Showing 183001 words to 186000 words out of 190738 words

Chapter 62 - MUNAFUKIN MIJI BOOK COMPLETE PDF ORIGINAL ONE TO END. .txt

24 Jul 2024

18764

aikin sai ɗan Amina oga shi fa TAHHB ɗan balaja'u ne ko a rukunninsa ba kowa ya san shi ba" da mamaki Dr Ghali Uba yake kallon Shazali a ran shi yana tambayar who is MUTALLAB TAHHB?


Mardiyya ta yi tsuru-tsuru lokacin da ƙawarta ta shigo gidan daman shirye-shiryen kai Ustaz koto take yadda ta ƙarfi za a mallaka masa yarinyar. Umma ta juya ta kalli wacce ta shigo haka Baba ƙarami da Junaid da sauran mutanen wajan "Baiwar ke fa?" Cewar Aliyu kafin ta yi magana Umma ta ce "Na san wannan fuskar ƙawar wannan ƴar iskar ce" cikin sauri Mardiyya ta ce "Laa ni ban santa ba, ban taɓa ganinta ba sai yau" da wani irin mamaki ƙawar ta ce "Idan ba ki ce haka ba ai ba ki cika cikakkiyar munafuka ba, ke har ni za ki kalla ki cewa haka? To bari ki ji I'm not coming for this ga uban yarinyar da kika haifa can waje yana jiranki" gaban Mardiyya ya faɗi ƙirjinta na dukan saba'in saba'in ta ce "Ban gane ba" ta ce "Oh bari na yi yadda za ki gane" ta juya ta kalli Ustaz ta ce "Sanda Mardiyya ta aureka tana da wanda take so, kuma maganar aure ya shiga tsakaninsu ma, tunda ta je gidan Ridayya suka samu saɓani ta ɗauki alwashin sai ta aureka, bayan an yi auren ta cigaba da mu'amala da Yaƙub suna haɗuwa a hotel kala-kala har mu'amala ta gitta tsakani ta samu cikin, hankalinta ya tashi domin a lokacin ta ji ta fara sakon ka gashi kana ƙoƙarin zama Gwamna, tana ta neman hanyar da za ku yi tarayyar aure saboda ta ɗauki bidiyo ya zama evidence na cewa cikinka ne, domin bata taɓa kawowa ranta zata haihu baka kasance ta ba, domin tabbatar da abinda nake faɗa ka je waje ai za kaga Yaƙub ɗin" Ustaz ya kasa cewa komai jin abinda yake kamar a littafan Hausa ko dram na film, ya juya tare da barin wajan. Mardiyya ta durƙushe a wajan tana rusa kuka bata taɓa ladamar abinda ta aikata ba sai yau, gashi wani irin mugun son Ustaz take kamar rai ji take kamar ta haɗeye shi ta hutawa ranta. Zuwan Hajia kenan ta ce "Amma dai kin watsa mini ƙasa a idanu Mardiyya, na yi bake bake raina bai huta ba sai dana ga kin auri yaron nan ashe tsatsa tuni ta cinye zuciyarki, to maza maza haɗa kayanki ki ɗauki ku yi gaba zuciyata har nunfashi take wajan ganin na ci miki mutunci" Inna ta ce "Ni dai daman zaman wanka na zo tunda abin ya zama haka ya lalace sai dai na ce Allah ya baku haƙuri amma tabbas anci mutuncin aure an kuma taɓa martabar aure" Tana kaiwa nan ta ja jakarta ko inda Mardiyya take bata kalla domin zata iya ci mata mutunci naƙin ƙarewa.


"Umma don Allah ki rufa mini asiri ka saka mijina ya mayar dani, wallahi na yi ladama ba zan kuma ba sharrin shaiɗan ne" Umma ta zare idanu ta ce "Wanne shaiɗan ɗin kuma? Ai kece shaiɗaniyyar kan ki wallahi kuma tsakanina dake Allah ya isa, ki yi gaggawar fito mini da takardar filin dana ba ki" ganin da gaske ta rabu da Ustaz rabuwa ta har abada ya saka Mardiyya miƙewa tana goge hawayen idanunta zuriyarta na yi mata wani irin zafi da ƙona ta ce "Ai fili na takwararki ne Hadiza, kamar yadda shaidu suka tabbatar tuni na siyar da shi na siya mata wata kadarar"


