Showing 51001 words to 54000 words out of 190738 words

Chapter 18 - MUNAFUKIN MIJI BOOK COMPLETE PDF ORIGINAL ONE TO END. .txt

24 Jul 2024

17315

farin Fulanin usul kuma Katsinawa ya yi wani irin kyau da shi, yara sun zagaye shi ƴan mata nata leƙo katanga suna kallo Giɗaɗon birni, hatta matan aure kallonsa suke wasu da alwashin tattara yaransu sukai su Almajiranci don kallo ɗaya za ka yi wa Giɗaɗo kasan yana saurarawa.
"Giɗaɗona" Ya cira kai da ƙyar yana kallonta, haka kawai ya ji ransa ya ɓaci tas, saboda kwalliyar da yaga ta yi ta ci uban jambaki har ƙasan leɓe haƙoranta jajur nan da nan ya ji zuciyarsa na tashi. Hanne ta washe baki ta ce "Giɗaɗo ni ce Hannenka, ta Giɗaɗo ikon Allah dole mu saka maƙiyanmu dariya" Ya ɗaga kafaɗa a dole shi wani shege ne ya ce "Ni daman na jima da saka su kukan, tunda na je birni ko ba kiga yadda ake ta kallona ba, saboda na celeborotin a ƙauyen Nahutun Batsari" Hanne ta yi fari da ido sosai ta ce "Sai ni Hannen Giɗaɗo, mijina da izinin Allah, na haifa maka ƴa ƴa kallo su karime su Baɗejo duk an yi musu aure don ka ji" Giɗaɗo ya taɓe baki sosai yana kallon Hanne sosai da ne take burge shi yake mutuwar son ta amma tunda ya fahimci inda mata suke ya gane Hanne ba komai bace
"Dube ki da kyau Hannen Nahutun Batsari, gaskiya bana miki kallon mace a yanzu, infat ma ba zan iya auren ki ba" Shi a dole a iya turanci haka Giɗaɗo yake jin kansa, babu shakka da sarauniyar Ingila za ta jisa sai ta yi masa kukan baƙin ciki.
"Me kake nufi? Ni ce Hannenka fa? Ka manta kalle ni" Ta faɗa tana jujjuya wa. Tas ya kalleta sai ya yi miskilin murmushi ya ce "Hanne ƙuruciya, Hanne kwaila, Hanne wawta, Hanne ƙauyanci, Hanne daƙiƙanci, Hanne no no no kai Hanne ba zan iya ba" Idanunta ya cika da hawaye gabaɗaya shekarunta Goma sha biyu ne a duniya amma tana da jiki kyakkawa da ita, amma tasan soyayya ta san aure tunda tun suna yara ake aurar da su."Ban fahimta ba?"
Giɗaɗo ya ce "Kalli ƙirjinki, idan na haɗa na cure su a tafin hannu ba su fi curin tumatir ɗan biyu biyar ba a birni, mazaunanki kam sai addu'a, ina taɓe su ba zai shige yankan biredi ɗan hamsin ba, ki je kiga matan birni yadda suke da kaya murguza murguza kamar sun ɗora ai zan nemi wata kawai"
Kuka Hanne ta fashe da shi don a duniya ba wanda take ƙauna sama da Giɗaɗo fari ɗan kyakkawan saurayinta haka tana kiran sunansa ya yi burus yana ji a ransa yanzu Hanne ba tsarar auren shi ba ce.




Haihuwar Mami ta yi daidai da samun aikin da Muhammad-Bilal Ustaz ya samu a wani Lagos. Aikin banki ne a Fidelity bank plc, dake Kofo Abayomi street victoria Island Lagos. Haihuwar Mami ya ƙara kawowa Alhji Mansur Rano buɗi, sosai ya nuna farin ciki da samun fara yarinya mai tsananin kama da Mami, kyakkawa asalin kyau na ban mamaki fari kamar ya yi magana. Baffa ya ɗaga babyn da tuni an yi suna ya ce "Sai yanzu kika haifo kalar zuri'ar Mansur Rano, yarinya kalar kyau ina alfahari da samun Zainura ita ɗin cikon farin cikina ce" Ridayya dake gefe ta yi zuru da Idanu ya kalle ta ya ce
"Da an haifo mai kama da jakin dawa na gidan zoo, baƙi kamar zunubi Idanu daƙwa-daƙwa gabaɗaya suffar Aljanu ce da ita, ji nake dama ta mutu domin bata da wani amfani" Mami ta yi shiru idanunta a kan fuskar Zainura. Ammi ta ce "Haba Baffa wannan cin mutunci ne, duk lalacewar goma ai tafi biyar albarka, kafin Zainura Ridayya ce ta fara zuwa duniya" Ya yi murmushi ya ce "Maryam kenan, ke kin fi uwar yarinyar sanin ciwon ƴar banda kina son ta da tuni na cire ta daga cikin zuri'a ta don ina kokwanto da ƙyar idan ba ƴan ruwa bane suka sauya ta a ciki, domin da yaran Aljanu take kama"


