Showing 39001 words to 42000 words out of 166068 words

Chapter 14 - UWAR SADIKU COMPLT BY SAKINA YAZID.txt

11 Jul 2024

25392

mata kuma ya nuna mata abinda yake faruwa kada taje ta cutar da su ita da Abban Sadik din.
……

Ranar Alhamis ce, kamar yanda suka saba a kwanakin nan Yusra ce da Nana a zaune a falon Aisha bayan sallar la’asar. Kallon TV sukeyi ta tashi ta shiga kicin ta dora abincin dare; tuwon miyar kuka ta dora wanda bayan ta sa komai a wuta ta fito daga kicin din ta shige daki.
Tana shigewa Yusra ta dubi Nana tace

‘Ki zauna a nan kada ki taso bari na samo ruwa na sha.’

Tayi sauri ta fada kichin din.

Da gaggawa ta karasa kusa da cooker, ta kai hannu ta dauki murfin tukunyar miya ta ajiye a gefe. Ta zaro 'yar farar ledar da ta ke daure a jikin siket dinta ta bude, da sauri ta debi abinda yake cikin ledar ta barbada a miyar ta juya ta kulle ledar ta rike a daya hannunta. Ta dauki murfin tukunyar wanda murfin glass ne tana kokarin rufe tukunyar, bata san yanda aka yi ba murfin ya subuce ya tarwatse a kasa. Karar faduwar murfin ya sa Aisha ta karaso kichin din da gudu wadda dama tana hanyar dawowa kicin din, itama Nana da sauri ta karasa kicin din.
Yanda Yusran take kallonta tana rawar jiki ya sa ta san bata da gaskiya, ta karasa a hankali tace

‘A’a, Yusra me kikeyi kuma a nan zakije ki kona kanki?’

Tana karasawa ta kula da ledar da take hannun Yusra, ita kuma tana ganin hankalinta ya kai kan ledar tayi sauri ta fara kokarin boyewa.


Da sauri Aishan ta cafke hannunta ta dauki ledar tana budewa da mamaki tana fadin

‘Yusra! Me kuma kike saka min a miyar?’

Tayi tsuru-tsuru tana kallonta tas tana wani murguda mata baki tace

‘ba komai.’

Ta fara kokarin juyawa ta fita daga kicin din Aishan ta daka mata tsawa, take ta tsaya.


Ta kwance ledar ta duba sosai tana yi tana shanshanawa; idan dai ba kuskure tayi ba to sabulu ne sai dai an gurza shi kamar da abun gurza kubewa. Ta gyada kai; tabbas sabulu ake saka mata a abinci ‘yan kwanakin nan da abincinta yake baci. Ta dubi Yusra tace

‘Sabulu Yusra? Kike zuba min a miya saboda mugunta ko me?’

Ta sunkuyar da kai tana gunguni.

Aisha tayi murmushi tace

‘Hhhh! Ba ni kike cuta ba Yusra, ubanki kike cuta saboda dai sabulu ba abinci ba kuma tabbas zai iya illata lafiyar mutum musamman mutum mai shekaru kamar Abbanki. Ni ubana ya mutu na san menene maraici, ba abune mai dadi ba amma ke naki uban kike so ki dinga bawa sabulu saboda ki illata shi. Na san Mommy ce ta turoki, don haka idan kin je ki gaya mata nace tsohonki kike zubawa sabulun yana ci, idan kuwa ya mutu ku ya macewa ku da ita domin kune kaf danginku babu wanda ya kaishi kudi balle ku sa rai wani zai kula daku kamar yanda yake yi. Garin zalunci zaku cutar da kanku a banza.’

Ta kama hannunta ta saka mata ledar ta danke mata tace

‘Gashi nan idan kin je kice mata nace abinda tayi min Allah yayi mata kuma kema haka.’

Ta murguda baki ta ja tsaki sannan ta fizge hannunta ta fice daga gidan tana huci, Nana tana biye da ita.


