Showing 84001 words to 87000 words out of 166068 words
don duk abinda yake so uwarsa yake gayawa ta sa ayi masa ko ana so ko ba a so.
Yana dauka kafin yace wani abu aka yi masa sallama daga daya bangaren da muryar da ba ta Saddiku ba. Cike da tsananin mamaki ya amsa sallamar inda kai tsaye mai sallamar yace
‘Sunana M. K. Takai, jami’i ne na hukumar road safety, zamu so muji alakar ka da mai wannan wayar da nake kiranka da ita.’
Yayi gyaran murya cikin sanyin jiki yace
‘Ni mahaifinshine.’
‘To Alhaji yaronka yayi hatsarin mota a nan kan tin gidan gwamna, a halin yanzu muna dakin bayar da taimakon gaggawa na asibitin Murtala da yake cikin birni. Zamu so ka zo domin kaga halin da yaranka suke ciki domin su biyu ne a motar.’
‘Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun! Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun. Officer gani nan zuwa yanzu-yanzu in Sha Allah.’
Ya ajiye wayar ya mike da gaggawa ya nufi daki, ta bishi da sauri ta sameshi a gaban durowar mudubi ya dauko mukullin mota ya juyo.
‘Me ya faru da Saddikun ne? Fita zaka yi?’
Ya dan tsaya yana fuskantar ta sannan yace
‘Accident yayi, ina jin a motar Mommynshi ne. An dai ce yana Murtala yanzu zan je na gani.’
Ya wuceta ya nufo falon da sauri, ta sha gabansa a falon yana dab da fita.
Ta kama hannunsa tace
‘Tsaya kaji mana. Ka san fa yanzu babu security kada kaje fa trap ne aka yi maka don ka fito, ka san yanzu babu wuya an yi kidnapping mutum.’
‘To ai da wayar Saddikun aka kirawo ni kinga ko ma wane yana tare da Saddikun kenan, gara kawai naje dare yana kara yi.’
‘To Amma ka kirawo Mommy ka tambayeta ta duba maka dakin Saddikun ta tabbatar, ka ga idan yana nan zai iya yiwuwa sace wayar aka yi. Tunda ka ga ka hanashi yawon dare kuma yanzu fa duba ka gani wajen sha biyu saura, yaushe ya taba kaiwa haka a waje?’
Ya dan yi tunani kadan, ya koma ya zauna a bayan kujera ya zaro wayarsa daga aljihu yana fadin
‘Bari na kirawota na tabbatar din kam.’
Ya lalubo lambar Zahra ya danna mata kira, cikin yanayi na bacci ta amsa wayar
‘Yallabai.’
‘Zahra. Ina Saddiku? Ya dawo gidan kuwa?’
Ta dan dauke wayar daga kunnenta ta duba lokaci sannan ta bashi amsa
‘Ya dawo mana, yana dakinsa yana bacci fa.’
‘To don Allah ki je ki duba kiyi min confirming zan kira ki nan da minti biyar.’
Ya ajiye wayar ya zauna yana jiranta.
Ita kuma tana ajiye wayar tana mamaki; har zuwa lokacin da ta kwanta wajen sha daya dai ta san Saddiku bai dawo ba amma tayi masa waya yace mata yana hanya. To wani munafukin ne kenan ya gaya masa bai dawo ba zai tashe ta daga bacci da wannan tsohon daren. Ta saka hijabinta ta sauko ta fito daga cikin gidan, tana fitowa farfajiyar gidan taga babu motarta don haka ta tabbar bai dawo ba. Ta haska fitila ta kirawo Malam Sado, nan da nan ya karaso inda take.
Tace
‘Malam Sado Saddiku bai dawo ba?’
Cikin girmamawa ya bata amsa
‘Bai dawo ba Hajiya ai yana tafe dai ko da wanne lokaci zaki iya ganinsa.’
‘Don Allah da ya shigo kace nace ya kirawo ni a waya, bana son na kirawoshi yanzu ya dauka yana tuki ga dare.’
Ta sallameshi ta koma ciki ta rufe gidan.
