Showing 15001 words to 18000 words out of 190738 words
Chapter 6 - MUNAFUKIN MIJI BOOK COMPLETE PDF ORIGINAL ONE TO END. .txt
aiki, da zarar na samu aikin zan fashe gidan nan na yi miki sabo ke da yaranmu, domin har miliyan biyu za a fara bani cikin satin nan muddin yau na kai takardun nan"
Daɗin ya kama Ridayya domin da zarar Zameer ya samu aiki zata fita daga wannan wahalar kuma zai siya mata kayan ɗaki "Har nawa kake so?" Ya ce "Dubu goma haka" Ta ware ido ta ce "Tab sai dai dubu biyar yanzu aka bani aronta na ɗora jarin ƴar tsala, kuma ka san na faɗa maka yar da mukai da Baba ƙarami na cewa Bilal kuma kar ya sake turo mini kuɗi bana buƙatar taimakon shi" Zameer ya zare ido ya ce "Amma ba ki da hankali ai ban hanaki kar ɓar kuɗi wajan shi ba, taimako ne maza ki bashi haƙuri ya dinga tura miki" Da mamaki ta ce "To tunda bana son shi me zan yi da kuɗinsa? Duk wanda zai wulaƙanta ka wallahi bana son shi" Zameer ya ce "Ai ana iya zuciya da komai ban da kuɗi, matsalarku daban taimako daban, bani kuɗin" Ta ɗakko dubu biyar ɗin ta bashi. Daga nan kuma ya dinga kallonta can ya ce
"Ina buƙatar ki"
A tsorace ta ce "Bani da lafiya ka yi mini afuwa, wallahi wannan abun baya gabana" A ransa Zameer ya ce "Banda wannan dalilin ni ma ko inda kike ba zuwa zan yi ba, wannan shi ne kawai dalilin daya sa ba zan rabu dake ba"
A fili kuma ya ce
"Shikenan na gode" Ta girgiza kai ta ce "Zameer ka yi mini uzuri, bani da lafiya ba cima mai kyau balle abin ƙara lafiya da kuzari" Ya ƙanƙance ido
"Ohho ƴan'uwanki za ki bi kenan Ridha, ni kike wa gori? Ridha ni mijinki aljannarki na tafin ƙafata? Kike cewa ba cima mai kyau sata zan yi na ba ki? Ko ni zan zo ki cinye ni, to wallahi hakƙina ko kina so ko bakya so sai kin bani ai sadaki na biya"
Kafin ta yi magana ya cimmata tana kuka da ihu saboda ba daɗin abin take ji ba tsananin a zaba kawai take sha, gashi kamar mahaukaci haka zai shaƙeta idan zai nutsu, wani ihu Ridayya ta yi wanda ya yi daidai da ƙarar ƙarar zagewar wani abu keeeetttt hakan ya yi daidai da ɗaukewar numfashi Ridayya tare da yin ƙaura daga jikinta wanda yake bayyana suman da ta yi.
*✿ MUNAFUKIN MIJI ✿*
_Nimcyluv@arewabooks_
BRIGHT PENS🤙🏼 free batch
Page 6
Ruwan da Ridayya ta ji ana sheƙa mata mai sanyi ya haddasa farfaɗo war ta daga suman hucin gadin da ta yi. "Ɗinkina zai farke, ka tausaya mini ba zan iya ba wayyy...,"
Zainaba ce ta jijjiga Ridayya da ƙarfi ganin kamar bata gama dawowa cikin hayyacinta ba cike da tausayi na halin da yarinyar ta saka kanta ciki ta ce
"Ridayya lafiyarki lou? Me ya sameki na gan ki a yashe kamar gawa? Ina shi mijin naki ya bar ki haka? Wacce kalar rayuwa ce wannan?"
Maganar Zainaba ya dawo da Ridayya cikin nutsuwarta ta fahimci ba Zameer ne a kusa da ita ba balle ta saka ran samun kulawa daga wajan shi tunda shi ya cillata halin da take ciki a yanzu. A karo na farko tun kafin auren su, da bayan auren su ta ji wani irin mummunan faɗuwa da ladamar abinda ya shuɗe sun dirar matar a zuciya ta ji babu abin da bata ƙauna irin tarayyar aure, rashin mafita da yar da zata fahimtar da Zameer ɗin ya saka take biye masa ba son ransa ba, yana nuna mata ƙarfin ikon shi akan ta matsayin miji.