"Alhaji Mansur idan fitsari banza ne kaza ta yi mana, kana da kasuwar samun kamar Ridayya ɗin? Ko zaka iya ƙera irin ta ne? Ai ko yanzu kura ta faɗi tafi ƙarfin Allah wadai" Baffa ya ce
"Bana son kina mini haushi kamar na kura Kaltum ba ruwana dake" Ta yi murmushi ta ce "Ai kura haushi ɗaya take yi wanda ka ji yau shi zaka ji gobe, ina son ka fahimce cewa ko yanzu ka mutu babu abinda zai hana Ridayya cin gadonka, daɗin abin kai ka kawo kan ka ma, idan ka ga dama ka tafi ruwan, domin Ridayya bata ɗauke ka matsayin uba ba" Tana faɗin hakan ta miƙe ta kalli Mami ta ce "Ke kuma shasha wacce bata san daraja da kimar kanta ba, yadda kike nuna ko in kula a kan Ridayya ki sani akwai ranar da za ki yi ladamar hakan ƙwarai da gaske"


Rayuwa ta juyawa Ridayya domin har Zainura ta tashi ta fara wayo bata kula ta, cikin lallami da dabara Ammi take nunawa Zainura Ridayya ƴar tsintuwa ce a gidan kuma mayya ce kar ta yadda ta dinga kula ta wannan dalilin yasa Zainura ta kewa yayar tata kallon hadarin kaji, ba ruwanta da Ridayya wani lokacin har hana ta zuwan gidan take kullum tana part ɗin Baba ƙarami wajan Abbiey. Zahura ta yi aurenta daman ita karatun bai dame ta ba, Balkisa ta karanci ɓangaren jarida tana aiki a gidan rediyon Liberty itama haihuwarta uku.


A gajiye Ridayya ta shigo idanunta lumshe saboda gajiya shekarunta Goma sha biyar ciff a duniya amma jikinta ya buɗe saboda tsananin kulawar Abbiey komai ya samu ita komai Shalale shiga matsala da damuwa da yawa sabo da ita amma ba wanda ya sanni ya ci bashi daga wajan jama'a saboda ya kula da ita nan ma babu wanda ya sani daga shi sai Allah sai mutanen. Kasancewar ta san Abbiey baya gari ya saka ranta duka a ɓace yake ta cire hijab ɗinta gashinta ya baje ta gire skirt ɗin makarantar sai ɗan ƙaramin gajeren sabon wanda da Abbiye ya siya mata ya zauna daidai da cibiyoyinta da suke da kyalli saboda baƙi ko'ina luff da gargasa ta miƙe tsaye. Madaidaicin ƙugunta a buɗe yake zaune daram Ubangiji ya bawa Ridayya dirin da surar jiki waist ɗinta tamkar ya yi magana har yanzu dai bata fara Irgan dangi ba. Ta ƙura wa kanta Idanu ta cikin madubi sosai take kallon kamar ta sai ta yi murmushi while hawaye na zuba a idanunta a hankali tana kwaɓe fuska cikin siririyar muryarta ta ce "Da gaske dai ni mummuna ce, me ya sa duka ni kaɗai ce baƙa mummuna a gidanmu? Me ya sa na girmi Zainu amma ita fara kyakkawa,me ya sa? Me ya sa?" Ta faɗa tana fashewa da kuka. Tunda Ridayya ta samu lafiya take so da ƙaunar farar fata da kwalliya gayu da ƙwalisa mutum irin haka yana masifar burgeta tasha yin kwalliya amma ita bata yin kyau.


