Showing 93001 words to 96000 words out of 166068 words
koma dakin sai dai zuciyarsu fari tas saboda wunin ranar yayi musu dadi.
Washegari Aisha tana bude Whatsapp taci karo da sakon Zahida na murya wato voice note, nan da nan ta bude tana saurara:
‘Wai mutum yana Dubai amma ba zai tura mana hotuna ba, to wallahi ni ko kasuwar garinmu naje sai na ishi duniya da hoto balle na hau jirgi na keta hazo. Ko da yake ma Yusuf din zan tambaya nake bata lokaci.’
Saida ta gama dariya sannan ta zabi hotunansu wajen kala goma ta tura mata. Ta cigaba da dube-dubenta a waya.
_
Duk da bacin ran da take ciki na tafiyar da yayi da Aisha Dubai bata fasa shirin tarbarsa ba kamar yanda ta saba; maganar Dubai ma ta riga ta bawa zuciyarta hakuri. Kawai dai ta yiwa kanta alkawarin ko da tsiya ko da tsiya-tsiya idan zai kuma fita kasar nan ko ina ne sai ya je da ita.
Hajja ta kawo mata kayan mata wadanda cikinsu harda na mallaka, duk ta fara amfani ma da su. Sai dai jiya da suka yi waya da Amina ta sanar da ita akwai wasu kaya da aka kawo mata daga Nijar, idan ta tashi daga office zata kawo mata su lallai ta gwada don ta bata tabbacin sai sun sa mata mutum sambatu.
Wadannan kayan kawai take jira tunda jibi zasu dawo.
……….
Ma’aikatar kudi ta jiha ne inda Amina take aiki. Su biyu ne a office dinta ita da abokiyar aikinta sai dai kowacce da teburinta. Daga gefe guda kuma akwai kafet karami wanda nan ne suke Sallah ko kuma su dan mike idan suna hutawa.
Yau ma a nan suke zaune, ita Amina tana rubuce-rubucenta yayinda Hadiza ke ta faman kalle-kalle a waya.
Sunayi suna hira jefi-jefi.
Hadiza ce ta budo wani status a wayarta tana kalla tana murmushi, can kuma a fili tace
‘To Amin, muma Allah ya kaimu wannan sharholiya.’
Amina tace
‘Keda wa?’
Ta dan matso tana nuna mata abinda ta gani a wayarta; mata da mije ne a kan doki yana rungume da matar suna ta dariya, ita kuma matar tana rike da kofi me straw tana zukar wani abu daga ciki. Yana wucewa wani ya fado suna tsaye ya rungumeta nan ma dariyar suke, shi yana sanye da kananan kaya ita kuma tana sanye da abaya. Bayan ya wuce wani ya fado yana kwance a kan yashin ita kuma ta tada Kai da bayansa tana ta dube-dube a wayarta. A kasan hoton karshe an rubuta “sharholiya made in Dubai. Allah ya maimaita mana.”
Wani status din ya fara budowa Aminan tace
‘don Allah mayar dashi na kara gani; matar kika sani ko mijin?’
Tayi ‘yar dariya
‘Wallahi babu ko daya. Ina jin a group ma fa muka hadu da matar nan kuma fa ban san ko itace a hoton ba ko ‘yaruwarta ce don bamu taba haduwa ba sai dai a group. Kawai dai sun burgeni.’
‘Sunanta Aisha ko?’
‘Gaskiya a’a, sunanta Zahida M. K don haka take sawa a WhatsApp name dinta.’
‘To wannan ta hoton dai sunanta Aisha kuma kishiyar kawata ce don hotunan nan ma hada baki sukayi da mijin ya tafi da ita suka bar Uwar gidan a nan tana fama da yara.’
Ta zaro ido
‘Ke Amina?’
‘Wallahi kuwa, wannan tafiyar ta munafunci ce. Uwargidansa ya rainawa hankali don maganar da nake miki ma suna can sai jibi yace mata zasu dawo.’
‘Kai kawata maza ‘yan bura uba ne! Wato Uwargida jakar gida an barta a gida an tafi da amarya Dubai sharholiya. Kai Allah ya shiga tsakaninmu da irin wadannan kishiyoyin, ki gama wahala da miji a zo a nuna miki iyawa.’