"Allah na tuba, na tuba Allah ka yafe mini zunubin dana aikata a baya yake bibiyata na ji a jikina, idan har haka ne gwara mutuwa da rayuwa a gare ni" Zainaba ta yi saurin rufe mata baki, ita ma hawaye ne ke sauka daga cikin idanunta kamar yar da Ridayya ke kuka mara sauti mai cin zuciya.
"Komai ya yi zafi maganinsa Allah, Ubangiji baya taɓa ɗorawa bawa abinda ba zai iya da shi ba, ba kuma ya ɗorawa bawa ƙaddarar a domin baya son shi ba, sai dai gwada imaninsa da Tauhidi" Ridayya bata fahimtar maganar Zainaba saboda tsoran daya rusketa da jin yar da ruwa ke gudu ta ƙasan cibiyarta. Zainaba ta yi saurin toshe hanci ta ce
"Ridayya warin mene wannan?"
"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Shikenan" Ridayya ta furta a raunace ganin yadda ɗinkin ya farke wajan ya yi jajur kamar yanzu ne aka yankata, ruwan dake zuba na fidda warin. Zainaba ta miƙe ta ce "Zama ai bai kama mu ba, dole a koma asibiti ki kira ƴan gidanku ki shaida musu" fahimtar kuka a rahama yake ya sa Ridayya bata damu da yadda hawayen ya tsaya mata ba, zuciyarta ta bushe tana mata wani irin suya, ta ƙura wa wajan ido numfashinta na fuska. "Babu wanda zan iya kira, domin na bar su"
"Kin bar su kamar ya?" Ridayya ta girgiza kai ta ce "Aurena za su kashe mini ta ƙarfin tsiya, suna son bawa Abbiey ni, na zaɓi mijina domin shi ne Aljannata" Baki sake Zainaba ke bin Ridayya ta ce "Kuma kin tabbata lafiya kike, ma'ana babu Aljanu a jikinki"
Murmushin takaici wanda ya fi kuka ciwo Ridayya ta yi.
"Idan ina da aljanu kawo yanzu da kin sani" Zainaba ta ƙara cewa
"Kuma babu wani asiri da tsinannan can ya yi miki?" Ridayya ta ɗaure fuska duk da halin da take ciki ta ce "Ki dai na zagin mijina cin mutunci ne wannan"
"Na ci uwar mijin ba mai ha ya ji, na ci shi ƙandas, na bisa da gudu aikin banza aikin wofi yanzu na ƙara tabbatar da bayan ƙuruciya har da rashin komawa ga Ubangiji da bijirewa iyaye" Zainaba ta ce
"Kin taɓa ganin inda iyaye suka mutu aka sauya wasu? Zaka iya sauya komai banda iyaye da dangi, hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar, iyaye ba abin wofintar wa bane Ridayya, a yau kika faɗi kika mutu jimawar duniya shi ne ki arba'in, zai yi sabuwar amarya ta tare a ɗakin da kike gadara da sunan ɗakin miji, gidan aure"
"Duk lalacewa GIDAN AURENA NE" Zainaba ji ta yi kamar ta yi wa Ridayya mugun duka, sai dai tausayinta ya danne haushin da take ƙunsa mata ta ce "Kira wannan kamilin ko shi ne ya kai ki asibiti" Ridayya ta yi shiru yanzu ta kira Abbiey ta ce masa me? Ustaz ina son ganinka?.
"Kira shi mana Ridayya ba lokaci idan ba haka ba kina kallo za ki ruɓe" Ridayya bata da zaɓin daya shige kiran Abbiey ɗin nata, idan kowa zai guje ta babu shi. Abin mamaki wayar baya tafiya tunda take bata taɓa kiran layinsa ya dawo mata ba sai yanzu. "Kiran baya tafiya" Zainaba ta yi shiru ta ce "Gashi babu kuɗi wajena, amma ina dubu biyar ɗin dana ba ki?" A hankali ta ce "Ya amsa?"
"Waye?" Cewar Zainaba duk da ta gane ta ce "Rayuwata" wata lailayayyiyar ashar Zainaba ta ƙunduma ta ce "Lahirar ki dai makashinki shege da munafukan idanunsa, dake ke makira ce uwar son miji shi ne kika kwashe kuɗin kika bashi? Ohhho ni Zainabu Abu ina ganin rayuwa a wannan gidan Munafukin mijin, Allah ka nuna mini sanda Ubangiji zai jarabci wannan mugun ya nuna mini ranar da zai ga amfanin matarsa"
Ridayya jin Zainaba take, ba don ta yar da ba ta ce
"Akwai wata Atamfa valisco da super was a akwatina idan za a samu masu siya, ki siyar mu je asibitin" Zainaba ta miƙe.