Tana shiga falon wayar Abba ta shigo, tana dauka yace
‘Ina Sadikun?’
‘Yana dakinsa, bacci ma yake don ta taga na leka ban zagaya ba saboda dare.’
Ya ajiye wayar ya dubi Aisha dake tsaye a gabansa
‘Kin ji kuma wai yana gidan.’
‘To ai shi nake gaya maka, kada kaje trap ne kai ake nema ba Saddiku ba.’
Ya dan yi shiru yana tunani, jimawa kadan yace
‘Bari dai naje gidan na gani, ko babu komai na ji wanda ya bawa wayar tasa.’
Ta sake shan gabansa ta langabe, ya dafa kafadarta yace
‘Gara naje na gani don zai iya yiwuwa boye min takeyi don kada nayi masa fada da safe. Idan na sameshi a gidan yanzu zan dawo, ko ma menene zan kirawo ki a waya in Sha Allah.’
Ya fice tana yi masa a dawo lafiya.
……..
Yana taba gate din gidan Malam Sado ya taso yana haskawa, yana gane wanda yake bude gate din ya ja baya ya kwashi gaisuwa. Ya karewa tsakar gidan kallo a takaice, motar Zahra bata wajen da aka saba ajiyeta. Yace
‘Sado ina motar matar gidan?’
Ya sosa keya sanna cikin in ina yace
‘Yallabai Sadiku ya fita da ita ai tun kafin magriba, sai dai ma yau yayi dare sosai amma na san yana tafe da izinin Allah.’
Ko sauraronsa bai yi ba ya nufi kofar shiga gidan a fusace, iya karfinsa ya buga kofar saida ya buga sannan ya tuna akwai mukullin kofar a hannunsa. Ya saka mukullin ya bude kofar ya shiga, kai tsaye ya haye saman.
Tana zaune a kan gado tana muttsike ido tana shirin saukowa don ta zata Saddiku ne ya dawo. Ta ja tsaki ta mika hannu ta janyo hijabinta a daidai lokacin da ya bude kofar ya shiga dakin.
Ta san fada zaiyi a kan fitar Sadiku don haka ta kara tsuke fuska tayi shirin kora masa jawabi.
Cikin dacin rai yace
‘Zahra, kika ce min Saddiku yana nan yanzu kuma naga baya nan, ina ya tafi? Don me zakiyi min karya?’
Ta mike tsaye ta fuskanceshi
‘Karya kuma? Wai kai don Allah me ya sa kake….’
Ba zai iya sauraronta ba don haka ya katseta da murya mai cike da damuwa
‘Zahra garin ki cutar da ni kina cutar da kanki, kin bashi mota duk da na hanaki baki ji ba, na saka masa doka kina taimaka masa yana karyawa. Waya aka bugo min da wayarsa cewa yana asibiti yayi hatsari a motar, yana can rai a hannun Allah. Nayi tunanin ya kamata a ce yana gida shi yasa na zata ko wani wasa ne ko karya don na san ya kamata ace yanzu yana gida, ashe baya nan. Allah ya sauwake, kin cutar da kanki kin cutar da mu baki daya.’
Tuni ta daskare jiri ya fara dibanta, kwakwalwarta ta daskare don tun bayan rasuwar mahaifiyarsu bata kara shiga tashin hankali irin wanda ta shiga yanzu ba da yake gaya mata Sadiku yayi hatsari. Ya juya zai fice daga dakin, cikin zafin nama ta dafa kafadarsa tana fadin
‘Sadiku fa kace min, la ilaha illallah! To yanzu yana ina? bari na taho muje.’
Hannu ya saka ya tureta daga jikinsa ta koma kamar zata fada kan gadon, ya fice ba tare da ya sake kallonta ba.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
28
Nan ta zube tana fitar da hawaye masu zafi; Sadiku yayi accident? A wannan daren? Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.
Ta dafe kirjinta wanda yake kara kuntata zuciyarta ta ja jiki daga inda ta zube ta koma kan gadon. Ta kifa kanta a kan filo ta fashe da kuka.
