Showing 81001 words to 84000 words out of 166068 words

Chapter 28 - UWAR SADIKU COMPLT BY SAKINA YAZID.txt

11 Jul 2024

25430

walima amma bai sami dama ba, sai ranar hudu ga watan Sallah shine ranar da aka ware domin yin wannan walimar ta taya shi murna a hotel din Bristol dake Kano.

An gayyaci Abba wannan taro kuma ya gama shiri shi da Aisha zasu je, hakan nema dalilin da yasa ya ce wa Mommy ba zai je daukota ba don yana so ya biya ta gidan Hajiya ya kai Aishan tayi mata gaisuwar Sallah sannan kuma su biya gidan Yaya Bello inda daga can idan sukayi Sallar Magriba sai su wuce wajen taron.

Bata taba shiga cikin abokansa da matansu ba, don a abokansa ma bai fi mutum biyu ba wadanda ta sani; duk sai sunayensu da take ji. Da farkon aurenta ya kai ta gidan mutum biyu sai dai tun a lokacin ta fahimci matansu duka kawayen Zahra ne don haka ta ja jikinta.

Sai da tayi alwala sannan ta tsantsara kwalliyarta cikin farar atamfa mai ratsin shudi, ta kawo luffaya mai kalar shudi wadda ta sha ado da fulawowi farare da duwatsu masu kyalli ta nade jikinta da ita.


Kunshin sallarta yana nan radau don haka ya kara fito da yatsunta da ta sakawa zobe me ruwan tasa sannan ta daura agogonta Fendi. Ta kawo takalminta mai matsakaicin tudu wanda ake kira wedge ta saka da jakarta Yar karama wadda ta dace da shigar. Goge fuskarta kawai tayi sannan ta dora jan janbakinta wanda yake karawa labbanta kyau, ta fito falo ta sameshi inda yake zaune sanye da farar shadda dinkin doguwar riga da wando da jar dara kamar yanda ya saba.

‘Na gama.’

Ta fada tana daga tsaye a bayan kujera, ya juyo ya dubeta ya mike yana murmushi yana fadin

‘Wannan kwalliyar ai sai ki sa a zata ni aka yiwa minister din.’

Tayi murmushin da ya kara mata kyau, ta sunkuyar da kai tana fadin

‘Allah Amin.’

Ya dubi agogon bangon dake falon yaga karfe biyar harda rabi, yazagayo yana fadin
‘Mu tafi.’

Motarsa tana bakin gate don haka har nan suka fita.

Dai-dai lokacin da suka fito daga gate din suna hirarraki a lokacin Yusra ta fito daga gidan commissioner tare da yarinyar gidan Rafi’a wadda kawarta ce. Tar ta hangosu ta kawar da kai; a ranta tace dama shi yasa ya cewa Mommy zai fita ba zai je daukanta a airport ba. Tabbasa tana dawowa sai ta gaya mata.

Suka shiga mota ya ja suka bar unguwar.

Ko minti talatin basuyi da tafiya ba Malam Ali ya dawo da Mommy.

Nan da nan gida ya rude yara suka hau sowa da tsalle ana ta oyoyo. A falon kasa ta zauna duk yaran da Jummai da Rahama suka gaisheta suna mata maraba; tuni Sumayya ta makale mata. Tana nan zaune a falon ta bawa Yusra da Rukayya mukullin dakinta ta bude ta share ta canza zanin gado sannan suka haye saman ita da yara.
Bata jima da zama ba akayi kiran sallar Magriba, ta lallaba Sumayya ta zauna a wajen Yusra taje ta yiwo alwala.


Tana fitowa daga alwala tace yaran duka suje suyi Sallah sai su zo ta basu dabino da bagaruwa wadanda ta zubo a jakar hannunta.


Nan da nan duka yaran suka ruga da gudu suka fice daga dakin, Yusra ce kawai tayi saura tana zaune a gefen gadon Mommy. Kafin Mommy tayi magana tace

‘Mommy wai Abba ya gaya miki inda suka tafi shi da matarsa?’