"Ya kamata ki yi farin ciki Ridha kin kammala final exam na secondary school" Wata zuciyar ta furta hakan domin Ustaz da kansa ya saka a yi wa Ridayya tsallaken aji saboda girman jikinta kuma ya samu kwakwalwar ta buɗe tunda ya bi shawarar Headmaster ya firgitar da Ridayya ya ce ai mutuwa zai yi yau ya kwanta a gado yana kakari har ya daina motsi ranar har suma sai da ta yi sai da ya yi ladama ya rungume ta a jikinsa yana jijjigata hankali tashe. Tunda daga ranar ta samu nutsuwa idan ta tuna da zarar bata karatu Abbiey zai mutu ta miƙe sosai.


"Abbieyna ka dawo kaga na yi karatu an bani gift ka ji Abbiey" Ta faɗa tana lumshe idanunta tana jin duk gashin kanta ya dame ta. Ba tare data damu ba ta saka slippers ta nufi parlour wajan Umma ta ce mata ta dawo yunwa take ji. Cak ta tsaya jikinta na rawa da ɓari idanunta ƙuri a kan Abbiye ɗinta wanda ya hakimce a saman kujera hannunsa riƙe da kofi yana shan black tea. Jallabiyya ce a jikinsa yau sumar kansa duk a cuccure kamar baya cikin nutsuwarsa. A hankali ya saka hannu ya mayar da sumar kan nasa zuwa baya yana ɗauke hannun ta ƙara dawowa gaban goshin, ya ɗan ɓata fuska a jikinsa ya ji ana kallonsa, yanayin yadda tsigar jikinsa ke tashi ya fahimci ba kowa ke kallonsa ba sai Shalale.


"How long will it take you to stop looking at me?" Murmushi ta yi idanunta na rufe wa sai kuma ta nufe shi da sassarfa domin mamakin ganinsa ya hanata motsi gabaɗaya kwanan shi biyu ta tafiya Lagos ɗin. Tana zuwa kusa da shi ya ajjiye kofin yana miƙewa tsaya tare da ƙoƙarin yin baya zai juya yabar parlourn. Ridayya ta yi saurin rungume Abbiey fararen haƙoranta na bayyana ta ce "Oyoyo Abbieyn Shalele i miss You mardly" A kasalance ta fara idanunta da suke cike da maye a rufe. Ustaz ji ya yi ta sakar masa nauyi ya saka hannu ya ciro ta daga jikinsa ya riƙe kafaɗunta tare da jijjigata.
"Yes Abbiey.... Yes yes Wlcm back" Ta faɗa a rarrabe ganin ko idanunta ta kasa buɗewa ya saka Ustaz taɓa kumatunta wanda yake da laushi kamar audiga da ƙyar ya ce "Ustaza, open your eyes Ustaza" Dake tunda ta yi sauka yake ce mata Ustaza.


Kafin ya yi motsi ya ji ta yi baya tare da faɗuwa ƙasa tim kamar saukar buhun siminti nan take gefen kanta ya fashe jikinta ya fara da kakkarwa ta shiga cuccure wa da kanannaɗewa tamkar maciji.






Ku yi haƙuri bisa jina shiru da kuka yi ayyuka ne sukai yawa😢🥹A yafewa Mar'atussaliha Saliha idan naga comment da yawa sosai da sosai birjik zuwa anjima za ku ga new update.




08164069385
Whatsapp only please
*✿ MUNAFUKIN MIJI 18 ✿*
Mikiya Writers Ass.....




BRIGHT PENS🤙🏼 free batch






Ustaz ya bi Ridayya dake kwance a ƙasa tana juyi da mummurɗewa zuciyarsa na ƙoƙarin tsinkewa ganin kumfa na fita daga cikin bakinta ta abu kamar bugun jinnu "Ustaz ya haka ka zubawa yarinya ido cikin wannan hali, haba babban mutum" Umma ta furta tana ƙoƙarin kai hannunta jikin Ridayya. Ya furzar da iskar bakinsa ya sauke ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya kafin ya ce "Karki taɓa ta"


"Kamar ya?" Ya ɗan marairaice fuska kamar an yi masa dole ba tare daya kalli Umma ba ya ce "Hausa fa na yi, da gaske Hausa ce Umma" Ta girgiza kai ya juya a hankali tare da ɗakko hiraminsa ya rufe jikin Ridayya da shi, bakinsa na motsa wa a hankali yana mai yin addu'a tare da tofa mata.