UWAR SADDIKU


Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)


15

A fusace suka shiga gidan, Anti Rahma ce a zaune a falo da Baby a hannunta. Ta bisu da kallo bayan da suka nufi hawa sama tace

‘Ke Yusra meye zaku shigo gida babu sallama ko baki ga mutum a falon bane?’

Ta share kwalla tana zumbura baki, ba tare da ta juyo ba tace

‘Mommy nake nema.’

Suka karasa hayewa saman ba tare da sun ce mata komai ba.

Tana zaune a falon Abban tana kallon TV tana shan romon kaza, suna shiga suka zube a gabanta Yusra ta kifa kai a cinyarta ta fashe da kuka. Ta dafa kanta da mamaki ta dubi Nana tace

‘Meye haka kuma? Nana me aka yi mata?’

Ta zumbura baki sannan tace

‘Mommy Anti ce fa, ta zageta ta zagi Abba harda ke ma ta zaga kuma tace Yaya Yusran ta gaya miki.’

Da mamaki ta tambaya

‘Anti Rahma?’

‘Matar Abba mana.’

‘Aisha? Lallai matar nan rainin nata ya isa! Me tace miki?’

Yusra ta dago kanta, kafin tayi magana Nana tace

‘Tace zamu kashe ubanmu kuma kowa a danginmu ba masu kudi bane sai shi, harda cewa ita babanta ya mutu.’

Yusra ta bude tafin hannunta ta turawa Mommy ledar garin sabulun wadda dama ita ta bata ita, nan da nan ta dauke ta zura a bayanta. Yusra tace

‘Mommy garin na rufe tukunyar ne to dama non stick ce mai murfin glass shine murfin ya fadi ya fashe tazo tana ta maganganu.’

Ta mayar wa da Mommy duk maganganun da Aishan ta fada.

Suna cikin wannan maganar Anti Rahma ta hawo sama ta zauna a kan kujera tace

‘Me aka yiwa Yayan ne?’

Cikin fushi Mommy tace

‘Ita da matar ubanta ne, kawai saboda ta fasa murfin tukunya shine za a zageta a gaya mata maganganun banza har ana cewa ta zo ta gaya min saboda raini.’

Rahma ta taya su jimami da mamakin yanda murfin tukunyar zai sa ayi haka, tace

‘To ai murfin tukunyar bai fi karfin uban Yusra ba da za a zageta a kai kwanukan nan da kai da kanka ma kake fasawa shine harda zagi. Kai wasu matan dai sun kwashe kayansu daga gaban ma’aiki.’

Sukayi shiru na dan lokacin, jim kadan Mommy ta zabura ta mike ta tsallake su ta wuce daki, jimawa kadan ta fito da mayafi ta dubi su Yusra tace

‘Ku tashi muje, sai na ji uban da ya tsaya mata.’

Sadik ne ya shigo yana rike da hannun Ummi yana karasa shigowa yace

‘Mommy kowa yana cikin gida wannan yarinyar tana baya tana ta faman wasan kasa, kalli jikinta fa.’

Rahma ta sha gaban Mommy tana mika mata Sumayya tana fadin

‘Haba Yaya, ai bata isa kije ba saboda wannan maganar. Riketa muje sai na ji uzirinta, ai idan kika je raini sai ya shiga tsakani.’

Ta karbi Sumayya ranta a bace; bata so Rahma ta hanata ba don da sai ta tafi da yaran ta sa Sadik ya mammari Aishan.


Tunda Abbansu ya daina shan zobonta a kan kullum sai yace cikinsa yana bashi matsala ta shiga damuwa saboda ta san yana samun biyan bukatarsa a can. Don haka ta fito da wannan dabarar domin ta san idan ranshi ya baci wajen abincin dare to daren ba zai yi dadi ba. Da farko gishiri tayi tunanin a dinga karawa sai kuma taga ai idan gishiri ne da an ci za a gane ta fi son abinda idan ya ci zai zargi ko wani abun ne na asiri aka zuba masa; don haka ta sami sabulu.

Ta dubi Rahma tace

‘Da kin bari naje in ga idon mara kunya.’

‘Ai bata isa ba wallahi, wutsiyar rakumi ai tayi nesa da kasa.’