Neman duniya babu atamfofin nan sun yi ɓatan dabo hankalin Ridayya ya tashi domin sune kawai kadarar daya rage mata sai katifar da take kwana akai. Duk atamfa ɗaya ta kusa dubu hamsin haka Abbiey ke bata baya mata ƙaramar suttura. Waye zai ɗakko har ɗakinta. Zainaba ta ce
"Uhm, lokaci"
Fita ta yi babu jimawa ta dawo da kuɗi a wajanta ta dafawa Ridayya ruwa ko zani baya zama jikinta haka ta rufe wajan ɗinkin dauɗa na taso mata ta yafa ruwan. Ruwan shayi mai kauri Zainaba ta bata ta kasa sha ganinta take kamar kayan cikinta zai fita, ta dinga kiran Zameer a waya shiru baya ɗauka Maman Hajjo ta kwace wayar ta ce "Uwar me zai mana banda ƙaryar da zai shirya miki, napep na waje mu je" da ƙyar ta shiga napep suka rufe gidan tare da nufar asibiti,suka samu Nas Hajjara cikin sauri aka yi wa Ridayya komai a account ɗin Nas Hajjara aka cire kuɗi, a nan kuma Ridayya ta kwana washegari da dare aka sallame su da zummar nas Hajjara zata dinga zuwa duba ta, har sannan Zameer bai kira waya ba.
Gama shan shayinta kenan bayan sun yi sallama da Zainaba Zameer ya shigo a gigice yana zuwa ya saka hannu ya ɗauke Ridayya da mari za ta yi magana ya sake ɗauketa da mafi ya ce "Ni kika mayar mahaukaci a unguwa? Kika rufe gida kika ta fi yawon duniya abinki? Har ki kwana ki yini bin maza kika fara?"
Ta kasa magana balle kuka bakinta ya kumbura tare da ƙara tsine ya sauya mata kama abinka da baƙar mace mai rangwamen kyan halitta muninta ya fiddo fili.
Ganin yar da take jan numfashi jikinta ya fara rawa kamar mai jijjiga ya saka Zameer yin ƙasa da murya ya ce.
"My love, ban yi da niyya ba, na gigice na zama mahaukaci a wajan nemanki da gudun kar na rasa ki, tsananin farin ciki ya saka na mare ki ba tare dana tuna ba ki da lafiya" Rana ta farko da ya ce "My love, masoyiyata" sai ta nemi duka zafin marin ta rasa ta kasa cewa komai.
Ya tausasa murya ya ce
"Haba mana, ki rama idan ba ki haƙura ba" Ridayya ta ce "So kake Allah da mala'ikunsa su yi fushi dani?" Ya kashe mata ido ya ce "Well is allowed"
"Baka tambayi ina na je ba, baka kuma ka neme ni a waya ba ai kasan tana wajena" Ya shafa kai ya yi mitsi mitsi da ido kafin ya ce "Ohh ina kika je?" Ta ce "Asibiti, daka gamar biyan buƙatar rai ka fita ka bar ni yashe a sume" Kamar bai sani ba ya zare ido ya ce "Suma kikai? Ayya"
Kafin ta yi magana sun ji an ce "Sweetheart" da sauri Ridayya ta ɗaga kanta taga Khairy tsaye daga ita sai three qauter na Zameer da kuma half vest iya ƙirji.
"Me kika ce Khairiyya?"
"Sweetheart na ce"
"Yayan naki ne sweetheart? Wandonsa ne a jikinki fa? Kalli rigar da kika saka ai da haka kika fito zai fi"
Khairy ta fara yunƙurin cire vest ɗin tana faɗin "Ok bari na cire idan hakan zai fi" Zameer dai na zaune yan ta son ya juya ya kalli Khairy kaifin idanun matar tasa ya hana "Fitar mini daga ɗaki" Khairy ta ce
"Su ɗaki manya, kar fa ki manta gidan miji ne wannan ba gidan uba ba, a yanzu zai iya tafa miki rasit ki yi gaba ni kuma zama daram mai naƙuda ta samu katifa don haka ki saurara mini kar ki nemi ɗaga mini hankali"
Ridayya ta kalli Zameer ta ce "Kana jin mai ƙanwarka ke faɗa mini?" Ya juya ya kalli Khairy daidai lokacin data kammala cire vest ɗin "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!" Wanne irin tashin hankali ne "Na shiga uku Khairiyya kina da hankali? Kalli ƙirjinki a bayyane kalli yar da yayanki ke binsu da ido"
Kasa magana ya yi ya miƙe tare da ficewa daga cikin ɗakin, wani irin kishi ya turnuƙe Ridayya ta fashe da kuka, sai da ta yi mai isarta ta haƙura har lokacin bacci ya yi bai shigo ba, ga sauro kamar ya cinye Mutum.
