Showing 96001 words to 99000 words out of 190738 words
Chapter 33 - MUNAFUKIN MIJI BOOK COMPLETE PDF ORIGINAL ONE TO END. .txt
yi ba, yau dole na kawo ƙarshen abubuwan da suke faruwa"
"Kaka, wacce ta haifi Abba" Yana faɗin hakan ya miƙe ta ce
"Ban gama ba" ya koma ya zauna. Ta kalle shi sosai ta kalli Mai ran ƙarfe ta ce
"Ka kawo mini dalilinka kuma na karɓa na amsa matsayin hujja mai ƙarfi, saboda yaran zamani ba ko wacce mace ce zata iya zama da namiji da ba zai sauke hakƙin aure ba. Na kuma yi wa ita Mardiyya bayanin komai amma ga mamakina ta ce mini ta amince zata zauna da kai a haka, ba zata taɓa kokawa ba, babu gori babu tashin hankali ba zata taɓa magana akan hakan ba. Wannan yarinya ƴar halak ce gaba da baya irinta kuma ake buƙata a aure ba riƙe sirrin miji dana aure"
"Muhammad idan har ka yarda ina da iko da kai ina son ka amince da batun auren Mardiyya, rashin amincewar daidai yake da cewa aurenne baka buƙata kuma wallahi zamu tattara mu bar maka gidanka in sha Allah"
Babu mai iya gane yanayin Ustaz balle ka fahimci yadda ya ɗauki zancen fahimtar halin da yake ciki daidai yake da fahimtar abinda mace mai ciki zata haifa mace ko namiji ya ɗauki daƙiƙo kafin ya fesar da iska yana kuma jan wata ciki zuwa ƙirjinta dake masa raɗaɗi a hankali ya ce "Allah ya sa albarka"
"Amin Amin. Kuma ka dinga amsa kiranta kuna hira ku fahimci juna tunda babu wani babba jagora Mai ran ƙarfe zai je da kansa Kano wajen iyayenta ya nema maka aurenta ai yarinyar nutsastsiyya ce kyakkawa da ita"
Da ƙyar ya ja ƙafafuwansa zuwa cikin bedroom ya yi shiru yana kallon abun tamkar a mafarki taya zai fara iya magana da mace shi yanzu? Balle zama gida ɗaya da ita, ɗaki ɗaya gado ɗaya bashi da wannan confidence ɗin dole ya nemi Mardiyya su yi magana important kuma confidentiality. Maganar Tajj ya gani a WhatsApp.
"Ka zo kano bana nan, wai zaryar me kake ne giss me" ya karanta sai bai bashi amsa ba.
"Munga abin arziƙi da ka yi wa takwaranka muna godiya, kasan Mimi bazawara ce ta yi idda kuma na ji hankalina ya kwanta da ita in sha Allah zan aureta amma har yanzu ban furta mata ba, bana son na yi mata dole ko kuma taga saboda na yi ɗawainiyya da ita" Sosai Ustaz ya karanta ya kuma karantawa. Can ya fara typing sai kuma ya tsaya
"Say something please"
Nan ma Ustaz ya ci-gaba da typing sai ya tsaya. "Talk mana bani da aminin daya shige kai Mohd"
"Ka rabu da ita"
Shi ne kawai abinda Ustaz ya turawa Tajj duk tsayin typing ɗin.
"But i love her"
"Ok" Ustaz ya rubuta yana fita daga whatsapp ɗin yana ganin kiran Tajj ya share.
Ta juya ta sake juyawa sai kuma ta kasa daurewa ta ce "Yanzu mene tunaninka idan Ridayya ta bayyana ana nufin haɗata aure da Babban mutum ne?"
"Haka ne" Umma ta ce
"Bana tunanin zan amince a gaskiya gabaɗaya yarinyar ta siri mini duk irin wahalar da ya yi da ita ta rabu da shi ta auri wani, sai ta jeme ta lalace take ƙoƙarin tashi daga aiki sannan za a haɗa auren?"