A nan ta saka Hadizan ta tura mata hotunan wayarta tunda dama idan ta tashi daga office din gidan Uwar Sadikun zataje.
Tunda taga hotunan nan ta kasa zama a office din, sosai ranta ya baci don tana taya Amina jin zafin wannan tafiyar da aka yi babu ita. Taci sa'a ana yin sallar azahar ogansu ya fice daga office din don haka itama ta fice ta nufi gidan Zahra.
A falo ta sameta tana hutawa yayinda Jummai take aikace-aikacenta da goyon Sumayya. Kafin su gaisa ta jata falon sama, bayan sun zauna ta ajiye mata ruwan sanyi da lemo. Suna gama gaisawa Zahra tace
‘Wai ya na ganki kamar a fusace ne, ina dai fatan kin taho min da tsumin?’
‘Na taho miki da shi. Wani abun takaici na gani wallahi. Ni wai ba cewa kikayi kwana biyu Abban Sadik zai yi a Dubai bane?’
Ta tabe baki ta kawar da kai
‘Haka yace. Amma ai daga baya na gaya miki ya tafi da amaryarsa wai wani idan ya dawo naji bayani, don haka yanzu kwana bakwai zasuyi shine sai jibi zasu dawo. Ai duk wannan shirin da nake yi sai ya ji daga gareni don wallahi ina binsa bashin zuwa Dubai.’
‘Hmmmn! Sai ma kinga abinda na gani sannan zaki tabbatar kina binsa bashi. Yana can suna ta sharholiya shi da kanwarki baki gani ba kamar wasu saurayi da budurwa.’
Ta budo wayarta ta nuna mata hotunan da Hadiza ta tura mata; tana kalla tana jijjiga kai zuciyarta tana zafi saboda takaici.
‘Ni zai rainawa hankali! Sai yanzu ma na gane babu wani business da yaje yi wallahi kawai hutawa ya dauki amaryarsa ya tafi ya barni a nan da yaransa. Tunda mutumin nan ya tsara tafiya Hajjin da matar nan na san ya shirya raina min hankali wallahi. Kawai daga kara aure mutum ya zama wani karamin munafiki, komai zai yi sai boye-boye? Kin san ko Hajjin ma ban san yana shirin tafiya ba sai da ya zama saura sati daya su tafi ya sanar da ni.’
Ta dafa cinyarta
‘Kada ki damu kawata na karshe sukeyi, wannan hotunan ma gani nayi kamar kin yarda da zancensa shi yasa nace sai na nuna miki. Amma kada ki wani damu da sun dawo za ayi maganinsu.’
‘Hmmmn!’
Nan suka cigaba da hirarrakinsu, daga baya ta bata tsumin da ta kawo mata sukayi sallama ta tafi ta barta tana takaicin hotunan.
Hotonsu a kan dokin nan yayi matukar tsaya mata a rai don ita bata ma taba sanin Abban ya iya hawa doki ba.
__
Jirgin safe suka biyo don haka wajen sha daya na safe suka sauka a gida Nigeria. Malam Ali yana jiransu a airport don haka nan da nan suka gama clearance suka dauki kayansu gaba daya aka zuba a mota suka kamo hanyar gida.
Suna shiga unguwar Abba yace ya kai su gidan Aisha don haka can ya kaisu suka sauka ya sauke musu kayan gaba daya. Duk da gidan ya dan yi kura amma haka Abban ya tayata suka karkade dakinsa yayi wanka ya canza kaya sannan ya fito ya nufi wajen Mommy.
……….
Tunda Malam Ali ya shiga dasu gidan Aisha yara suka kai mata labarin Abba ya dawo yana gidan Anti; bata yi zaton haka ba don ta zata a gidanta zai sauke jakar tsarabarsa amma duk da haka sai ta daure. Ta tare yaran gaba daya ta hanasu fita don so take tayi kamar bata san ya dawo ba.
Sai dai kafin ya gama wanka ya zo ranta har ya gama baci; kenan wani abun ya tsaya yi a wajen Aisha.