Can ta saki fitsari a saman carpet yana bin cibiyoyinta. Ustaz dai na tsaye haka Umma na kallon abin al'ajabi domin ba'a taɓa yin farfaɗiyya a gabanta ba sai yau. "Ikon Allah, Allah ya sauwake daman haka take yi kenan? Baiwar Allah" Tausayin Ridayya duk ya mamaye mata zuciya bayan matsalar gidan uba gata zubin halitta, gata gorin kalar munin da ake mata, ga makarantar babu daɗi. Uwar data haifeta ma sam bata damu da ita ba, balle kuma uba, wata sabuwar ƙaddarar na lalura ita kanta ba ko wanne namiji ne yake ƙaunar mace mai farfaɗiyya ba, ga shi ƙanwarta Zainura kamar ba jini ɗaya ciki ɗaya suka fito da Ridayya ba haka take nuna mata.


Da ƙyar ta buɗe idanu saboda tsananin kunyar Umma da Abbiey wanda yake tsaye har yanzu, ita bata san lokacin data faɗi ba gashi duk sanda ta yi hakan sai ta yi fitsari a kwance. Basu san ta dawo hayyacinta ba sai sautin kukanta suka ji wani irin raunataccen kuka bai taɓa zuciya. Ustaz ya runtse idanunsa saboda wani irin dokawa da zuciyarsa ke masa, a hankali komai na jikinsa yake sage wa kansa ya fara sara masa da wani irin ciwo. Ya saka hannu yana dafe kan tare da furza goshinsa.
Can ya juya a ɗan fusace kamar zai yi faɗa sai kuma ya tausasa murya, daga ƙarshe ma ya rufe bakin ya fasa faɗar abinda ya yi niyya.


Yatsu ya kaɗa mata yana gyaran murya ta miƙe da sauri tana bin bayansa da sanyin jikin daya zame mata jiki komai nata a sanyaye yake yadda take tafiya kamar bata so haka take yi ko gudu bata iya ba, muryarta kodayaushe a ƙasa ba hargagi so silent, innocent gril. Ta yi jim tana leƙen bedroom ɗin can kuma ta shiga tana furta "Assalamu alayka"


Babu tabbacin ya amsa kawai tana da yaƙi nin dole zai amsa idan har ba ta yi sallama ba baya kula ta duk kalar zancen da za ta yi masa. Ganin yadda ya yi tsaye a bakin wardrobe bai kula ta ya saka Ridayya ƙara fashewa da kuka tana yarfe hannunta
"I am sorry Abbiey, ban san na faɗi ba, ban san na yi fitsari ba Allah"


Ustaz ya juya ya kalleta idanunsa duk ya shige ciki sai ya girgiza kai a hankali ya ce "Yaushe Ustaza za ta girma?" Da sauri ta ce "Yau Abbiey" Sai kuma ta girgiza kai ta ce "A'a ai ba zan girma ba, ai dabbobi basa hankali ni ma ba zan yi ba" A rikice Ustaz yana riƙe jarumarsa ya juya ya kalleta da kyau kana ya yi baya a taushashe ya ce


"You said that?"
"Zainura ce Abbiey" Ya yi shiru tana shassheƙar kuka sosai ta kama hannun Ustaz ta ce "Abbiey da gaske wai tsinto ni a kai ba nan ne gidanmu ba? Abbiey you're my father ko? Ammi ce Ya haife ni ko?" Ustaz ya rasa wacce amsa zai bawa Ridayya wacce za ta yi daidai da tunaninta ya fahimtar da ita ƙaddarar ta ce ta zo a haka? Ya nuna mata babu wanda ya isa ya ja girman ƙaddara, komai lokaci akwai sanda za ta shige. Bai dawo daga tunanin da yake ba ya ji ta saki ajjiyar zuciya.


"Abbiey mene kwaila kuma? Yau da muna yin final exam ina murna wata ce mini wai na daina murna jss 1 a dawo dani saboda ni kwaila ce kuma Kangaroo basa zuwa University. Abbiey mene kwaila kuma mene Kangaroo?" Ustaz ya yi shiru yana son Ridayya ta fahimci abubuwa da dama amma babu mai faɗa mata, babu mai nusar da ita shi ya sa wani lokacin idan ta yi magana yake girmama wawtar ta, da tunanin har yanzu ita ɗin yarinya ce gata ƴar'fari ga lalura abin ya yi mata yawa. Jin ya yi shiru ta sake marairaice fuska ta ce


"Abbiey mana, please"
Ya kama hannunta tare da janta saman kujera bayan ya zauna ta, zauna a ƙasa wajan ƙafafuwansa kan ta a ƙasa shi kuma ya zuba mata ido, yana jin yadda zuciyarsa ke dokawa da ƙarfin gaske abubuwa da yawa na farmakar shi. "Ustaza" A sanyaye ta ce "Abbiey"


Ya yi shiru ya ce
"Kina bari ana raina ki ta hanyar nuna ƙuruciya Ustaza, da gaske ba za ki girma ba har yaushe zan kasance dake haka?"