"Ya taɓa ce miki yana son ta ne?" Baba ƙarami ya faɗa yana ajjiye jaridar hannunsa. Umma ta haɗe fuska tana kaɗa ƙafa ta ce
"Ko da wasa amma ai wawa ba mahaukaci bane ni fa uwa ce ina fahimtar abinda ba kowa zai fahimta daga wajan Ustaz ni bana ra'ayin haka ya samu wata ya aura kuma na fara gajiya da ɓoye kai na daga wajan ɗana"
"To ba shakka sannu uwa, idan Ustaz na raye Ridayya na raye kuma bata da auren wani a kanta ita da Ustaz tamkar sun zama miji da mata ne wannan rubutaccen al'amari ne daka rubutacciyar ƙaddara"
"To wallahi idan har ina raye hakan ba zai faru ba, ka rubuta ka ajjiye" ta miƙe fuu ta yi ɗaki. Baba ƙarami ya girgiza kai yana mamakin sha'anin mata duk abinsu wani lokacin zai su shafawa idanunsu toka.
Tajj ya sake ɗaukan Ridayya zuwa asibitin bela suka ƙara duba fatarta suka sauya mata mayuka daidai da kalarta, na wanka na shafawa da kuma na sha. Kasancewar sun ga ji ya sa kai tsaye yayu gida da niyar da yamma ko zuwa dare ya je ko ya aika asiyo mata mayukan.
Wanka ta yi ta shirya Washegari Tajj ya ce zai yi baƙo sa fita gobe ta cire abayar jikinta ta bar wata ƴar top mai ƙaramin hannu da wando a jikinta iya qwiwa kayan sukai mata ainahin kyau sai baza ƙamshi yake ta sanya man leɓe a baki ta tattare sumar kan nata zuwa tsakiyar kan ta ɗaure da ribbon. Gaban goshin duk sumar ta kwanta ɗan faffaɗan ƙugunta ya zauna das ƙirjinta daidai dana ko wacce budurwa domin Little bai damu da shan nono ba. Tasan yau dole Sadauki zai zo ya kwana bakwai ciff da fara game ɗin. Bayan ta gama shiryawa ta nemi waje ta zauna kiran Sadauki ne ya shigo taƙi ɗagawa a kira na uku ta ɗaga
Ya sauke numfashi ya ce "Shanshan za ki zautar dani" Ta kwaɓe fuska
"I don't know amma kullum ƙara son ki nake" ta yi shiru
"Ridayyerh"
A sanyaye ta ce "Na'am"
"I don't know why I love you, but I do
I don't know why I cry so, but I do
I only know I'm lonely and that I want you only
I don't know why I love you, but I do....,"
"Sadauki" Ta yi saurin faɗa a karo na farko ya yi shiru
"The game is over ka je ka faɗa mata" A hankali ya ce "ko?"
"Eh" ok kawai ya ce ya kashe wayar. Sai ta ji babu daɗi ta kira shi ya ce "Ya akai?"
"Zuwa za ka yi ka faɗa mata kenan?"
"E, da matsala ne yau in sha Allah zan faɗa mata ki taya ni da addu'a Shanshan" Sai kawai ya ji ta fashe da kuka ta yi saurin kashe wayar ta cillar. Ta jima tana kuka kafin ta ji Nadra ta kinkimi Little Bilal dake bacci ta yi waje..
Da sauri Ridayya ta miƙe gudun kar ta yar da shi tunda ai yafi ƙarfinta ko takalmi bata saka ba riga da wando ne kawai a jikinta ta nufi waje tana kiran Nadra amma ina yariyar gudu take ta ƙanƙame yaron.
Idanun rufe Ridayya ke bin Nadra ta marairaice fuska duk ta ga ji yariyar ta wahalar da ita idanunta ya yi raurau da hawaye daman zuciyarta a kusa take tuntuɓe ta yi da ƙafar mutum ta yi taga taga zata faɗi ta yi saurin riƙe jikinta muryarta na rawa ta ce
"Haba Nadra ki kawo Abbiey na ga ji" ta saka hannu tana goge idanunta. Ganin har yanzu wanda ta buge da ƙafarsa bai motsa ba, bai kuma janye ba fararen jerarrun yatsun ƙafarsa da suke shimfiɗe take kallo. A hankali ta fara bin jikinsa da kallo.
Kyarma da ɓari jikinta ya ɗauka zuciyarta ta fara bugawa da ƙarfi sai da ta yi amfani da dukka ƙarfi hali da jarumta wajan sake ɗora idanunta a kan fuskarsa wacce take kwance a kan waya yana dannawa. Ji ta yi gabaɗaya wasu abubuwa na yi mata yawo he just confusing herself me ya sa yake mata gizau.
