Showing 168001 words to 171000 words out of 273152 words

Chapter 57 - FULANI BOOK COMPLETE DOCUMENT by Khadijah Candy .txt

29 Aug 2024

72742

na ratsa kwakwalwarta. Shi dai be ce mata komai ba har ta ci ta koshi tai gyatsa.


“Ina Yogurt din?”


Tashi yai ya karasa gabanta ya dauki kopin ya kai mata a baki, ta fara kwankwada sai da ta shanye tass sannan ta janye bakinta tana lashi gefen bakin.


“Kai ba zaka ci ba?”


“Na koshi”


“Ka aje min ragowar har gobe ko anjima”


“Ga wata nan ma zan saka miki a firji da safe sai ki ci”


Ya kama hijabinta ya goge mata inda bakin ya bace da maski da yogurt.


“Zan kaiki ciki ki yi wanka sai na saka yarona ya shiga kasuwa ya samo miki wasu kayan, kin yarda?”


“Eh Wallahi, na yarda daman ina son nai wanka tun ranar da na zo garin nan ban yi wanka ba, amman ba zan saka sosonka ba, da sabulu kawai zan yi”


Yayi murmushi finally ya hadu da mai kyamarsa.


“Shikenan bari na kira shi”


Ya mike tsaye ya fara tafiya sai ta kira shi.


“Shattima...”


Ya juyo ba tare da ya amsa ba. Ita ma bata jira ya amsa din ba tace.


“Na gode sosai, da wacan Zainab ce ba zata min haka ba, bata taba bani nama ba, ko ranar da na zo ina jin Iya tana soya nama amman bata bani ba, ina ta jin kamshi, sai cewa take tantabarun nan suna da mai, amman bata ba ni ko man ba”


Shattima yayi murmushi ba tare da yace da ita komai ba ya haura sama, kudi ya dauko sannan ya sauko ya fita waje, Zubairu na ganinsa ya taso da sauri ya nufo inda yake.


“Ranka ya dade, Allah kara maka lafiya wani abu za ayi?”


“Yeah so nake na shiga kasuwa ka samo doguwar riga medium ta manya da hijabi, ba dole sai mai tsada ba”


Ya mika masa 30k din hannunsa, Zubairu ya saka hannu ya karba yana amsawa da.


“To an gama yanzu kuwa”


Shattima ya juya ya koma cikin falon, wannan karon ya samu Fadime tsaye a inda ya barta tsabanin dazun da take zaune a kasa. Karasawa yai kusa da ita ya kama hannunta suka nufi upstairs din.


“Sai kin taka a hankali”


“Tau bismillahi”


Ta fara takawa a hankali.


“Ban taba hawa gidan sama ba”


Be biye surutunta ba ya saka hannunsa ya dauke ta sama ya haye da ita. Rike shi tai sosai har sai da ya shiga cikin dakin ya sauke ta sannan ta sake shi.


“Cikin bandakin ne ka kawo ni?”


“Aa”


Yaja hannunta zuwa bathroom din ya bude ya saka ta ciki, ya kai hannunta a a inda zata aje kayanta.


“A nan zaki dora kayanki”


Ya dauki sabulun ya mika mata a hannu ya ya kunna mata shawa.


“Tau fita”


Ya juya kamar yadda ta fada sai ta kai hannunta tana lalaben bayansa shi dai ban da murmushi babu abun da yake har ya fita ta ji ta rika kofar ta rufe da kanta.


“Yi magana na ji”


“Gani a nan ba zan shigo ba”


Sai da ta tabbatar ta ji muryarsa a waje sannan ta juyo da lalabe ta karaso gurin da ya kaita ta cire tufafinta ta aje ta karasa gurin shawar ta tara jikinta tana ayyana yadda bandakin yake, sai da ta duka kasa ta taba tile din ta taba jikin bandakin sannan ta cigaba da wankan tana jin dadi ruwa na sauka a jikinta, abun da bata taba ba.
Sai da ta gama wankan ta dauki tufafinta ta saka ta maida hijabin sannan ta fara kiran sunansa.