"Kika siyar mini dame? Dukiyar tawa akan ƴar zina?" Mardiyya ta ce "Bafa nina ce ki bani ba, da hannunki kika ɗakko tare da mallakawa cikina shi, da saka hannunki da komai, idan ba ki yarda ba kina iya kaiwa koto" tana kaiwa nan ta ɗauki yarinyarta tana cewa "Ga Hadiza ga takwarar Hadiza" Umma ta dinga tsinewa Mardiyya albarka duk irin cin mutuncin da takewa Ridayya bata taɓa yin tari ba balle tai mata kallon banza, yau wacce ta zaɓa ta fifita ita ke kiran sunanta haka tsirara. Baba ƙarami ya dinga murmushi daman wannan ranar yake jira gashi lokaci ya yi yana danne dariyarsa ya ce "Sai haƙuri,surikar so kuma surikar gwal da kika fifita ce akan zaɓin da ƙaddara taiwa ɗanki ce fa? Mardiyya fa? Haba Umma a dinga sara ana duban bakin gatari" Umma ta sake fashewa da kuka ta ce "Daman ai kana sani ka sawa shegiyar yarinyar suna Hadiza,kuma wallahi bani Hadizan ba" Ridayya na can part ɗin Mami bata san meke faruwa ba sai da Zainura ta shiga take bata labarin komai, ita kam ko a jikinta haushin Ustaz ɗin ma take ji.


A daren Ustaz ya saka Baffa a gaba akan ya yi haƙuri ya saka a saki Ammi haka nan tasha wahala da ƙyar ya shawo kan Baffa ya yi wa aka saki Ammi amma ya ce ba gidan shi ba, Junaid ya ɗauke ta zuwa gidan daya siya mata daman ya san zai wahala Baffa ya yafewa Ammi ta sauƙi. Ta dinga kuka tana bawa Junaid haƙuri da sauran yaran banda Yaya Zuhura ko wajanta ma bata je ba, domin ta ce ita ta sake uwa.


Prof na durƙushe gaban Hajja Azizat idanunsa sun ɗauka tare da yin jajur saboda damuwa da tashin hankali, abubuwa sun masa yawa ga matsalar takara daya samu domin tuni an sauke shi an bawa wani, ga matsalar Talatu ƙarin kunama data ke shirin tattare arziƙinsa saboda barazanar da take masa akan bidiyon data ɗauka duk ya fita hayyacinsa, ya yi gurfane kamar mai neman ɗauki ya ce "Me ya sa kika kasance mai taurin kai ne? Mara yafiya da duba baya?"


"Baya? Wanne bayan zan duba kenan Prof?" Hajja Azizat ta furta cikin yanayin mamaki dake cin zuriyarta lokaci guda kuma ta juya tare da zuba masa idanunta masu kaifi ya ce "Ki tuna ni ɗin mijinki ne zuri'a ta shiga tsakaninmu, karki duba kuskure na ki yafe mini ki dawo gidanki ƙarshen igiyar aurenki" ta cije baki tana girgiza ƙafarta ta kasa furta komai saboda yadda zuciyarta ke mata zafi, bata taɓa dana sanin auren Prof ba sai yanzu, ba shine irin mijin daya dace da ita ba, rabon Sadauki daya rantse shine ya ƙaddara auren nasu Sadauki ya rasu he is no more don haka dole auren ma ya rasu.
Ya miƙa hannu zai kamo ƙafarta ta yi saurin zamewa ya ce "Ki tausaya mini sharrin shaiɗan ne, wallahi ina matuƙar son ki da gaske i don't know what come over me nake aikata zunubin da bai dace ba, i love you i so much love you Azizat" Mother ta yi murmushi tana miƙewa tsaye ta ce "You know what Prof? Fita a parlon nan kafin zuciya ta ɗauke na faɗa maka abinda har ka mutu baka mance ba" ya miƙe tsaye idanunsa sun ƙara jirkicewa ya ce "Don girman Allah ki tausaya mini Azizat do you know how much I love you, kin san yadda nake son ki kowa? Me ya sa ba zaki yadda da ƙaddara ba? Eh?" Rai ɓace ta juya zata shige cikin gidan daman a parlon farko suke ya yi saurin kai hannu ya jawota, kafin ya zame hannunsa ta ɗaga hannu tare da sauke masa wani gigitaccen mari a kunci da yatsa ta ce "Kul! Ko da wasa don't even try to do, jikina ba irin na karyan matan da kake mu'amala da su bane Prof, a tsarkake nake kuma na gode da tsayin shekarun daka dinga tauye haƙƙina ashe hakan alheri ne a gare ni, wallahi tallahi na yi ladamar aurenka na ji inama ban taɓa aure ba" ta share hawayen idanunta don kar rauninta ya danne zafin zuciyar da take ciki ta ce "Me kake tunani dukiya shine aure da jin daɗi da kwanciyar hankali? An faɗa maka dukiya na kewa, ana yin aure ne domin raya sunnar ma'aiki, tare da tattali da soyayya da kulawa, haɗe da kare mutuncin juna da martabar aure, ban yi zaton soyayyar da kake nuna mini iya ta waje bace, baka san ka zauna da matarka ku yi hira ba, baka san ka sauke haƙƙina da ke kan ka ba, baka son ka zauna a gida cikin iyalanka, kai maƙaryaci ne you're a liar, cheater, hypocrite, adulterer, you're nothing but my destiny, you kill your own child saboda rashin kulawa da tsoran Allah irin naka" Prof ya dafe kunci ya ce "Ni kika mara Azizat? Ni kike zargi da kashe ɗana Sadauki?" Murmushi ta yi tears running down on her face tana girgiza kai she couldn't feel yadda take jin zuriyarta a lokacin.