Inuwar da ya gani ta cikin wayarsa ya sanya shi kashe wayar domin shigowarsa Kano kenan kai tsaye nan ya nufi ko minti uku bai yi da shigowa parlourn ya tsaya duba wani saƙo ko zarafin zama bai samu ba. Ya kashe wayar tare da ɗago kansa was the first abinda ya a fara gani RIDAYYA tana tsaye tana kallonsa bai san yaushe ne jikinsa ya saki ba har wayar hannunsa ya zame ta faɗi ƙasa duk ƙoƙarin da ya yi amma zuciyarta da gangar jikinsa suka ƙaryata Ustaz, jikinsa ya ɗauki rawa da ɓari naman jikinsa dana zuciyarsa gabaɗaya karkarwa yake.
Mahmah da Tajj suka tsaya kallon ikon Allah ganin abinda ke ƙoƙarin faruwa a kan idanunsa rawar da jikin Ustaz yake shi ne ya fara basu tsoro zufa ta wanke shi tas hatta Nadra tsayawa kallo Uncle ɗin nata take.
Hawaye ya gama wanke fuskar Ridayya idanunta har yanzu a kan fuskar Ustaz. Bai sai yaushe ya ɗaga ƙafarsa ba samun kansa ya yi kawai ba gaban Ridayya ganin abinda ke shirin faruwa ya saka Sadauki saurin juyawa ya bar palroun hannun Ustaz na rawa ya miƙa tare da riƙo ƙafaɗun ya kasa magana sai kawai ya kifa fuskarsa a saman tata tare da....
Idan kin karanta danna share bayan kin yi comment🥰
*MUNAFUKIN MIJI 29*
Mikiya Writers Ass
Bright pens free batch
Nimcyluv
Ganin abin na Ustaz azumin ne ya saka Mahmah kama hannun Nadra ta ce "Mu je ciki"
"Ki haɗa da Junior"
Tajuddeen ɗin ya furta da ƙyar yana jin wani abu mai zafi na tsaya masa a ƙahon zuciya, mene ya shiga tunanin Ustaz har haka? Mene tsakaninsa da Ridayya girman tuzuruntakar tasa har ya kai ya fara kama yaran mutane? Gabaɗaya tunanin Tajj ya tsaya wani abu mai kama da zullumi ya fara kawo masa ziyara.
Miƙewa ya yi tare da yin waje ya bi bayan Sadauki domin ya lura da shigowar tasa da kuma sauyin daya gani tattare da shi ɗin.
Bakin Ridayya ne ya fara rawa idanunta a fuskar Ustaz har yanzu ta kasa kallon cikin idanunsa wanda kuma hakan shi yake buƙata, jininta na rawa tana jin saukar numfashinsa a fuskarta yana saukar mata saboda fuskarsa dake ɗan rakaɓe da nata ya kasa furta komai. Da sauri kuma ta yi saurin zame fuskar tana yin baya tare da ƙare masa kallo.
Sai kuma ta shiga girgiza kai while hawaye running down on her face. Ta buɗe baki cikin firgitaccen yanayi ta ce
"Mafarki nake da gaske mafarki ba kai nake gani ba, irin mafarkin dana saba yi ne a kullum a koyaushe ba zaka taɓa zuwa gare ni bakai bane you're not my father...... My Abbiey is dead, he is in the grave"
Baki Ustaz ya buɗe zai yi magana ya kasa ta yi saurin cewa
"Me zaka ce? Shiru ko na san mafarki nake ni kaɗai ce bani da kowa sai wanda yaga Allah ya taimaki rayuwata me ya sa zaka bar ruhinka ya fito domin ya firgitar dani Abbiey why why why?"
"Don Allah ka yi magana ka ce kai ne ka dawo gare ni baka mutu ba, wayyo Allah wayyo ni Ridayya na shiga uku"
Ji ya yi kamar an saka sofa glue tare da manne masa laɓɓansa ya kasa buɗe baki balle furta komai ya kasa nufar inda yake da tunanin idan ya riƙe ta da hannayensa zata dawo cikin hayyacinta da nutsuwarta. Duk dauriyarsa da yadda ya so riƙe kansa kasawa ya yi jikinsa ya shiga ɓari hatta laɓɓansa rawa yake baya son tunkararta kai tsaye domin a farkon ma, tsananin ta'ajjuji ya saka shi yin hakan da son fahimtar da gaske ita ɗin ce tsaye a gabansa shekaru nawa? Wata nawa? Kwanaki nawa? Mintunawa nawa? Daƙiƙo nawa ya shafe yana jiran wannan ranar?