Bata san tsawon lokacin da ta dauka a haka ba amma lokacin da ta daga ta duba agogon wayarta karfe uku na dare saura kwata. Nan da nan ta dauki waya ta bugawa Abban don bai gaya mata koda asibitin da aka kai Saddikun ba. Ta kirawo shi ya kai sau goma amma bai dauka ba, don haka hankalinta ya kara tashi.
Bata yi niyyar saukowa ta shirya yara su tafi makaranta ba amma sai ta tuna idan basu tafi makarantar ba damunta zasuyi tayi; musamman da yake Rahma ta tafi, don haka ta sauko bayan ta idar da sallar asuba ta fara shirinsu.
Har karfe goma na safe bai dauki wayarta ba, so take kawai ya gaya mata inda Sadik din yake amma ya ki daga wayar. Haka ta hakura ta zauna tana ta abu kamar zautacciya.
--------
Yana fita ya kirawo Aisha ya sanar da ita halin da ake ciki, ya wuce asibitin.
A emergency ya samesu; kusan a sume Saddikun yake duk da dai likitocin sun sanar da shi allura akayi masa ta sashi barchi. Ya sami karaya a hannun hagu, sannan kuma ya yanke a cinyarsa wanda sun riga sun yi masa dressing sannan kuma akwai sauran ciwuka kanana a waje daban-daban a jikinsa. A take likitan ya bawa Abban shawara a mayar da shi asibitin kashi saboda a duba hannunsa sosai.
An nuna masa Munir sai dai Abban bai san yaron ba, kuma ba a sami lambar iyayen yaron ba don tun a wajen da akayi accident din aka sami wani ya dauke wayar tasa. Bai sami wani babban ciwo ba sai kurjewa nan da can sannan kuma da firgita da yayi, don haka aka yi masa allura yake ta barci bayan an wanke masa ciwukan.
Kafin asuba an gama duk wasu shirye-shirye aka saka Saddiku a ambulance Abba ya bi su a baya bayan ya sami wanda zai tsaya masa a kan Munir. Suna zuwa aka kwantar da shi; wajen karfe takwas da rabi likitocin suka shigo.
Nan da nan aka duba Saddiku aka yi masa hotuna, aka tabbatarwa Abban karayar hannunce kawai matsala. Kafin a gama hotunan nan ya faraka, babu abinda yakeyi sai kuka da kiran Mommy. Don kamar ma baya gane mutanen da suke kansa balle ya gane Abban.
Nan da nan aka sake yi masa allura ya koma bacci, aka gyara shi aka kwantar da shi. Lokacin wajen karfe tara da rabi.
A take Abban ya dauki waya ya kirawo Rahama ya sanar da ita halin da ake ciki ya roki alfarma tazo ta zauna da Saddiku a asibiti; ta jajanta masa hatsarin sannan ta fara shiri. Tana shiryawa tana mita don tayi alkawarin ba zata sake zuwa gidan ta zauna da yara ba ko yanzun ma da Zahra ce ta kirawota ba zata je ba.
Amma tana jin nauyin Abba, ba zata iya ki ba. Tayiwa Ummansu sallama ta nufi asibitin.
Rahama tana fita Ummanta ta fara waya tana gayawa dangi Saddiku yayi accident; bayan ta kirawo su Murja ta kirawo Zahra ta jajanta mata. Sai a lokacin ta sanar da ita ai Rahama ta tafi asibitin kashi wajen Saddiku.
Taji haushin Abban da yaki daga wayarta har ya gayawa danginta inda Saddikun yake amma ita bai sanar da ita ba. Su Yaya Murja duk sun mata waya a kan kafin azahar zasu sameta a asibitin. Nan da nan ta tashi ta soya kwai da dankali ta zuba ruwan zafi a flask sannan ta shiga wanka.
Saida ta gama shiryawa ta kirawo Abban taci sa’a ya dauka, kafin ta gaisheshi tace
‘Ya Saddikun? Sai kiranka nake baka dauka ba, don Allah kuna ina?’