Da mamaki ta dubeta

‘Aisha? Ce min kawai yayi zai fita, ina yace miki sun tafi?’

'Nima bai gaya min ba, kawai dai naga lokacin da suka fita dab da ki dawo. Kinga kuwa yanda taci gayu kamar wata matar gonna, ina jin ma dai dinner zasu je fa.’

Cikin tsananin bacin rai tace

‘Um.’

Sukayi shiru na dan lokaci, daga baya Mommy ta dubi Yusran tace

‘kije kiyi Sallah.

Ta fice ta barta tana kaiwa da kawowa a dakin.

Wai yaushe Yusuf ya zama munafiki ne? Ba zai ma gaya mata zai fita da Aisha ba sai yace mata kawai zai fita? Har yanzu bata daina mamakin yanda akayi ya koma wajen Aisha ba.

Tana nan tsaye ba tare da tayi sallar ba yara suka shigo da murnarsu sunyi tasu sallar a basu dabino da bagaruwa.


Ta bude jakarta ta bawa kowa nashi sannan ta basu wani a leda tace su kaiwa Rahma daga nan sai su zauna a can tayi sallah.

Suna fita ta bude wardrobe ta lalubi wayarta wadda ta bari a gida, ta kunna wayar sannan ta sayi data. Ta kunna data din sannan ta ajiye wayar a kan gadon ta tayar da Sallah, ta san kafin ta idar da sallah sakonninta sun gama shigowa.

Tana idar da sallar ta mika hannu ta dauko wayar tana daga zaune a kan daddumar, nan da nan ta bude wayar ta fara duba sakonninta.

Sakon Hajiya Sharifa ne a sama wanda da alama ma yanzu yake shigowa; Sharifa matar abokin Abba ce wato Alhaji Jibrin Muhammad Minjibir; suna aminci sosai da Mommy, don ko da zata tafi Umra ma musamman tayi mata waya sukayi sallama.
Tana ganin sakon Sharifa tayi murmushi; yanzu haka har ta sami labarin dawowarta shine take mata maraba. Ba tare da bata lokaci ba ta danna sakon ya bude:

“Hajiyata ya ibada? Na san dai yanzu kun hado kaya ko ma kuna hanya.”

“Kina jin dadin kasa mai tsarki kin bar maigidan a hannun yara.”

“Ai gamu nan muna kallon soyayya shi da kanwarki, naga ta goge fes da ita.”

Sai hoto ya biyo baya, yana budewa taci karo da hoton Aisha da Abban Sadiku. Bata san me ya basu dariya ba don dariya suke a hoton sosai, ta kalli laffayan dake jikin Aishan; wato da yake bata nan shine ya sayowa Aishan wannan dandatsetsen laffayan. Ita kuwa ko da tayi maganar kayan Sallah cewa yayi banda ita tunda an kwashe kudi an biya mata Umra, idan taje ta saya a guzurinta.


Wai yaushe ma Abban ya rainata haka? Tayi kwafa.

Ta sake karanta sakonnin sannan ta bada amsa kamar haka

“Bikin wa akeyi ne haka?”

Shiru babu amsa ga dukkan alamu Hajiya Sharifa ta sauka daga online don haka ta fita daga sakonnin Sharifan.

Nan da nan ta lalubi lambar Yaron Malam don dama shine abinda take nema, ta budo ta fara yi mishi sako na murya wato voice note:
“Yaron Malam duk wani aiki ya rushe wallahi, don yanzu haka maganar da nake maka ya san zan dawo amma ya dauketa suka fice. Sati biyu kawai nayi da ‘yan kwanaki amma duk wani aiki da kayi min sun lalata shi wallahi. Gaskiya na gaji da zama da yarinyar nan yaron Malam, ban taba tunanin akwai matar da zata iya kasa min hankalin miji kamar yanda yarinyar nan takeyi ba. Ya kamata dai a tumbuketa daga rayuwarmu ni da mijina Malam.”