Abu biyu ne zai faru idan ya ƙarasa wajan wanda kuma a yanzu bai isa ya hana zuciyarsa da gangar jikinsa hana afkuwar hakan ba, domin baya da iko da su a yanzu sune suke jan ragamar shi. Idan bai riƙe Ustaza ya sanyata cikin jikinsa ta jiyo ɗuminsa wanda ta saba da shi tun tana ƙaramar, to idan bai hakan ba yasan sauran abinda zai biyo baya shi kansa bai sani ba yana tabbacin sahihiyar runguma ce zata samu matsayin tarba a gare shi.
Yana kallo ta juya tare da shigewa ɗaki ta rufe ƙofar kai tsaye kuma zaman dirshen ta yi saman carpet ta saki wani irin raunataccen kuka na ƙuncin rayuwarta. Tunanin Abbiey har ya kai ya dinga zuwar mata idanu biyu? Ya fito daga kabarinsa yana wasa da tunaninsa tasan tunda ya kasa furta komai to wannan mutum mutuminsa ne kuka take da iya ƙarfinta har sai da ta ga ji ta fara shassheƙa tare da kwanciya saman carpet ɗin duniyar ta mata zafi cikin wani irin sounds na fitar hayayci ta ce
"Allah ya isa Zameer Allah ya isa ka rusa mini rayuwata ka hanani sukuni da jin daɗi na yi regretting sanin ka a rayuwa, ka yi amfani da rashin gata na, rashin farin ciki, kushe da zunɗen da ake mini a kan halittar da Ubangiji ya yi mini ka yi amfani da son da nake maka ka rabani da jin daɗina ban san haka ɗabi'unka suke ba ashe kura ce da fatar akuya ashe kyan ɗan'maciji ka yi ka zame mini ƙarfen ƙafa bani da sukuni sai na fargabar abinda za ka iya yi mini. Ka zame mini MUNAFUKIN MIJI ba tare dana fargaba ka yi mini illa ka yi mini shamaki da dukkan wani ɗa'namiji babu mai dubana idan ya ji zumubin dana aikata saboda soyayya!"
Wani irin ɗaci take ji a duk sanda ta tuna lokacin data bawa Zameer kanta wai saboda kar ya daina son ta ya koma wajan wata ko ya fasa aurenta. Batun bidiyon da ya yi musu ya fi komai ɗaga mata hankali video ne da zai iya taɓa career ɗinta dana iyayenta da suna raye a ranta take jin ko zai yi sanadin da kowa zai guje ta; ta zama mujiya ba zata taɓa komawa auren Giɗaɗo ba.
A tsaye nan Mahmah ta fito ta ruske Ustaz ya gama haɗa zufa fuskarsa ta yi jajur wanda yau ne kaɗai ta taɓa ganinsa cikin hakan, dukda ba komai ta sani game da Muhammad ɗin ba. Ta kalle shi ta ce
"Babban Mutum ka zauna mana, ina fatan yau zaka tsaya kaci abinci ko?"
Numfashi ya haɗiye zuwa cikin bakinsa kafin ya yi magana Tajj ya shigo ya nuna kamar bai ga komai ba ya ce
"Saboda Allah ka mayar da hanyar Leges da Kano kamar wajan wasan yara? Kodayake kuɗi ke ake shiga jirgi baya yi maka wahala"
"Ni ai na ji daɗin hakan ya fi samun nutsuwar zuciya gabaɗaya ya sauya tamkar ba shi ba" cewar Mahmah.
Ustaz ya tattare nutsuwarsa yana juyawa zai fita, sai da ya je bakin ƙofa ya tsaya ya ce
"Zan buɗe baki a nan in sha Allah Mahmah,
Bari na je muga?"
" To to ma sha Allah babu laifi a dawo lafiya, yau na tarki sa a" Murmushin yaƙe kawai Tajj ya yi yana bin Ustaz da idanu tare da mamakin abubuwan da suka faru a yanzu ɗin kamar gilmawar walƙiyya.