"Zan iya yi maka abinda ya fi haka, wallahi na tsaneka kuma ka gaggauta rubuta mini sakina ba zan taɓa iya cigaba da zama da kai ba, daman can kasancewar mu tare zanen ƙaddara ne kuma yanzu ta sake rabawa" shi kansa Prof a sama yake jin maganganun nata, bai zacci girman son da ya kewa Azizat ya kai har haka ba sai yanzu da ƙaddara ke barazanar raba shi da ita, sakaci da son zuciyarsa sun takawa rawa wajan yin fatali da muradan zuciyarsa dana iyalansa ya duƙa saman ƙafafuwansa ya ce "Let by gone be by gone Hajja Azizat, wallahi ba zan ƙara bari mummunan zuciyata ta kwaɗaita mini wata sura ba face take, ki yafe mini na bi Allah na biki please ki yi komai zan ɗauka banda rabuwa da ke" kasa ce masa komai ta yi sai ta juya ya yi kamar zai bita ciki tana zuwa ƙofa ta ce "Mu haɗu a koto" Prof ya jingina da jikin bango yana dafe kansa ya bita da kallo har fa shige ciki. Tana shiga ɗaki ta ji kanta na sara mata ƙirjinta ya yi mata nauyi mutuwar Sadauki ya dawo mata sabuwa ta dinga kuka kamar ranta zai fita har bacci ya ɗauke ta.


Kwanaki biyar da dawowarsu Nigeria Ridayya ta shirya zata asibiti a ƙara duba jikinta tana sanye cikin ash ɗin Abaya ta yi rolling kanta sosai ta yi kyau ta ƙara cika da buɗewa, hankalinta ya kwanta ga kulawar da take samu a wajan Mami da Yaya Zuhura da Anty Kaltum, domin sosai Anty Kaltum ta tura Maiduguri aka amso mata tsumin mai jego hakan ya saka Abbiey daƙulewa ya rasa abinda ke yi masa daɗi, har baya so Ridayya ta ƙarasu kusa da shi sosai yake gigicewa, gashi baya da sukuni a gidan yana ta sauri su koma gidansu domin an kammala komai na hadaɗɗan gidan. Dawowarsa kenan daga duba babban boutique ɗin da yake haɗawa da Sunan Ridayya, business yake sosai kuma Ubangiji ya saka masa albarka dukda cewa Fidelity bank suna ta masa requesting ya dawo amma ya nuna bai son aikin bankin yanzu. A hankali ya juya tare nutsa ganinsa a kanta ta yi masa murmushi shi kuma ya kame fuska sai kallon ta yake har ta ƙarasu kusa da shi ta zauna tana sake kyakkyawan murmushi a hankali ta saka hannu ta shafo gemunsa ta ce.