Kamar daman jira yake tayi magana nan take taga alamar yana kokarin turo da amsa, don haka ta dan saurara kadan. Nan da nan sakonshi ya shigo shima ta voice note kamar yanda ta tura masa:

“Hajiya ai na gaya miki yarinyar nan hatsabibiya ce, kuma wasu lokutan bata tabuwa don haka kinga dole sai mun bi lamarinta a hankali. Idan kika sami lokaci ki shigo sai kiji cikakken bayanin yanda za ayi. Amma nayi miki alkawarin ko ta karya komai kwarjinin da na baki in dai kin masa amfani da shi yana nan don ba zata iya karya wannan ba sai dai idan shi da kansa ne zai karya. Ki kwantar da hankalinki. Sai kin shigo din.”

Ta dan sami natsuwa bayan ta saurari wannan sakon don ta san ko da akwai wani dalilin da zai sa Abban yace zai mata wata tijara to ba zai iya ba saboda kwarjinin yana aiki.

A nan ta kirawo Amina ta sanar da ita dawowarta da kumma halin da ake ciki sannan daga baya ta kirawo su Yaya Murja da sauran dangi ta sanar da su dawowarta.
……….

Sai wajen goman na dare saura sannan Abban ya shiga gidan, tana jiyoshi ta tashi daga falon saman ta shige dakinta ta turo kofar. Bata dade da mike kafa a kan gadon ba ya tura mata kofa ya shiga da sallama; yana dauke da Sumayya yayinda Ummi take biye da shi tana surutu.

Ya karasa ya zauna a kan gadon, ya dubeta yana murmushi

‘Hajjaju mutan maka. Kun dawo lafiya ko?’

Tayi murmushi tace

‘Lafiya kalau, mun sameku lafiya?’

‘Alhamdulillah duk gamu nan lafiya kalau. Ummi tace an bawa kowa dabino da chocolate nima a bani nawa '.

Tayi dariya tace

‘Au harda kai ma.’

Suka dan taba hira kadan, tayi kamar bata san daga gidan Aisha yake ba. Daga karshe tace

‘Ga abinci can a dining table an dora, naga dare yanayi baka ci abinci ba.’

Yayi dariya yace

‘Haba Hajiya, daga dawowa sai ki sa mana baki a harkar gida ke da zaki huta. Ai Rahaman ta san ba a nan zan ci abinci ba, don na ma riga na ci abincin dare na.’

‘Um! Dama ni nace ta ajiye maka.’

‘To nagode amma na koshi.’

Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan yace

‘Bari naje, ina gidan kanwarki a can zan kwana in ya so gobe sai a fara rabon kwanan daga nan kafin nan kin dan rage baccin gajiya ko?’

Ya mike ya jefa Sumayya dake kan cinyarsa sama ya cafeta ta kyalkyale da dariya, shima ya sa dariyar yana fadin

‘Sarkin tsalle-tsalle, muje na mayar dake inda na daukoki Mommy ta huta ko kafin gobe a kara mana dabino da chocolate.’

Ya dubeta yace

‘Sai da safe ko? Allah ya huta gajiya.’

A can kasan makoshinta ta amsa

‘Amin.’

Ba tare da ya kalli fuskarta ba ya fice daga dakin ya ja mata kofa, yana saukowa kasa ya ajiye Sumayya ya cewa Sadiku wanda yake zaune a falon ya tashi ya fita ya koma dakinsa Rahma ta rufe cikin gidan.

Duk gajiyar da ta kwaso bata samu tayi baccin kirki ba saboda yanda take takaicin kasancewar Abban a wajen Aisha; kusan sati uku basu ga juna ba amma shi ko dokin ganinta baya yi, ya tafi wajen amaryarsa saboda ya nuna mata bata isa ba.
------

Ko da gari ya waye ranar asabar ce babu aiki don haka sai wajen karfe goma suka tashi daga bacci. Nan da nan ta hada musu abincin safe suka ci suka shirya.


Wajen sha daya da rabi yace mata zai je gidan Zahra, take ta dauki mayafin abayar da take jikinta tana fadin

‘Bari na zo muje sai nayiwa Mommy sannu da zuwa na dawo kada tsaraba ta kare gara na karbo tawa da wuri.’