Mayafin Mommy din ta karba ta yafa ta dubi Yusra tace

‘Muje Yaya.’

Mommy ta dubi Sadik wanda Nana ta gama yiwa bayanin abinda ya faru tace

‘Ka bisu kaima saboda naga matar nan saitin ta yana gocewa.’

Rahma tace

‘Yayi zamansa ma na isheta.’

‘Gara dai ya biku, kuje Sadik.’

Haka Rahma ta wuce Yusra, Nana da Sadik suka bita a baya suka nufi gidan Aishan.
……..

Su Yusra suna fita Aisha ta zubar da miyar, ta gyara wajen. Har zata dora sabuwar miya sai kuma taji hankalinta bai kwanta da tuwon ba ma don haka sai ta sauke ta sheka masa ruwa tunda daman rude kawai tayi.


Ta fito daga kicin din ta zauna a falo da niyyar idan tayi sallar magriba ta dafa musu jollof kawai.

TV a kunne take amma bata gane me ake fada a TV din tunani kawai take tana mamakin me ta tsarewa Zahra.

Tana nan zaune aka buga kofa don haka ta tashi ta bude, batayi mamaki ba da ta gansu don ta san sai wani abun ya biyo baya.

Babu yabo babu fallasa Rahma tayi mata sallama don haka ta wuce ciki bayan ta cewa Rahman Bismillah. Suka karasa falo suka zauna, ita Yusra sai faman muzurai takeyi tana murgude baki shi kuwa Sadik ko zaman ma bai samu yayi ba, tsayawa yayi a kansu yana muzurai kamar wani soja. Ta bi su da kallo, har zata cewa Sadik din ya zauna sai kuma ta fasa don ba ita ta hanashi zaman ba. Bata son kallon da yake mata; tunda take a rayuwarta bata taba kallon idon mutum taga zallar kiyayya ba kamar yanda take gani a idon Sadiku.


Rahma ta katse mata tunanin tana gaisheta, babu izgilanci ko alamar fushi a maganar Rahman don haka itama ta dan saki jiki suka gaisa ba yabo ba fallasa.

Rahman tace

‘Yar taki ce tace ta fasa murfin tukunya kuma sai tazo da maganganu marasa dadi, shine nazo na ji wai me ya faru ne?’

Kamar ba zata yi magana ba, ta dan kauda kai tana murmushi sannan tace

‘Haba dai murfin tukunyar me? Abinda kaima a hannunka yana fashewa.’

Nan ta mayar mata da abinda ya faru da kuma sabulun da ta kama Yusran da shi, tace

‘Murfin tukunyar bai dameni ba kwata-kwata amma ace yarinya kamar Yusra ta san yanda zata bi ta cutar dani saboda ina auren babanta ai kinga dole na zata aikota aka yi.’

Mamaki ya cika Rahma, ta juya ta kalli Yusra. Yanda yarinyar tayi tsamo-tsamo ya tabbatar mata lallai ta aikata. Ta mayar da dubanta ga Aisha tace

‘Ikon Allah! To don Allah kiyi hakuri, wallahi abune na yarinta don na tabbatar babu yanda za ayi Mommy ta turota tayi wannan aika-aika. Kuma na tabbatar da taje bata gaya wa Mommy din abinda tayi ba, ta dai ce ta fasa miki murfin tukunya kinata fada. Zan yiwa Mommy din bayani in naje, yara ne sai hakuri in Sha Allah na san haka bazata sake faruwa ba.’

‘Hmmm! Babu komai ai ya wuce.’

Rahma ta mike tana fadin

‘Bari mu koma.’

Sukayi mata sallama suka fice.

Gaba daya yaran haushin Rahma suke ji saboda su zuwa sukayi ayiwa Aisha rashin mutunci amma ta zauna tana bada hakuri.
Koda suka koma wajen Mommy din haka Rahma ta zauna tayi mata bayanin abinda Yusran ta aikata; sai dai daga yanda Mommy din take bata amsa ta san bata gamsu ba. Domin daga karshe ma cewa Rahman tayi sharri ne Aishan takewa Yusra, itama bata san sharrin Aishan bane shi yasa ta kama zancen.