"Barka da hutawa Abbiey"


Ya ɗauke kai yana mayar da idanunsa saman laptop ganin hakan ya saka ta marairaice fuska ta ce "Me na yi kuma?" Still ya yi mata shiru wayarsa ce ta fara ringing suka kalli wayar lokaci guda sunan Muwahib ya fito, Ridayya tai shiru tana tunanin ina ta san sunan?. Ustaz ya gyara zama yana matsar da laptop ɗin tare da ɗaukan kiran a taushashe ya ce.


"Kina lafiya Wahib?"


Ya faɗa bayan amsa sallama ɗin, Ridayya gabanta ya faɗi who is Muwahib? Da har Abbiey ya bata dukkan attention ɗinsa haka? Bata san me take ce masa ba sai gani ta yi ya miƙe yana ɗan jan gemunsa ya ce.


"Ohh, i will come"


Ya kashe kiran kana ya kalli Ridayya da kanta ke ƙasa ta yi nisa cikin tunani sai ganin shi ta yi ya duƙa gabanta tare da tallafo fuskarta a tafin hannunsa taƙi yarda ta kalle shi ya kai baki ya sumbaci lips ɗinta ta yi saurin janye fuskarta


"Ina za ki?"


"Asibiti"


Ya haɗe girar sama data ƙasa yana sake matsar da fuskarsa dab da nata tare da sauke mata nunfashi ƙamshin bakinsa na shigar mata hanci a hankali ya ce "Wa kika tambaya"


Muryarta na rawa ta ce "I toot i told you"


"Ko?" Ta yi sauri ta miƙe ta ce "To na fasa, ka je kiran Wahib ɗin"


Ta juya zuwa bakin ƙofa ta fara ƙoƙarin buɗe ƙofar zata fita hawaye tuni ya fara cika idanunta tana gani dishi-dishi saboda tsabar kishin daya mamaye idanunta tana tsaye ta ji ya zuro hannunsa ta baya ya saƙale ƙugunta tare da haɗe shi a nasa, ya rungume ta ta baya ya ɗan ranƙwafa ya ɗora kansa a kafaɗarta ya ƙi cewa komai sai kawai ta fashe da kuka tana doke hannunsa, ya sake matseta a ƙirjinsa da kyau, he just trying to explain to her, wace Wahib and who is she to him, taƙi yarda ta ji sai kuka take ai kowa ya nuna mata da wayo, ya kinkimeta gabaɗaya ai kowa da sauri ta riƙe shi ta ce


"A'a don Please"


Ya matse ta jikin bango ya ce "Ok listen" ta ce "Oh oh ok"


Ya ƙura mata she just love her, yana tsananin son matarsa bawai tsoron ta yake ji ba ko shakkata ba, baya son damuwa da ɓacin ranta musamman abinda ya san shine da laifi, haka yanzu bai ma san dalilin daya saka zai yi mata explanation ba.


"She is my ex"


A gigice Ridayya ke kallon shi jin abinda ya ce, ya ɗage mata gira idanunta ya sake cika da haway yana shafa mata fuskarsa ya ce. "Ina son aurenta ne beb" kallonsa kawai take babu ko ƙiftawa ƙirjinta na ɗagawa kamar mai Asthma cikin sauri ya ce


"Kee wasa nake miki, ɗalibata ce ta ma yi aure mijinta ne ba lafiya take neman taimako"


"Ka aure ta mana"


Ta faɗa zata shige ya ƙara damƙo ƙugunta ya haɗa da nasa idanunsa ya sauya "Da gaske nake miki Allah" nan da nan ta fashe da kuka kamar ranta zai fita tana yarfe hannu


"To ka aureta mana ai ban hanaka ba ban isa kuma na ce a'a, daman na san ba sona kake ba, u just manage kawai daman ban cancanci ka aure ni ba, ƙaddarar su Al'hussan ya saka ka taimake ni ne kawai kamar yadda ake cewa ni dai na son ina son ka amma don baka so ni ba wani abu bane it's all my fault"


Ba iya jijiyoyin kansa ba, hatta gargasar jikinsa ta gama miƙewa gabaɗaya ya jima tashin hankalinsa bai bayyana ba ƙarara irin yanzu ba, so daman auren under age haka yake? Mutum da girmansa da gemunsa da shekarunsa ƙaramar yarinya like Ridayya ta yi ƙoƙarin sukurkuta masa tunani da lissafi domin tashin hankalin daya shiga ya ninka nata. Ya dafe kansa kana ya kamo hannunta har zuwa bakin gado ya zaunar da ita saman cinyarsa ya riƙo tafin hannunta ya sarƙe da nasa ya kasa cewa komai ta kwantar da kanta a ƙirjinsa tana shassheƙar kuka wanda duk na ƙarya ne kukan banza ne kawai, ya sauke numfashi.