Yayi dariya yace

‘Ko kuma na karbe taki da tawa ba.’
Suka fice suna dariya.

Babu yabo babu fallasa ta tarbesu don har ruwa da lemo ta sa aka kawowa Aishan; sai dai hakan bai hana Aishan ta gane yanda Zahra take kare mata kallo ba kamar mayunwacin karen da ya ga abinci. Suka gaisa tayi mata Allah ya sanya alkhairi, jimawa kadan tayi musu sallama; Mommy ta mike da kanta ta debo mata dabino da bagaruwa ta bata sukayi sallama ta tafi ta bar Abban a nan.

Kafin Abban ya shigo sunyi waya da Amina ta gaya mata idan Abban ya shigo kada ta wani tada hankali, ta gaya mata ta lallaba shi domin akwai wani malami ta da zata kaita wajenshi domin shi aikinsa kamar yankan wuka ne. Idan suka je sai yanda taga dama zata yi da Abban don haka ta bata shawara kada ta daga masa hankali; ta huta na sati daya in ya so sai ta zo suje. Kawai dai ta sanar da ita ta tanadi kudi domin su hada aikin biyu; da na yaron Malam da na wannan sabon Malamin domin ayita ta kare kawai a gama labarin Aisha.

Don haka duk wata fitna da ta tanada zata yi bata yi ba, musamman da ta ga alamar har yanzu yana shakkarta kamar yanda ta tafi ta barshi.
_

Tunda ta dawo take tunanin inda zata sami kudi, amma duk wata dabara ta kare mata. Business din ma ya dan durkushe tunda harda kudaden business din ta hada ta tafi Saudiyya da niyyar zata saro abaya; sai dai bata saro abayar ba kuma ta kashe kudin.

Tana dan samun a wajen Abban amma da dabara take yaga da dubu ashirin da goma, zata dauki lokaci bata tara yawan abinda take so ba. Gashi ita ba ma’aikaciya ba balle ta tara albashinta. Tayi tunanin ko zata sayar da babban saitin gwal dinta amma gaskiya bata jin zata iya saboda tana sonshi kuma idan ta siyar shine kadararta ta karshe; don haka wannan ma ba zai yiwu ba. Ta san Suwaiba zata iya bata kudin rance to amma idan ta bata sai ta gayawa Yaya Murja, don haka ta hakura.


Kusan kwananta biyar da dawowa kafin dabara ta fado mata.

Bayan yayi mata sallama ya tafi wajen Aisha tunda a can zai kwana; Saida ta tabbatar kowa yayi bacci a gidan sannan ta shiga dakin Abban ta turo kofa. Ta riga ta san inda yake duk wata ajiya, duk wata takarda da yake ajiye da ita ta san inda take.

Wani karamin bakin akwati ta dauko daga wardrobe din can saman, ta koma kan gado ta zauna. Akwatin yana da password amma ta dade da sanin password din ba tare da Abban ya sani ba.

Nan da nan ta bude akwatin ta fara duba envelope din ciki tana neman takardar, sai da ta bude kusan guda biyar sannan ta sami takardun da take nema.


Tayi murmushi ta zare takardun daga cikin envelope din ta ajiye a kan gadon da take zaune. Ta mayar da akwatin ta rufe ta tashi ta taka wardrobe din ta mayar da akwatin.

Ta kwashi takardun ta fice ta nufi dakinta cikin tsananin farin ciki.

Tana shiga dakinta ta zauna a gefen gado tana duba takardun tana yiwa kanta murmushi; takardun fili ne wanda Abban ya saya da sunan Saddiku. Ya sanar da ita lokacin da ya saya kuma ya gaya mata filin ba kato bane amma dai ya sayawa Sadikun ne saboda nan gaba. Sun gama magana da Amina an samo mata wanda zasu sayi filin a kan kudi sama da miliyan hudu, a hakan ma sunce don ba a kewaye filin bane. Ta gama lissafin idan ta siyar ta biya malamanta suka yi mata aiki canjin sai ta zuba abusiness dinta da ya durkushe.