Haka ta taso jiki babu kwari ta sauko daga falon saman tana jiyo hayaniyarsu. Tabbas daga wannan dan bayani da suka mayar ta gamsu ko da ba Mommy ce ta sa Yusra wannan aika-aika ba to da saninta aka aikata; haka ta zauna tana mamakin yaushe Zahra ta zama haka, ta watsar da tarbiyyar yaranta saboda kishi.
………

Ko da ma su Rahma basu zo ba dama Aisha bata yi niyyar gayawa Abban Sadik abinda ya faru ba, ba ayi abun a gabansa ba kuma zuwa yanzu ta fahimci Zahra mace ce da ta iya juya zance don haka ta barwa ranta abun. Amma idan suka gaya masa wani abu to tabbas da shi da su bazasu ji dadinta ba.

Sai dai itama Mommy din ta gane idan ta kai masa wannan maganar abun zai zama kamar ta kai karar kanta ne, don haka itama sai tayi shiru. Suma yaran ta gargadesu kada su gayawa Abbansu kuma kada su gayawa Rukayya wadda lokacin da akayi abun tana daki tana hadda.
……….

Wajen fiye da sati biyu kenan rabon da ya sha zobo a wajen Mommy, musamman da daddare. Don haka yanzu normal yake harkarsa, duk yanda yake so yana samu a wajen Aisha tunda ita Zahra tana jego. Baya son ya zargeta da zuba masa abun da zai taba lafiyarsa amma dai yana so ya tabbatar ko don ya gane abunda ya haifar masa da wannan matsalar.


Tun kafin ya karaso unguwar ya yiwo mata waya yace ta ajiye masa shayi in ya zo zai sha kafin ya wuce tunda kwanan Aisha ne.

Da murna ta tashi da kanta ta shiga kicin don dama tunda ta haihu ko zobon zata hada masa bata bari Rahma tayi kuma ko ya sha ko bai sha ba da kanta take zubar da sauran ba tare da mutan gidan sun sani ba.


Nan da nan ta dafa shayin ta juye a flask ta hada da kofuna biyu ta kai dakinta tunda yanzu mafi yawancin lokuta idan ya dawo tana dakinta.

A dakin kuwa ya sameta, tun kafin ma yace ina shayin ta zuba masa. Ya zauna a kan dadduma ya jingina da gadonta yayinda ita kuma take kan gadon. Yana shan shayin suna hira; a zuciyarsa yana fatan abinda yake zargi kada ya tabbata. Yana ji a jikinsa cewa Zahra ba zata iya cutar dashi ba ko da kuwa don kishi ne.


Sai wajen tara da rabi sannan yayi mata sallama ya tafi; yana ta mamakin yanda yau din take ta walwala fiye da ‘yan kwanakin baya, tana ta faman kakalo hira har ya shanye shayin.

A wannan daren duk yanda yake bukatar Aisha kasa yin komai yayi, sai jagwalgwala ta kawai da yayi. Sosai ta firgita saboda da ta fara murna cewa matsalarsu ta kare, don haka saida ya dauki lokaci yana kwantar mata da hankali yana bata tabbacin ya riga ya sami magani don haka daga wannan daren ba za a sake samun irin wannan matsalar ba.


Haka suka kwana tana fatan Allah ya sa da gaske yake ya sami maganin yayinda shi kuma yake matsanancin mamaki na yanda za ayi ace Zahra tana zuba masa wani abu a shayin don ya kasa kusantar Aisha.

Wayewar garin ranar ya kama kwananta ne ita Zahran, har dare yayi ya shiga wajen nata. Yayi niyyar ya tunkareta da maganar abinda take zuba masa a zobo amma kuma har suka kwanta bacci yana wasi-wasi.


Duk saukin kanta da halayenta masu kyau da yake so amma fa bata taba karbar laifinta; haka zata saka shi a gaba suyi ta musu a kan lallai sai ya fahimci ba itace mai laifi ba sai dai idan wani ne mai laifin. Don irin wannan ma ya san ba zata taba yarda tace ta saka masa abu a zobo ba, idan taga dama ma haka zata sa kuka ta juya zancen a kan cewa shine zai zargeta tayi ta rigima har sai ya bata hakuri.