“Shattima.... Na gama”


Ta fara takawa tana tafiya, har ta isa gurin kofar ta fara lalabe ta bude ta fito tana tafiya a hankali.


“Shattima...”


Ta kwara masa kira, sai ya amsa yana zaune kan gadon.


“Na'am”


Tsayawa tai a gurin bata sake ce masa komai ba, shi a be ce mata ba, sai tunanin karfin halinta yake yadda ya fada mata be da mata kuma ba kowa a gidan sai ita da shi amman bata jin tsoro ta sake jiki babu wata fargaba, gashi kuma ba gani take ba.


“Zo ki zauna”


Ta fara takawa ta nufi inda take jin muryarsa sai da ta karasa sannan ta lalaba ta zauna kan gadon.


“Sanyin Ac”


Ya kalleta tufafin ma a birkice ta saka su, ya dauke kai ya mike tsaye ya nufi kofar fita, tana jin fitarsa ba hakuri bata ce komai. After like 30 min ya dawo dakin ya warware rigar, ya kama hannunta ya saka mata rigar.


“Zan fita sai ki saka, inda kike jin stone nan ne gaba, wannan dankwalin ne, ga kuma hijab”


“Tau na gode”


Ta fada da murmushi a fuskarta tana jin dadi duk kuwa da kancewar bata ganin komai. Juyawa yai ya fita yana jindadin ya farantawa wani rai. Sai da ta ji ya rufe kofar ta kwala masa kira.


“Shattima”


“Na'am”


Ya amsa mata da karfi yana juyowa.


“To tafi daman dan na tabbatar idan ka fita ne”


Ta mike tsaye ta fara cire tufafinta, sannan ta dauki rigar ta saka ta saka hijabin. Be dawo dakin ba sai bayan sallah magariba. Yana shigowa ta fara tambayarsa wai ta yi kyau, da taimakonsa tai alwala ya shimfida mata abun sallah tai sallah.
Bata kwanta ba sai da ya sake bata naman na kaza ta ci sannan ta hau gadon ta kwanta ta.


“Amman ka kwanta a kasa, idan ka bar ni ni kadai zan ta maka ihu”


Yana kallonta yasan zata iya tsab.


“Kina firgita da dare ne?”


“Aa amman dai nan ina jin tsoro, ba zan iya kwana ni kadai ba”


“To ki yi addu'a kamin ki kwanta”


“To zaka kwanta a kasa din?”


“Ke ki kwanta a gado?”


“Eh mana, a ba zamu kwanta a gado daya ba Allah ya tsare, in Bappa ya sani zai ya kusa kasheni”


“Okay”


Ya fada yana murmushi, bargo ya dauko ya shimfida a kasa ya saka filo, ita kuma ta kwanta saman gadon ta zuro hannunta kasa ta yadda zata rika jinsa ta tabbatar a kasa yake kwance.


Washe gari da asuba ya farka kamar kullum bayan yayi sallah ya tasheta tai sallah sannan ya fasa sabon brush ya rika fuskarta ya wanke mata baki ya fito da ita ta dauko mata ragowar kazarta ta cinye da yogurt, shi kuma ya hada tea ya sha.
Bayan sun gama mai gyara ya shigo ya gyara ko'ina a gidan sannan ya fita.


“Zan biya dake ta wani gida, na yi ma Ammy sallama sannan mu wuce airport”


“Ammy kuma...”


Tana ta tunanin inda ta san sunan can kuma ta tuno da zancen airport.


“Jirgi zamu shiga kenan?”


“Eh”


Ta dafa zuciyarta tana dariya wani shauki na ziyarta ta.


“Tsoro kike ji?”