Ta yiwa kanta dariya ta tashi ta adana takardun nan a kasan katifar dakinta, sannan ta koma ta kwanta.
__
Tunda ta dawo daga Saudiya Saddiku ya hanata motarta, shi yake hawa motar nan kullum musamman da yake baya wani karatu yana zaman jiran sake jarrabawa; sai dai kawai ya zo ya tambayeta kudin mai ko kuma idan ya ballo gyara ya zo ta bashi kudin.

Dole ta hakura da motar Malam Ali Direba da da ta kwace tunda tatan Sadiku ya hana; sai dai shi Sadikun ya kaita duk inda zata ko Malam Ali ya kaita.

Duk lokacin da Abban yayi magana sai tace wai duk abokan Sadikun wadanda ma iyayensu basu kai Abban kudi ba an basu mota amma shi ya hana Sadiku; idan kuma ya bi abokan yace zai bi ‘yan shaye-shaye. Don haka ya hakura ya sa musu ido.
--------

Abokinsu ne Tijjani Tukur wanda suke kira TT yake birthday, don haka ya shirya party a gidansu da yake unguwar Lodge Road; da yake iyayensa ba sa gari.

Sai wajen karfe tara na dare aka fara fatin, suka hadu maza da mata sukayi ta sakarci, wadanda suke shaye-shaye a cikinsu ranar kowa kyauta TT ya basu kwaya irin wadda suke so.

Saddiku ya san Abbansa yana gari don haka yake ta kokarin dawowa gida da wuri, shi da abokinsa Munir wanda dama a wajen Saddikun zai kwana. Sai wajen goma da rabi na dare suka samu suka fito daga wajen kuma duk su biyun a buge suke.

Take Sadiku ya fada kujerar direba ya fizgi motar da gudu; babu mutane sosai don haka suka sami sararin gudun.

Mutum suka hango a tsaye a gefen titi yana haska karamar tochila, Munir ya dubi Saddiku yace

‘Ga mutanenka can 'yan KAROTA har an fara tsayar da mu.’

Ya kyalkyale da dariya yace

‘Kuma ba zan tsayaba ba, bari ka ga tsiyar da zan masa dan iska kawai.’

Ya kara taka motar yayi kan mutumin wanda ya zura da gudu, sunata dariya shi da Munir din yayinda yayi wuf ya fara kokarin mayar da motar kan titi. Babu wanda ya san yanda akayi sai gani akayi motar ta kwace ta daki fitilar titi ta dawo tsakiyar titi tayi tsalle sannan ta kife. Gilasan motar suka tawarwatse sannan injin ya mutu.

Tsirarun mutanen da suke wajen suka karaso da hanzari harda mutumin da suka kusa kwashewa; nan da nan aka fara kokarin zaro su.


Ihun Munir kawai ake ji domin shi Sadiku tuni ya sume, sai jini da yake fita daga wasu bangarori na jikinsu.

Kafin wani lokaci Jamai’an road safety sun bayyana, don haka aka kwashesu sai asibitin Murtala.

Ba a sami wayar Munir ba amma jami’an road safety din sun sami waya guda daya wadda ta Saddiku ce. Sai da aka shigar da yaran dakin bada taimakon gaggawa wato Accident and Emergency na asibitin Murtala sannan jami’in da wayar ke hannunsa ya samu ya bude wayar. Duba jerin sunayen dake cikin jerin lambobi yake har yazo kan lambar da aka saka Daddy; ba tare da bata lokaci ba ya danna mata kira.
…………

A kwance yake a falo Aisha tana yi masa tausa, wayarsa da take chaji a gefe tayi kara. Ta mike ta dauko wayar tana fadin

‘Waye wannan da tsakar dare?’

Tana kallon wayar tace

‘Kaga kuwa Saddiku ne.’
Cikin hanzari ta mika masa wayar ya karba, tana dab da tsinkewa ya amsa yana mamakin abinda yasa Sadiku zai kirawoshi a wannan daren; don ko haka kawai ma basu fiya waya da Saddiku ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login