Haka har gari ya waye sai dai kawai kallonta da yake yana mamaki; sau biyu tana tambayarta me yasa yake kallonta shi kuma sai yace mata babu komai.


Haka ya kare wannan kwana biyun ba tare da yace mata komai ba.
Kuma duk cikin kwana biyun nan batayi zobo ko lemon tsamiya ba, shayi ma kuma da bai nema ba bata bashi ba. Sai na safe kawai wanda yace a daina saka komai a ciki a dinga bashi ruwa kawai zai hada shayinsa da kansa.


Ranar da zai koma kwanan Aisha ranar ne tayi zobo, lafiyayye sai kamshi ne yake tashi ga sanyi har gumi jug din yakeyi. Duk yanda yake son zobon nan haka ya hakura, har ta cika masa kofi ya dubeta yace

‘Kai ba zan sha zobon nan ba, bana jin dadin cikina sai dai ko wani lokacin.’

Suka cigaba da hirarsu a dining table, shi yana cin abinci ita kuma tana taya shi hira da yake lokacin wajen karfe biyar ne don haka ita ta riga taci abincinta na rana. Ya dubeta ya tura mata kofin zobon yace

‘To ai sai ki shanye wannan da kika zuba.’

Tayi ‘yar dariya tace

‘Ni kam na sha nawa, wannan ai naka ne. Sai dai idan baka sha ba na ajiye da daddare na sha.’

Ya cigaba da cin abincinsa; dama bai yi zaton zata sha ba tunda ta san ta saka wani abun a ciki don tabbas ya san da babu wani abun a ciki da tuni ta shanye zobon nan.

Ya kusa gama cin abincin Sadik ya shigo daga makaranta, ya riga ya shiga SS 2 don haka idan aka tashi daga makarantar yana tsayawa lesson sai biyar suke tashi. Bayan yayi musu sannu da gida ya dubi jug din zobon nan yana gumi yace

‘Abba in dauko kofi in sha zobonka, wallahi zafi nake ji yau an yi rana.’

‘Ai ba ma sai ka dauko kofi ba dauki wannan ka sha.’

Abban ya bashi amsa yana nuna wanda Mommy ta riga ta zuba masa a kofi.


Da sauri Sadik ya karaso da niyyar daukan kofin, kafin ya karasa ta balla masa harara tana kokarin buge masa hannu

‘Naka zobon ai yana kicin da abincinka ka shige ka dauka.’

‘Mommy wai na sha wannan din kafin na cire uniform.’

‘To ki barshi mana tunda ba sha zanyi ba.’

Abba ya fada yana kokarin daukar kofin ya mika masa, tayi wuf ta rigashi daukewa tana fadin

‘Allah ba zai sha ba sarkin rashin kunya, yaje ya sha nasa.’

Sadik ya jefa jakarsa kan kujerar falon ya shige kichin yana gunguni, ta mayar da kofin ta ajiye tana ta wani kumbura.

Sai da ya gama cin abincin tsaf ya dubeta yace

‘Zahra.’

‘Na’am.’

Ta amsa da alamun jikinta ya dan yi sanyi.

Ya kalleta suka hada ido, ta kau da nata idon saboda yanda yake kallonta kamar yana kokarin karanto wani abu a zuciyarta.

Yace

‘Ko dai akwai wani abu a zobo nan ne wanda ba Sadiku aka zubawa ba ni aka zubawa.’

Ta dan dirirce sai kuma tayi kokari ta waske

‘Ban gane ba? Kamar me kenan? Bayan ga irin zobon nan Sadiku ya debo daga kicin kuma ya sha.’

‘To me yasa ba zai sha wannan ba kema kuma ba zaki sha ba?’

Ta dan bata rai sannan tace

‘Gani nayi ai ba tarbiyya bace na zubawa ubansa abinci shi kuma ya dauka ya sha, a kofin ma da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login