Tana zaune a falon sama tana ta faman cika tana batsewa ta jiyo yara suna ta murnanr dawowarsa bayan da ya shigo gidan. Sai da ya gama hirarsa da yara ya rarraba musu chocolate din da ya riko sannan ya hau saman ya sameta.
Da kyar ta daure ta amsa sallamarsa; ya fahimci damuwarta saboda dama tun lokacin da yace mata ga su a Dubai shi da Aisha ta daina kiransa a waya sai dai shi ya kirawo, Kuma da ya kirawo sai ta hadashi da yaran. Don haka ya shiryawa duk wata rigimarta.
Bayan sun gaisa ya tambayeta gida da yara ta tashi ta dauko kunun aya ta ajiye ta cika masa kofi, ta koma ta zauna a inda ta tashi kusa da shi. Sai da ya kwankwade kunun ayan ya ajiye kofin sannan ya dubi fuskarta.
Sai cika take tana batsewa tana ta faman harare-harare. Ya mike tsaye yana magana cikin halin ko in kula
‘To ni bari na koma dama akwai inda za mu dan……….’
A fusace ta mike tana harare-harare
‘Ban gane ka koma ba, ina kenan kuma? Shikenan mu…'
Ya kama hannunta wanda ya sha kunshi yayinda ta kara shan kuna, yayi taku daya ya matso gabanta sosai yace
‘To ai na ga kamar baki ji dadin dawowata bane shi yasa da zan dan koma na baki waje ko.’
Ta murgude bake zatayi magana, kafin ta bude baki ya sumbaci lebenta yayi dariya
‘Allah ya nuna min ranar da za a daina murgude min bakin nan na rashin kunya.’
Ta zumburo baki, ya sa hannu ya kara janyota jikinsa. Duk wata tsiwa da ta haddace zatayi ya goge mata haddarta, haushinsa take ji amma ta kasa ture shi. Yace
‘Na san dai kinyi kewata da yawa, to ba gani na dawo ba kuma shikenan sai a tare ni da murguda baki sai kace wani wanda bashi da galihu. Ai dole na koma tunda dama jakata a kulle take idan kika shirya sai na dawo.’
Shiru kawai tayi ta kwanta a kirjinsa ya rungumeta yana shafa bayanta. Tayi kewarsa kamar yanda shima yayi kewarta. Suna nan a tsaye suka ji motsin hawowa saman wanda kana ji ka san Ummi ne da Sumayya. Tayi gyaran murya ta dan ja baya don ta tabbatar shi ba sakinta zaiyi ba, tace
‘Yara fa suna nan.’
Ya ja baya ya koma ya zauna.
Nan ya zauna suka cigaba da hirarrakinsu shi da ita da Yara.
Jimawa kadan ya mike zai shiga daki, yace
‘Ayi abinci da ni fa a nan zan kwana.’
Ya shige dakin bayan ta amsa; yana so yace tayi abinci da Aisha amma yana tsoron fitna, don ya kula duk lokacin da yayi mata maganar Aisha to da fada suke rabuwa don haka ya hakura.
…………
Bayan sallar la’asar ne suna zaune gaba dayansu a falon a kasa ana ta hira, ya duba agogo lokacin karfe biyar da kwata. Ya san dai zuwa yanzu Aisha ta dan huta don haka ya dubi Mommy yace
‘Bari muje da yara mu yiwa Anti sannu da zuwa, yanzu zamu dawo.’
Ya dauki Sumayya ya tasa yaran gaba daya har Saddiku suka nufi gidan Aisha; domin ya san idan ba haka yayi ba bazasu je ba, shi kuma baya jin dadin wannan zaman da sukeyi kamar suna gaba da juna.
A zaune take a falo tana hutawa lokacin da suka shiga; cikin fara’a dalwala ta karbesu.
Bayan ta amsa gaisuwar kowa taki amsa gaisuwar Rukayya don haka bayan kowa ya gama magana Rukayyan ta sake cewa
‘Anti sannu da zuwa.’
Ta harareta tace
‘Bazan amsa ba Rukayya, sai yanzu kika zo inata nemanki.’