‘Mtsewww. Ki zo nan asibitin Murtala, akwai yaron da sukayi accident din tare da Saddikun ko zaki gane shi don ni ban sanshi ba . Har yanzu bamu sami iyayensa ba, ki zo ki gani ko kin san iyayensa in ya so daga nan kya wuce asibitin kashi.’
‘Ina jin Munir ne yaron kuma wallahi nima ban san iyayenshi ba, sai dai ko idan ya farfado a tambayeshi.’
Sukayi sallama ta ajiye wayar, ta karasa shiryawa ta shiga mota Malam Ali ya ja suka wuce asibitin kashi.
Haka Abban Sadiku ya zauna a asibitin Murtala wajen Munir har saida Munir din ya farfado, aka samu aka tambayeshi. Nan ya bayar da lambar babansa aka kirawoshi, ba a gari yake ba don haka kaninsa ya turo. Kafin ya iso Abba ya gama biyan duk wani abu da ake bukata an canzawa Munir daki, an sayo magungunan da yake bukata; duk da ma likitan yace zasu iya sallamarsa zuwa gobe.
………..
Ba karamin tashin hankali Mommy ta shiga ba da ta ga Saddiku, musamman da yake lokacin da taje ya farka yana kukan hannunsa yana ciwo. Da kyar nurse ta taimaka mata ya Sha shayi Rabin kofi sannan aka sake yi masa allura ya koma bacci.
Bayan yayi bacci ta barshi da Rahama ta fito daga dakin ta sami waje kan wata baranda ta zauna; ta rasa me yake mata dadi. Matse hawaye kawai take tana ajiyar zuciya.
Tana na zaune tana kirga motocin da suke shigowa wajen ta hango motar Amina, da sauri ta fito daga motar ta karaso wajen Zahran. Tana zama ta fada jikinta ta fashe da kuka, Saida tayi mai isarta sannan ta dago ta kalli Amina tana share kwalla
‘Amina kinga Sadiku kuwa yanda ya zama?’
‘Hmm! Na dai ga motar da ina tahowa Zahra, wallahi wannan motar ma idan aka ce na ciki duka sun mutu ba zan yi mamaki ba. Kuma kamar ita kadai ce motar ba tare da sun bige kowa ba sukayi hatsarin. Gaskiya abun da mamaki.’
Ta mike tana fadin
‘Tashi muje ki gan shi.’
Suka mike suka koma dakin gaba daya.
Suka tsaya a gefen gadon nasa bayan sun gaisa da Rahma, har yanzu bacci yakeyi sai dai kana kallon fuskarsa ka san a cikin wahala yake baccin.
‘Kin ganshi ko Amina, duk jikinsa ciwo ne kuma an ce karaya ce a wannan hannun sai gobe za a yi masa aiki.’
‘Allah ya baka lafiya Saddiku.’
Amina ta fada cike da tausayawa.
Ta jata suka fito suka koma inda suka tashi suka suka zauna, suna zama ta share kwalla tace
‘Kin ganshi ko Amina? Kuma fa Abban yace daya yaron da suke tare a motar shi buguwa kadan yayi, amma dubi Saddiku. Ya za ayi na yarda ba hannu aka sa masa ba, wannan ma ina jin kasheshi aka so yi Allah ya ja kwanansa.’
‘Gaskiya ne kawata, sai ma kin ga motar yanda ta lalace gaba daya zaki san nisan kwana ne ya hanashi mutuwa. Gaskiya wannan abun kam sai kin mike tsaye.’
Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan Zahran tace
‘Wallahi ba zan yarda ba, babu wanda nake zargi sai matar ubansu don motar ma ai tunda tana hawa ba zata so na hau ba. Na samo takardun filin nan ma amma bari a kwana biyu mu ga jikin Saddikun sai muje a gama komai; in sha Allahu matsalar kudi ta kare komai tsadar aiki sai inda karfina ya kare.’
‘Gaskiyarki kawata, kin san hatta faduwar Saddiku jarrabawa ma kawai shiru nayi miki amma ina zargin matar nan. Tunda kin ga Saddiku yana da kokarinsa amma ace jarrabawa ta gagareshi.’