“Aa dadi dai? Jirgi fa zan hau, dan ma bana gani, wayyo Allah”


Yayi murmushi ya riko hannunta suka fito, sai da ya saka ta cikin motar sannan yaje ya rufe kofar falon ya dawo ya shiga motar ya saka key din ya murda motar ta ki motsawa ko wuta taki dauka, ya murda ya murda ta ki tashi fita tai daga motar ya bude gaban motar ya duba be ga komai ba, ya dawo ya sake tadawa ta ki tashi. Fita yai ya koma cikin gidan, ya dauko key wata mota ya nufeta ya kunna sai ta tashi, dawowa yai ya cire Fadime a motar farko, ya saka a wanda ya kunna Fadime na shiga motar ta mutu.


“Oh Wow....”


Shattima ya furta yana cike da mamaki.






ZAINAB POV.


Tana shiga cikin dakin ya fada kan gado ta rushe da kuka, bakincikin abubuwan da Fadime ta fadawa Shattima ya saka taji kamar ta kashe kanta, da wane ido zata kalle gashi ta hada karya da gaskiya ta fada masa, har abun da Iya ba tai ba. Bata dauka Shattima zai dauki Fadime su tafi ba har sai da ta ji tashin motarsa ta sauko saman gadon da zimmar zuwa tai ma Fadime dukan mutuwa sai ta samu falon babu kowa, tsaye tana tana karewa falon kallo kamin ta nufi dakin da fadime take kwana ta duba ganta ba, ta shiga dakin Iya ko zata same ta a ciki nan ma bata ciki, fitowa tai harabar gidan ta tambayi mai gadinta ya tabbatar mata da tare ya fita da yarinyar, sai ta dawo cikin falon tana mamakin abun da Shattima yai wanda be taba ba, me ma zai saka ya tsaya kulata? Or Maybe saboda tana makauniya ya ke ganin tausayinta. Ina zai kaita? Gashi bata isa ta kira ta tambaye shi ba, indai har masarauta ya nufa da ita ta san Fadime sai ta fadawa kowa cewa Iya mayya ce. Fashewa tai da kuka tana jin ina ma ba a kawo Fadime gidan ba. Tana cikin kukan Iya ta shigo rike da leda tana ta sauke gajiya da alama wani gurin ta fito. Jin Zainab tana kuka yasa ta kalli inda take xaune cike da faduwar gaba.


“Kai Subhanallahi lafiya dai?”


Zainab kamar mai jira ta dago tana duban iya hawaye sharaf a fuskarta.


“Ina lafiya Iya? Kin ja mana abun kunya, kun yi komai a gaban yarinyar nan yanzu ta kwashe ta fadawa Shattima, ba ke kadai ba har ni sai da tasa, tace ni da ke duka mayu ne, yanzu ya dauke ta ya tafi da ita Allah kadai ya san wanda zata fadawa a masarautar nan, gashi ta kiri karya tace kin ce rayuwar wani kike bibiya wai kin cinye matansa kina cin yayansa wane irin abu ne wannan?”


Ba shiri Iya ta saki ledar hannunta.


“Ita yarinyar ni zatai wa lazafin maita?”


“Ba gaske bane? A gabana Wasim ya fada miyasa baki karyata shi? Bakinciki abun da na ji ne ya saka na kyale ban miki magana har yanzu, amman yanzu ina bukatar sanin komai asalina wacece ni, ina mahaifina i need to know, Wasim ya fada min saboda Maita aka koreki daga garinsu kuma na san ba zai min karya ba, miye dalilinki na daukar maitar nan Iya? Why?”


Gumi ne ya fara kemowa Iya ta ko'ina, jikinta na rawa ba abubuwan da Zainab take tambayar ne ne ya daga mata hankali ba, zancen Fadime ne ya tsaya mata a rai. Sai dai hakan be hana zuciyarta dakewa bakinta ya amsawa Zainab tambayarta ta ba ta sigar da kwararun mayu suke yi.