‘La Anti wallahi aiki nakewa Mommy shi yasa.’
Ummi tayi caraf tace
‘Abba kaga Anti tayi fushi da Yaya Rukayya.’
‘Shikenan sai muyi ta dariya.’
Aisha tace tana rungumo kafadar Rukayyan
‘To mun shirya, dama ba fada bane.’
Sukayi dariya gaba daya. Saddiku ne kawai bai saka musu baki a hirarsu ba yana zaune da hannusa wanda bai gama warkewa ba a rungume yana ta muzurai.
Ta tashi ta shiga daki, jimawa kadan ta fito da kaya ta ajiye ta koma ta sake dauko wasu ta fito ta ajiye sannan ta zauna. Ta janyo hannun Sumayya wadda take kan cinyar Abbanta, ta noke alamar ba zata zo ba. Ta dauko ‘yar tsana daga leda ta mika mata sannan ta mika mata alawa a 'yar karamar roba. Ta mika mata hannu tace
‘To zo mu shirya.’
Ta sake nokewa, tayi dariya tace
‘Sumayya kiwa.’
Ta bawa Saddiku takalmi sau ciki, Yusra da Nana da Ummi kuma kowa ta bashi abaya da agogo.
Akwai keken dinki mai aiki da wutar NEPA dan matsakaici na dorawa a kan tebur, ta janyo kwalin ta mikawa Rukayya tace
‘Chief fashion designer, ga keke.’
Nan take tasa ihu, ta sunkuci kwalin ta mikawa Abba cikin murna tace
‘Abba ka ga.’
Kafin ya amsa ta juyo tace
‘Anti nagode, kayan sallarki zan fara dinkawa.’
Tana dariya tace
‘Umm! Wannan dai mayi magana daga baya idan kin dinka na ‘yar tsana dai mayi magana.’
Duk gaba dayansu sukayi mata godiya, har sun mike ta mikawa Rukayya Leda tace kin manta da taki abayar. Abba ya karbar mata duka yaran suka wuce suka barshi a nan yana dauke da Sumayya. Ya dubeta yace
‘Wannan ai ke baki sayowa kanki komai ba yara kika siyowa, na zata ma kanki kika siyowa keken dinki.’
Tayi dariya
‘Ai ni bana son dinki itace take so, tunda suka je gidan Zahida da sallah ta gano kekuna kuma Zahida tayi mata alkawarin zata koya mata dinki shikenan ta kasa nutsuwa kullum dinki.’
Yayi mata sallama ya bi yaran a baya.
Yana shiga gidan ya tarar da su a falo sun baje gaban Mommy.
Rukayya sai murna take ta kasa zama guri daya saboda keken nan wanda ta riga ta fitar da shi daga kwalinsa.
Ya ajiye Sumayya ya wuce sama, ya shiga dakinsa ya kwanta don ya huta.
Da sallama ta shiga dakin, bayan ya amsa sallamarta ta zauna a gefen gadon wajen kafarsa. Ya gyara kwanciyarsa yana kallonta alamar ita yake sauraro saboda ya san wannan zaman da magana.
‘Mun ga tsaraba yara suna ta godiya.’
‘To ma sha Allah.’
Ta sake hade fuska sannan tace
‘Kuma wannan keken da aka siyo guda daya ina na Yusra? Tunda ka san itace dai Babba. Idan dai ba hada fada ba da so a raba min yara ai biyu ya kamata a siyo. Kuma abayar ma ita Yusra sai aka siyo mata iri daya da Nana ita kuma Rukayya tata ta fi kyau gashi harda wata jaka da turare bayan agogon. Idan ba hadin fada ba ai jaka ma da turare Yusra ya kamata a bawa itace 'yan mata tunda ko a makaranta yanzu SS 3 take yayinda Rukayyan take JS 3. Irin wadannan abubuwan ai su suke raban kan ‘yan uwa, duk abinda za a yi ko dai ayi musu tare ko kuma a fara yiwa Yusran tunda itace babba.’