"Ustaza"


"Abbiey"


Ya juyo da fuskarta ya ɗora goshinsa a kan nata ya ce "I am sorry ok?" Ta jinjina masa kai ya haɗe rai ya ce "Talk"


"Na bar Al'hussan zazzaɓi yake"


"Ok ki shirya I'll drop you off beb" ta jinjina kai tana miƙewa ya miƙe shima ya rungume ta.


"I love you beb"


"Thank you"


Ya ware idanu "Are you still angry with me? Ni me zan yi da mace bayan ke? Kin isheni kin kuma wadata ni da komai, soyayya, biyayya anything Mimi ai ba wata bayan ke no one but you Mintyna"


"Uhm'uhm" ta ce cikin shagwaɓa tana turo baki wanda ya sha lipstick. Ya girgiza kai "Allah ya yafe miki Mimi"


"Amin"


"I love you "


Kutunsa ta sumbata ta ce "I adore you"


Ita ta yi driving nasu zuwa asibiti ya ce sam ya gaji, yana riƙe da Sadauki Zainura na baya ita da little da Al'hussan a hannunta Al'hassan sai bacci yake a cikin wani ɗan ƙaramin gado. Bayan sun ga likita suna ƙoƙarin fitowa daga emergency Ridayya ta ji ana "Me haƙuri me haƙuri" da wani irin murmushi ta juya domin ba zata taɓa mance muryar ba, Abbiey na jingine da mota yana kallon su "Wa zan gani kamar Zainaba?"


"Ni ce nan mai ƴartsala ikon Allah rai kan ga rai" Ridayya ta yi murmushi suka gaisa cikin farinciki ta ce "Ina mijin naki, wai da gaske kece haka mai ƴartsala?"


Ridayya ta yi mata pointing ɗin Abbiey ta ce "Ga mijin nawa can da yarana"


Da sauri Abbiey ya ɗauke kansa kamar bai gansu ba, Zainaba ta zare idanu ta ce "Lillahi wadihul ƙahhar Allah alhakamu, wancan ba shine kikaiwa iskanci kala-kala ba? Ina Zameer ɗin?" Ridayya ta haɗe rai ta ce "Kin jiki da wani zance?"


Zainaba ta yi ƙasa da murya ta ce "To kin bashi labarin abinda ya faru da jami'a kafin aurenku da tsinannen nan?" Ta girgiza kai ta ce "A'a, ina so ya san komai amma" Zainaba ta zare idanu ta ce


"A'a sam kar ki soma, idan Allah ya rufa maka asiri sai kace zaka tunawa kanka? Wallahi ki gode Allah Ubangiji ke son ki da Rahama tunda har ya rufa miki asiri ki yi shiru da bankin, ai idan Allah bai so kunyataka a idanun duniya ba babu wanda ya isa ya yi haka, Allah ya duba zuciyarki ribatarki akai bada sunan iskanci kika je ba" Ridayya ta yi murmushi ta ce "Ga numberta idan na tare a gidana sai ki zo" "Ai kowa in sha Allah za ki ganni faka-faka"


"Mai sona"


Da sauri ta juya ganinsa a wannan halin ya saka Ridayya waro idanu ƙirjinta na bugawa, kafin Zainaba ta yi magana ya zube ƙasan qiwwarsa ya ce "Don Allah ki ji tausayina ki yafe mini Mai sona, karki bari na zauce a tunaninki a zuciyata ki tausaya mini"


Moo ya ƙarasu wajan ya ce "Wai Zameer mene haka? Ba zaka ɗauki ƙaddara bane kai? Aurenta zata kashe ta dawo wajanka?"


"Ba wani aure da ta yi kawai an faɗa ne domin a rabani da ita, a hukunta ni akan kuskure da wawta tare da son zuciyar dana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login