, na so na kira ka sai ga labarin rasuwar Talba ya same shi shiyasa da naje gaisuwar ban maka magana ba, yanzu miye mafita?”


“I don't know, na tambaye ta idan akwai wanda take so, tace babu”


Sirleem ya fada yana dagowa daga jikin kujerar da yake zaune. Momy ta kalleta wani irin tausayin Falmata ne ya shiga zuciyar Momy fiye da da, bayan wannan wahalar da ake bata sai kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login