“Karya ne fa, ke kin taba ganin maita? Babu maita ko a kur'ane, idan ana son bata maka sunane ake maka wannan abun, karki sakawa zuciyarki shakku akan mahaifiyarki”


Zainab kallonta take tana tunanin karyar da take zargin Fadime ta yi wanda tai daidai da abunda yake faruwa a zahiri wato mutuwar matan Shattima da kuma yayansa.


“Taya akai yarinyar nan ta san haka har tai karya a kai?”


“Me kenan?”


Zainab ta yi shiru bata ce komai ba, sai ma juyawa da tai ta nufi dakinta. Iya ta kara bata mummunar fuskarta tana jin bakincikin abun da Fadime tai duk da masancewar ba a gabanta tai ba.


“In ban da sakarci irin na ki taya zaki bar shi ya tafi da ita?”


Ta tambaya kamar Zainab din tana kusa ta amsa mata.


“Wallahi bana son irin mutanen nan sam, miyasa Wasim zai kawo min ajiyar?”


Ta furta mayu basa son mutun marar jin magana da mafadaci kurwarsa na da wuyar ci.


“Dole ne na bi bayanta dole ne sai na taba ba, idan ba haka ba zata bata min suna a gidan nan kuma ta tona min asiri, ni ko da nai kunya biyu kara na yi guda”


Ya duka ta dauki ledar ta nufi dakinta ta aje sannan ta fito ta saka makulli ta rufe dakin sannan ta fice da sauri gabanta sai faduwa yake tana tunanin kalar surutun da Fadime zata zuba a gidan gashi ta ji komai.






***


Tun ranar da suka kai rahoton abun da ya faru, suka dukufa da addu'a ba dare ba rana, musamman ma Inna da tafi jara'a akan cewar aljanune suka sace ta, washe gari kuma Bappa kuma ya koma asibitin domin jin ko an samu wani abu a can din. Wannan karon shugaban asibitin da kansa ya kira shi yana masa bayani cewar ya dage da addu'a kuma yai har hakuri tun da an saka cigiya a ko'ina a gashi kuma likitan da abun ya shafa an masa rasuwa sai ya nemo ya daga masa kafa har nan da kwana hudu zuwa biyar ko sati. Su kansu za su taya su nema, har ya bukaci idan akwai hotonta a kawo masa sai saka a media ko Allah zai saka a dace, da wannan Bappa ya baro asibitin ya nufi gurin police duk da kasancewar ya bada number wayars cewa idan aka same ta ko aka ji wani abu a sanar da shi. A can din ma da ya tafi babu labari har ya taka yaje har gidan redio da aka kai ciya duka dai maganar daya ce ba a ganta ba.
Kamar wani marar lafiya haka ya dawo gida gaba daya wunin ranar be tafi kasuwa ba, ko ya iso ya samu Inna ba lafiya, har wani yayansa ya dauko mai allura yayi mata guda biyu.
A gefen tabarma da take kwance ya zauna yana mata sannu, shi kanshi ji yake kamar lafiyar bata ishe shi ba. Be wuce minti ashirin zuwa ashirin da biyar da zama ba, wata matashiyar budurwa ta shigo gidan tana sallama, makociyar Inna ce dake gyara gida ta amsa mata.


“Hauwa ce?”


“Inna Ramla ina wuni?”


“Lafiya kalau”


Budurwar da ba zata wuce sa'ar Fadime ba ta juya gurin Bappa tana mika masa gaisuwa da yaren fulatanci, bayan ya amsa ta fada masa ana masa sallama a waje.


“Bappa wani ne a waje yace a sallamo ka, yace ace Wasim na maka sallama”


Ta fada da yaren fulatanci.


“Wasim?”


Bappa ya maimaita jin sunan wani iri da be tana ji ba, sai kuma ya yunkura cike da gajiya ta mike tsaye yana hamdalla ya nufi kofar gida.