Tunda ta fara maganar yake binta da kallo yana mamaki, ya tashi zaune yana binta da kallo yana murmushin takaici yayinda ita kuma take kara shan kunu. Yayi gyaran murya yace
‘To yanzu dani kike wannan hayagagar ko kuwa Aishan zan kirawo kiyi mata?’
Ta kara kulewa tana harararsa
‘Au hayagaga ma nakeyi ko? Ka kasa yin adalci tsakanina da matarka kuma yaran naka ma bazaka yi musu adalci ba saboda ana zuga ka ko?’
Ya tsani tace baya adalci saboda shi ya san iya karfinsa yana kwatantawa, yayi tsaki
‘Zahra kada fa ki gaya min magana saboda kinga Ina sauraronki. Duk abinda kika gani sun zo da shi Aisha ce ta siyo musu da kudinta don ni ban ma kwance kayan ba kuma ba wannan korafin ya kamata kizo kina yi ba godiya ya kamata kije kiyi mata. Tunda idan ban manta ba da kika je Umra banda dabino na ganin idona babu abinda kika bata kuma har yau ban ji korafinta ba. Idan kuma tafi yiwa Rukayya tsaraba ina jin ba sai na gaya miki dalili ba kema kin san dalilin ko. Saboda haka ki fita ki bani waje so nake na huta ba wai surutunki nake son ji ba.’
A fusace tace
‘Dole ka koreni tunda ka kasa yi mana adalci, tafiya Dubai din ma ai ba haka aka tsara ba amma da yake abun duk shiri ne sai kuka wuce da matarka saboda kai kanka ka san ni ya kamata ka fara zuwa dani wata kasar ba ita ba. Yara kuma ai da kudin ubansu aka yi sayayya don haka sai ayi musu adalci ni din dai da aka raina sai a cigaba da murdewa hakki.’
Mamakinsa ya karu saboda ya kasa gane dalilin wadannan maganganun da take zubawa haka barkatai. Yayi tsaki yace
‘Zahra, Aisha ita ta biyawa kanta kudin zuwa Dubai kuma duk wata tsaraba da ta yiwo kudinta ta saka tayi, zabi ya rage naki ko ki yarda ko kada ki yarda. Idan dai wannan shine rashin adalci to an ki ayi miki adalcin idan kina da karfi ki shake ni nayi miki adalcin. Ki fice min daga daki so nake na huta bana son wannan hayaniyar.’
Ta hadiye malolon da ya tokare mata makogoro tace
‘Shikenan saboda ka auro fitinanniya ba zan gaya maka gaskiya ba sai ka dinga korata, to wallahi…'
A fusace ya mike ya dauki mukullansa da wayarsa ya fice ya barta ba tare da ya gama jin abinda zata fada ba.
Ta share zafafan hawayen da ya gangaro kan kumatunta; ya kasa yi mata adalci yanzu kuma zai raba mata kan yara. Ta tabbatar wanna shirin Aisha ne. Kuma saboda ita ya mayar da ita ‘yar matsiyata shikenan komai sai ya bawa Aishan kudi yace da kudinta takeyi bayan musamman ta sa aka tambayar mata albashin Malaman gwamnati. Ta tabbatar kudinsa ne Aishan take facaka da su haka, amma zata yiwa tufkar hanci.
Tayi kwafa ta fice daga dakin
………..
Yana fita ya kirawo Aliko suka fice, ya kaishi gidan Yaya Bello. Can ya zauna har dare, ya shiga gidan Hajiya inda ya zauna suka ci abinci sannan ya kamo hanya ya dawo.
Lokacin da ya shiga gidan babu kowa a falo sai Rukayya da take zaune bata komai yayinda Yusra take kan dining table tana yin homework. Bayan ya amsa sannu da zuwansu yace
‘Rukayya taso na raka ki ki taya antinki kwana ko?’
‘To Abba, bari na dauko kayana.’
Ta shige dakinsu na kasa inda nan suke ajiye tarkacensu shi kuma ya haye sama, bayan ta fito ta haye sama.
Yana zaune a falon yayinda Mommy take zaune itama tana kallon TV, bayan Mommy ta amsa sallamarta tace
‘Mommy Abba yace