Haka suka cigaba da tattaunawa Amina tana kara zuga ta a kan su dauki mataki.
Kafin yamma dangi duk sun zo anata duba Saddiku, don saida likita ya hanasu shiga dakin yace su daina damunsa.
Har dare yayi Zahra tana nan a asibitin, sauran yaran kuma suna gidan ta barsu da Jummai. A yanda ta tsara Rahma ta tafi ta kular mata da gidan ita zata zauna da Saddiku zuwa a yi masa aiki don an ce da safe karfe bakwai za a shiga.
Bayan sallar Isha’i Aisha ta dafa macaroni da sauce din kaza, ta sami flask ta zuba na asibiti. Ta zuba madarar waken suya mai dumi a flask ta hada Abban ya dauketa suka nufi asibitin.
Babu kowa a wajenshi daga Mommy sai Rahma, ya dan sami sauki don idonsa biyu kuma ba kuka yake ba. Da kyar ta bude baki ta amsa gaisuwar Aisha, itama Aishan sai taja jikinta. Ta yiwa Sadikun sannu ta koma kan dadduma kusa da Rahma ta zauna, suka gaisa da Rahman suka dan taba hira.
Basu fi minti goma Sha biyar ba Abban yace ta tashi su tafi, ya dubi Zahra yace
‘Kema ki tashi mu tafi, Rahma ta kwana da shi in ya so da safe kya dawo.’
Aisha ce ta yiwa Rahma sallama ta fice sai Abban ya bi bayanta.
Saida ta jira Abban ya fice ta ja Rahma gefe ta rada mata
‘Kada ki bashi abincin da matar ubanshi ta kawo, akwai ragowar burodi da ruwan zafi a flask din da na zo da shi ki hada masa kawai tunda da kyar yake cin abinci. Wanda ta kawo ki bada shi kawai.’
‘To.’
Sukayi sallama ta fice; Rahma ta bi bayanta da kallo tana jijjiga kai tana mamakin wannan kiyayya da zargi da ake wa Aisha don ita bata ga alamar cutarwa a tare da Aishan ba.
……..
A hankali ta biyo bayansu domin ta shirya tijarar da zatayiwa Abban idan Aisha ta shiga gaban mota; a nan zata nuna musu iyakarsu don babu yarinyar da ta isa ta shigar mata gaban motar miji.
Shida Aishan suka fara isa wajen motar, yana budewa ta shige bayan motar. Bayan ya zauna ya juyo ya dubeta
‘Kika shige baya?’
Tayi ‘yar dariya tace
‘To mai guri ya zo ai dole mai tabarma ya nade ko, naji kace da Mommy zamu tafi kaga kuwa ita ya kamata ta zauna a nan.’
Kafin ya bata amsa Zahra ta karaso, babu haske sosai a wajen don haka bata hango Aisha ba. Cikin isa ta fizgi murfin kofar motar, sai dai ga mamakinta babu kowa a wajen; ta hango Aishan a bayan motar. Ta shiga ta zauna cike da isa tana ta wani cin magani ta rufe kofar motar.
Ba tare da kowa yayi magana ba Abban yaja motar suka nufi gida.
Kwanan Zahra ne don haka Aisha ya fara ajiyewa sannan suka wuce.
Ta tanadi tsiya kala kala da magnaganu masu zafi da zata gaya masa idan har ya kuskura yayi mata maganar bawa Sadiku mota, sai dai ga mamakinta suna shiga gidan ya rufe gidan; bayan yara sun sanar da shi Jummai ta tafi; ya shige dakinsa ya barta da yara suna tamabayarta labarin Saddiku.
Iya haushi ta shaki haushin Abba sai dai ko sauraronta bai yi ba sannan kuma ita kanta damuwar halin da ta baro Saddiku ya isheta. Haka ta kwana cikin matsananciyar damuwa.
-------
Karfe bakwai aka ce za a shiga da Saddiku tiyata don haka tun karfe shida da rabi Abban ya gama shiryawa. Ya riga ya sanarwa Aisha ta hada masa abincin safe da nashi da na ‘yan asibiti don haka ko abinci