_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
03/12/2021, 18:56 - 🤐🤐🤐🤐: *Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*




Da tunani kala kala Iya ta isa masarautar, domin ta san ita Fadime zata fara fallasawa kamin ta fadi kowa, tabbas indan ta fadi abun da Zainab ta fada mata kowa zai gane kuma za a yarda da Fadime, sai da ta kusa isa gate din Ammy sannan ta tuna gargadin da Ammy tai mata cewar kar ta sake shigar mata falo, idan wani abun take so ta fada a sanar da ita. To idan ma ta shiga me zata yi? Ai dai ba zata iya cewa Shattima ya bata Fadime ba, idan ma ta bukaci hakan wani tonon asirinta ne domin Fadime ihu zata saka ta fara mata ihu tana kiranta da Mayya, anya ma zata iya shiga ciki ta hada ido da Shattima? Idan tace masa Fadime ta zo dauka ai wani karin abun tonon asirinta ne. Zaune tai gindin gate din tai tagumi hantar cikinta sai kadawa take, tana ta tuke tana tauna abun duniya ya mata yawa.


“In da na san haka yarinyar nan take, Wallahi kame kurwarta zan yi na matse ta kwanta ciwo sai na ga bakin maganar”


Taja tsaki.


“Dai dai nai kunyar duniya kara ta kiyama gaskiya ba zan yi kunga biyu ba”


Ta mike tsaye ta nufi hanyar bangaren Ammy, da tsoro ta doshi gurin tana kawar dai kai, sai dai jin yadda kowa yake mika mata gaisuwa kamar yadda suka saba yasa ta ji sanyi, ko da yake ko ta fada ai be isa ace har sauran mutanen gidan sun ji ba, sai idan ta yi kauri. Ta isa bakin kofar ta kwankwasa tana ayyana yadda zata fadawa Ammy cewar daga wani gurin ta fito ta biyo ta nan ta gaishe ta, ba dole sai ta nemi tafiya da Fadime ba ko kurwarta ta samu sa'ar kamawa ta san ya wadatar da ita.
Ta dade tana kwankwasar kofar kamin ta samu a bude mata, daya daga cikin manyan hadiman gidan nan, a take ta washewa Hadimar hakora.


“Ramatu ana nan”


“Ina nan Iya ya gidan?”


“Lafiya kalau, Allah yasa Ammy na ciki, ita dai Hajiya na gaisota tana nan ita”


“Eh Ammy tana nan amman ta shiga dakinta kuma tace kar a dame ta”


“Oh bachi take ina jin, to Babban Mutum fa?”


“Aa Shattima baya nan”


“Baya nan? Kin tabbata kuwa”


“Ba shi nan ai ba zan kiki karya ba Iya”


“Haka ne, kuma ba ku yi bakuwa ba ko? Wata yarinya haka fara yar makauniya”


“An yi ta baki gaskiya masu shigowa gaisuwa, amman babu makauniya, duk ba ba lallai na san komai domin ba kullum nake zama ba”


“Aa ita fa da yamma nan ne ko awa daya ina jin ba ayi ba”


“Gaskiya makauniya bata shigo ba, yawancin yan matan da suke zuwa wasu duk kawayen Nana ne”


“Haka ne, to a gaishe da Hajiya ni zan koma”


“Inshallah zata ji”


Iya ta juya ba dan ta yarda ba, wata kila ma Shattima ko Ammy ne suka ce mata yarinyar bata nan, waya sani ko tana can tana zuba musu surutun nata. Iya ta ji kamar ya daka tsalle ta ganta a gaban Fadime, tsabar bakinciki bata san lokacin data fara kudar hakora ba tana tsatsagarsu.


“Wallahi sai na nunawa yarinyar nan iyakar ta, ai daman na fada duk wanda ya shigo gonata nake kawarwa, ba a taba min abun da tai min ba, babu wanda ya san sirrina sai da ta zo, babu wanda ya damu da rayuwata sai da aka ka kawo min fitina, gashi har Zainab tana kokarin ballo min wani balli, lallai wannan makauniyar sai ta san ta taba maye...”


Ta yi kwafa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login