"Wacece Ridayya mene haɗin ta da Bilal abinda ya faru ya yi confusing ɗina, dana juya naga Little na ƙara kallon Ustaz sai tsoro ya kamani kamannin Muhammad-Bilal nake gani kwance a fuskar Little hakan ya tabbatar mini akwai alaƙa mai ƙarfi ta jini a tattare dasu duka biyun, da Ustaz ya yi aure zan iya cewa wannan yaron jininsa ce ya fito ne daga ƙwan halittar Ustaz na haihuwa"
"Tajuddeen ina magana"
Mahmah ta faɗa tana taɓo Tajj daya zurfafa a tunani, ya tuna sanda Majnun yake cewa Ridayya ita ce wacce ta bashi tsoro a lokacin a area ɗin su Ustaz ne, ya tuna sanda ya yi mata gani na biyu furucin data faɗa ta kira sunan “Abbiey” abu mai muhimmanci kamannin Ustaz da Little da yadda Ustaz ya riƙe fuskar Ridayya ɗin banda yana da kusanci da ita ko farcenta ba zai taɓa ba. What is going on? Meke ɓoye?
Ya miƙe tsaye yana ƙara zurfafa tunaninsa a matsayinsa na police mai rang ɗin DCP a firgice yana dafe kansa ya ce "Bilal's adopted daughter?"
"No! But how ya akai ban taɓa tsayawa na yi tunani a kan haka ba? Why Tajuddeen mene ya saka duk wannan wahalar da Ustaz yake sha na neman yarinyar nan ashe ina tare da ita? No wonder Ustaz ya damu da batun Junior ashe jininsa ne tsatson shi" Tajj ya shiga damuwa lokaci guda amma daya tuna wani abu sai ya ji damuwar ta kau babu ita dole ya idda nufinsa a kan buƙatar zuciyarsa.
Zama ya yi tare da yi wa Mahmah bayanin komai ta jinjina kai ta ce
"Allah Alhakkamu sarki gagara misali Ubangiji ya sa ƙarshen wahalar kenan, Allah ya jiƙan iyayensu da rahama gaskiya na yi wa Muhammad murna da farin ciki dole ya ruɗe sosai shekarun da yawa kuma akwai shaƙuwa tsakanin zuciyoyin guda biyu"
Ustaz na fita motar da yake amfani da ita idan ya zo Kano ya shiga, ya jima yana sauke numfashi da tunanin ta inda zai ɓulluwa lamarin Ustaza da kalaman da zai yi amfani da su wajan rarrashinta na nesan ta kansa da ya yi da ita, zai ɗauki duka laifi ya ɗorawa kansa ita ɗin yarinya ce kuma macace mai tarin rauni da ƙalubale bata da wani zaɓi zai amshi laifin da hannu bibbiyu.
Ya miƙa hannu da ƙyar ya daɗo gudun a.cn motar tare da kunna karatu duk dan ya samu nutsuwa zai ciccije bakinsa yake komai na Ustaz special ne daga yanayin kallonsa zuwa buɗe baki da sarrafa harshensa. Ya ɗauki lokaci kafin ya zame hular kansa ya ajjiye a gefe sumar kansa ta baje ta sakko wacce ta sha gyara da saloon ya yi key tare da yin Bismillah ya bar gidan bakiɗaya.
Har bayan la'asar Ridayya bata daina kuka ba, kewar Abbiey ya dame ta domin da gaske bata yar da shi ta gani a ɗazon ba. Tana zaune ta idar da sallah tana karatun Alkur'ani ko ta ji sauƙin raɗaɗin da zuciyarta ke yi mata wayarta ta fara ringing ta duba a hankali taga an saka “Sahibi”
Ta lumshe idanunta ƙofofin zuciyarta na buɗewa ba zata manta ba shi ne ya yi saved number a haka ta ɗauki kiran tana manna wayar a kunnenta.
"Hello"
"Amincin Allah ya tabbata ga ruhin Hamza Hamdan Hamish barka da yamma Shanshan"
Ya faɗa a kasalance ta cikin wayar yana sauke ajjiyar zuciya. Ridayya ta ɗan juya idanunta a nutse ta ce
"Ina yini ya mother?"
"Ni ba ki tambayi ya nake ba sai mother, ni da mother waya fara saninki Shanshan?"
"Yi haƙuri to ya kake?"
Ya mirigna daga hagu zuwa dama yana rungume pillown kusa da shi a hankali muryarsa very slowly and sadness ya ce
"Cewa za ki Mijina ya zuciyarka take ba ya nake ba" Ta yi shiru.
Cikin serious magana ya ce "Ridayya"
"Na'am"
"Waye naga ya riƙe ki ɗazo? Ya riƙe miki kafaɗu?" Ta ɗan yi jim tana tunani ita kam ai babu