Ganin ba a kawo nepa ba ya saka ta kunna hasken wayarta domin rage sauro. Cikin bacci kamar kuma ido biyu taga an zuro hannu tare da ɗauke wayar kafin ta motsa an yi waje da gudu ta laluba bata ji Zameer ba ta saki ihu tana faɗin "Wayyo jama'a ɓarawo.....
*Ku yi haƙuri da jina shiru bana jin daɗi ne, wannan ma da ƙyar na yi ya ɗan yi short da yawa.A ci-gaba da bibiyar labarin RIDAYYA na MUNAFUKIN MIJI😢😭 Bright pens na godiya da karɓar su hannu bibbiyu da kukai*
08164069385
*✿ MUNAFUKIN MIJI ✿*
Nimcyluv@Arewabooks
Page 7
BRIGHT PENS🤙🏼 free batch
A kiɗime ta ƙara cewa "ɓarawo, Innalillahi wa'inna ilahir raji'un ɓarawo a ɗakina, Meer rayuwata ɓarawo ya shigo mana" Babu wanda ya amsa Ridayya balle kawo mata ɗauki ta tashi zaune tare jingina da jikin bango, abu goma da ashirin ya haɗe mata. Ƴar raguwar wayar da ta yi mata saura a kadara itama an rabata da ita wai meke shirin faruwa ne. Daidai ɗaga labulen ɗakinta sa'arda nepa suka kawo wuta, hasken wutar ya haska fuskar Zameer da yake ɗan mustsike Idanu alamar bacci cikin kulawa ya ce
"Sama-sama ina bacci na ji ihunki lafiya?" Ya tambaya yana daga tsaye, domin baya jin zai iya zama a ɗakin.
Ridayya ta sauke ajjiyar zuciya ta ce "Kana gidan ashe?" Ya ware Idanu kamar zai yi magana sai kuma ya yi shiru kawai.
"Ina bacci ne ɓarawo ya shigo, ya ɗauke wayata" Zameer fuskarsa shimfiɗe da damuwar daya ƙirƙira a lokacin ya ce "Waya kawai aka ɗauka?" ta jinjina kai alamar "E" Ya ja tsaki a fili ya ce "Shi ne abin ihu a kan ɗaukar waya? Ke dai Ridayya ba ki da tawakkali Kwata-kwata, kece raki idan babu lafiya, kece surutun yunwa kamar za ki yanki naman jikina ki gasa kici, duk abinda na yi miki baya birgeka bana miki gwaninta daman kece kika zubar mini da ƙima da girmana a idanun ƴan'uwanki, ni kam na auri matar ƙaddara!"
"Matar ƙaddara!?"
Ta maimaita a fili idanunta tsaye cur cikin na Zameer domin a ko wanne yanayin a duk halin da zata tsinci kanta bata shayin sanya idanunta a cikin nasa. Muryarta na rawa laɓɓanta na karkarwa saboda ciwon ciki ta ce
"Ni kake kira da matar ƙaddara Rayuwata? Ni Ridayyanka?"