"Kasancewa kuma Abbiey?" Ta tambayata cikin rashin fahimta. Ya fasar ya ce "Wai suna nufin ba ki fara irgan su Zainu su Junaidu su Abdullah ba" Ta yi ƙuri ya ce "Wai fa nono suke nufi Ustaz idan mace nada shi ta girma if not kuma she's still a baby, kwaila ce ita" Ridayya ta zare ido sai kuma ta yi ƙasa da kanta. Ustaz ya tallafo haɓarta yana zubawa fuskarta Idanu ya nutsu yana nutsa ganinsa da kyau wai ko zai yi dace ya hango ta inda Ridayya ta samu tawaya amma ya kasa. Yasan idan ana neman asalin baƙar fata ta ƴan arewa to Ridayya ce a fusge kuma yanajinta kamar haihuwar ƙasar Ethiopia ko Mali. "Kin fahimta?" Cike da rashin sanin me take cewa ta ce


"Ni ina ruwana da wani nono Abbiey? Ai ɗan Iska ake gani da shi nikam bana so" Ya ɓata fuska ya ce "Saboda me bakya so?" Ta ce "Ai yarinya ce ni shiyasa" A ransa ya ce
"Allah ya sa motsin gado ce ke Ustaza" A fili ya ce


"Allah ya shirya mini Ustaza" Ta yi murmushi tana lumshe idanunta a hankali ya ce "Congratulations an gama school sai University daga nan kuma sai.....," Ya yi shiru ta miƙe ta ce "Sai auren Abbiey in ji Umma" Bai kalleta ba sai girgiza kai da ya yi kawai yana sauke numfashi domin tun ɗazo a takure yake jinsa ya kasa nutsuwa da zuciyarsa bai bama ga dalilin dawowarsa Kano ba a daidai wannan lokacin.


Da sauri ya shiga shagon yana duba lokaci can dai ya tsaki yana gyara sajensa daya zaune a fuskarta ya yi masa kyau, ga farar fatar nan ta shi gwanin sha'awa kyakkawa ne ajin farko, san kowa ƙin wanda ya rasa ga aji da masifar ɗaukan wanka. Ya sake yin tsaki a karo na biyu yana cije laɓɓansa.
"Ni da wajan sana'a ta ba za ka zo kana mini tsaki ba a gaskiya, kuma yau ko asirinka zai tuno ba zan baka aron kayan kowa ba. Haka kurum kaja mini jarfa jiya fa da zaka je dinner ɗin Farouk wallahi saura kaɗan mai kayan dana ɗauka na baka ya ci ubana, to neman halak ɗina nake wanda zan rufawa kai na asiri da iyayena ban ja magana ba, to ka yi kaɗan ka yi tsararo ka ja mini ita wallahi" Rai ɓace ya kai ƙarshen maganar yana ɗauko wata dakakkiyar shadda gezner blue black ta ji ɗinki sai ɗaukan idanu take ga ƙamshin turare na tashi a jikinta. Ya shimfiɗa rigar shaddar yana yayyafa ruwa zai goge domin mai ita ɗan bala'i ne. Ganin yana ta tsaye ya saka shi kada baki ya ce


"Zai fi maka kyau kasan inda dare ya yi maka, tunda ka ɗauki rayuwar da Allah bai baka ita ba ka ɗorawa kan ka, banda ƙarya da yaudarar yaran jama'a babu abinda ka iya, ba fus ba ass sai zaman kashe wando idan mota Benz ta shigo shigewa a ɗora buri da lissafin duniya a kanta, bayan ana fama da dattin aljihu" Sai a lokacin wanda ya shigo shagon ya ce


"Kasan dai zan yi arziƙi kuma zan zama millionaires?" Mai gugar ya saki dariya ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login