Ya ɗaga kafaɗusa duka biyun yana ƙanƙantar da idanu murya ƙasa ya ce
"Kar ki mini gurguwar fahimta, kar ki mini, ai ba kece ƙaddarar ba, ƴan'uwanki da auren sune, tunda na aureki ban hutawa raina ba, Allah ya ƙara mini haƙuri, shi ya sa magabata suke cewa Allah ya saɓa halayya"
Ikon Allah kawai Ridayya ke kallo ko dai mijin nata wani abu ya sha yau? Bai taɓa mata furuci makamancin wannan ba a hankali ta ce "Don na bar ƴan'uwana baya nufin bana son su ai" Ya riƙe ƙugu ya ce "Ba shakka, idan tururuwa ta so lalacewa, daman fiffike take yi ta tashi ai"
Idanunta suka cika da hawaye fal idan da sabo ta saba da kuka tun a daren amarcinta ta ce
"Meke damunka na rayuwata? Me na yi da zafi har haka? Don Allah ka yi haƙuri ka yafe mini"
Ya ja tsaki yana juyawa. Kasancewar a waje ya yi shimfiɗe tunda ya kammala buƙatarsa da Khairy. Juyi ya dinga yi akan tabarma shi sam ba haka ya tsara gani a auren Ridayya ba, duk abinda yake buri bai samu ba sai masifa kala-kala da auren ya jefa shi. Ridayya ta share hawayen da yaƙi tsaya mata, tana nan jingine da jikin bango, da tana da ikon tariyo rayuwarta ta baya babu shakka da ta yi hakan domin gyara ƙazantar data aikata wacce babu mamaki warinta ke bibiyarta a yanzu.
"Ƴar baƙata" Ta ji ya kirata jikinta na rawa ta miƙe zani na faɗuwa ɗuwawu a waskace saboda masifar zama waje guda ta zama tsohuwar gaske wacce masifaffiyar wahalar gidan miji ya mai da ita, daman ba kyakkawa ba domin Ridayya ko a kwatance tana cikin mutanen da za a yi kwatance da girman munin halittarsu. Domin saboda wannan yanayin nata zubin halittar ko a makarantar da aure ya datse mata ita Duduwa ake ce mata.
Kamar zata yi masa sujjada haka ta tsuguna a gabansa jikinta na rawar ɗari kar ya taɓa lafiyarta. A hankali ta ji ya ce "Sorry ƴar baƙa, raina ne a ɓace mece waya? Ni da nake saka ran siya miki zuƙeƙiya kalar ya yi, kin san komai na samu naki don ke nake fafutuka da ba ke, da tuni ina Lagos wallahi"
Ta yi shiru ya ce "Ki manta da faɗan ɗazo, zan yi miki swapping na sim ko?" A nutse ta ce
"Allah ya baka iko"
Tunawa da cewa bai tsarkake jikinsa ba ya ce "Ɗan dafa mini ruwan zafi" Ta kalle shi da sauri
"Me za ka yi da ruwan zafi a wannan tsakiyar daren?" Ya haɗe fuska da kyau yana nutsa idanunsa a nata bisa dole ya ce "Wanka, zafi ake yau" Ta dinga kallon shi haka kurum gabanta ya dinga faɗuwa ta ce
"Ba gawayi ai" kai ya bata amsa da "Amma akwai ita ce ko Ridayya?"
Muryarta a sanyaye saboda rashin ƙwarin jiki da yunwa da gajiya da surutun Zameer domin wuta take buƙata.
"Duka manya ne, babu faskararre"
A zuciye yana ɗaga murya ya ce "Kuma Allah bai azurtaki da hannu ba? Bayan rashin fasali har da nakasa ko? Ina cewa akwai gatari a gidan nan, aure ba abin wasa bane dole ki yi bautar gidan miji, da ake cewa Aljanna da wajan miji ai ba banza ba, bauta kawai aka san mace da yi a gidan miji ta yi ta wahalarta masa yana saka mata albarka, idan albarkarce bakya so sai na ji ba'asi"
Miƙewa ta yi a tsakiyar daren ta tattare zaninta shi kuma ya ɗauki wayarsa yana ƙarasa kallon wani blue film yana rufe ƙananun idanunsa. Da ƙyar ta ja itacen zufa na yanko mata haka take ɗaga gatarin tana yin faskaren ana ƙarshe tana ɗagawa ruwan gatarin ya zare ya sauka a yatsan ƙafarta wani ihu da kururuwar azaba, zafi da raɗaɗin daya ratsa jijiyar kanta ya shiga rabawa sauran jijiyoyin jikinta, ƙofofin fatar jikinta ta mimmiƙe wani zazzaɓi mai zafi ya kunno kai ya ratsa jikinta, kuka take majina na fita daga hancinta ga jini na zuba sosai.
"Ke kam an yi raguwa kamar ba mace ba? Ba har haihuwa mata na yi ba kuma su jure gabaɗaya ruwan gatarin nawa yake?"
Bata gane saboda ji take kamar ranta za a zare ya haska yatsan da wayarsa yaga farcen saura kaɗan ya cire, ya ware ido ya ce
"Tab, ɗan wannan abin?"
Kafin ta