Showing 87001 words to 90000 words out of 166068 words

Chapter 30 - UWAR SADIKU COMPLT BY SAKINA YAZID.txt

11 Jul 2024

25414

bai nema ba a shirye ya sauko.


Yara sunata shirin makaranta duka suka gaisheshi. Ya wuce kichin inda ya jiyo motsinta; bayan ta gaishe shi tace

‘Ba zaka ci abinci ba? Kafin ka gama Jummai ta karaso sai mu tafi tare.’

‘Yanzu zan tafi na karya a can, ki jira Malam Ali idan ya kaisu makaranta sai ya dawo ya kaiki, don akwai takardun da sai na saka hannu sannan zasu shiga da shi tiyata. Ni na tafi.’

Bai saurari amsarta ba ya fice.

Ta share kwalla; itama tana so ta ga Sadikun kafin a shiga da shi tiyata shi yasa ma taso tafiya yanzun, tayi kwafa ta cigaba da aikinta.

Ko da Malam Ali yazo daukan yara da kanta ta fito tace masa da ya ajiye yaran a makarantar ya zo ya kaita asibiti. Ya amsa suka fice shi da yara.

Yana ajiye yara a makarantar kiran Abban ya shigo wayarsa, bayan sun gaisa Abban ya tambayeshi inda yake ya sanar dashi. Abban yace

‘Idan ka ajiyesu ka wuce office ka jira ni.’

‘To ranka ya dade Hajiya dai tace idan na saukesu naje na kaita asibiti, idan na kaita asibiti sai na zarto office din kenan Ranka ya dade.’

‘Ali, ni kake wa aiki ko ita?’

A take ya shiga taitayinsa, yace

‘Ah Ranka ya dade!’

‘Daga nan inda kake ka kai min mota office ka zauna ka jirani.’

Ya tsinke wayar ba tare da ya saurari amsarshi ba.

A take shi kuwa ya karkata kan motar ya tafi office. Ya san Mommy tana da lambarsa kuma bai san me zai gaya mata ba idan ta kirawoshi don haka yana shiga office din ya kashe wayarsa tunda ya san idan Abba yana nemansa zai kirawo wani a office din yace a bashi.

Haka tayi ta jiran Ali bai dawo ba, shi kuwa Abba tunda ta kirawoshi ya ki dauka ta sa a ranta ba zata sake kiranshi ba a kan maganar Saddiku.
Sai can wajen sha daya Suwaiba ta kirawota zata tafi asibitin don haka sai tace ta biyo mata su tafi.
………..

An yi aiki kuma komai ya tafi daidai sai dai likitan ya bada umarnin ‘yan dubiya su dan saurara zuwa awa ashirin da hudu kafin nan zugin hannun yayi sauki. Don haka mommy da Abban ne kawai suke zuwa.

Musamman Amina ta dauko mata hoton motar yanda ta kwankwatse kafin daga baya road safety suka janye motar.
--------

Tunda Hajiya ta sami labarin hatsarin hankalinta yake kan ta zo taga Saddiku, sai dai Abba ya hanasu zuwa. Saida ya kwana biyar a asibiti lokacin ciwon yayi masa sauki tunda har ana hira da shi, kuma duk ciwukan jikinsa sun fara nuna alamar warkewa tunda tun a asibitin Murtala aka yi masa dressing dinsu.

Malam Ali ya tura ya dauko Hajiya tare da Yaya Saratu da kuma Innani, Yaya Bello shima duk da kusan kullum sai ya zo haka ya biyosu suka taho.

A nan dakin aka shimfida musu tabarma suka zauna ana ta jajantawa ana ‘yan hirarraki har Abban.

Wajen karfe sha daya sai ga mutanen gidan su Aisha; Hajiya, Anti Uwani da kuma Yaya Zuwaira wanda Yaya Abubakar da kanshi ya kawosu.

Cikin mutunci da girmamawa suka gaisa da su Hajiya, itama Zahra da yake a gaban Hajiya ne da Abba cikin mutunci aka gaisa. Suka jajanta musu sosai suka duba Saddiku. Suka dan taba hira, jimawa kadan suka ajiye musu leda cike da kayan marmari ga kuma wata ledar da kajin gidan gona guda shida gyararru. Yaya Abubakar ya zaro kudi naira dubu goma ya ajiye a gaban Hajiya yace a saya masa abun tabawa. Suka fito ana son barka, Abba ya biyosu yana rike da hannun Yaya Abubakar yana yi musu godiya.

Bayan sun fita Yaya Saratu ta dubi Zahra tace

‘Ikon Allah, albasa batayi halin ruwa ba. Mutanen gidansu masu mutunci da karamci amma kanwar taki kam babu hali.’

Ta jijjiga kai tace

‘Hmmm! Don ma baki zauna da ita ba, ai micijin sari ka noke ce lamba daya.’

Kafin ta bata amsa Abban ya dawo don haka sukayi shiru.

Jimawa kadan Abban yace Malam Ali ya mayar da su gida, ya bashi kajin yace ya kai gida ya bawa Jummai. Sukayi musu sallama suna sake jajantawa suka fice.
_

Satin Sadik biyu a asibitin lafiya ta fara samuwa domin har likita ya sa masa ranar sallama. Yana iya rataye hannunsa ya yita yawo a cikin asibitin sannan kuma yawancin ciwukan jikinsa duk sun warke, sai karayar wadda dama zata dauki lokaci.

A zaune suke ita da Amina a farfajiyar asibitin, inda suke babu nisa da dakin Saddikun don suna hango kofar dakin.

Zahra ta dubi Amina tace

‘Ina jin ma zuwa gobe zasu sallameshi don kin ga yana yawonsa ko ina.’
‘Ma sha Allah ai haka ake so, zakaran da Allah ya nufa da cara kenan.’

‘In Sha Allah.’

Sukayi shiru na dan lokaci jimawa kadan Zahra tace

‘Ina jin gobe zan fito miki da takardun filin nan tunda kin ce akwai mai saye a hannu. Mun gama magana da Yaron Malam yace an daure min bakinsa duk abinda zan yi na yi ba zai iya magana ba don haka a siyar kawai ki turo min kudin account dina.’

‘Ko ke fa kawata, ai gara da kika motsa.’

‘Na gaji ne kawata da cin kashin da mutumin nan yake min, don a kan accident din nan ina jin da ya sami dama zai iya kai min duka.’

‘Ai kece kike abu da tsoro uwar Sadiku, da kin biye min da tuni an sa miki shi a kwalba wallahi idan kika ce ya zauna ko uwar da ta haifeshi bata isa tace ya tashi ba sai in ke kika so.’

Ta jijjiga kai tace

‘Hmmm! Ai kuma yanzu dole ayi hakan kawata tunda yana so ya nuna min taurin kai. Wannan wulakanci da yake min ba zan dauka ba don na ga kamar ya manta lokacin da muke hannu baka hannu kwarya na hakura da komai na zauna da shi yanzu ya sami kudi ya auro matar so zai yi min tijara. Wajen wancan Malamin naki zamu fara zuwa daga baya sai muje wajen yaron Malam, na san kudin filin nan zai isheni.’

‘Zai isa sosai ma, magana ake fa ta wajen miliyan uku da rabi zuwa hudu kinga kuwa ko Aisha kike son siya ai kin saya kin gama.’
Sukayi dariya suka tafa.
Suka karasa hirarrakinsu, daga baya Amina tayi mata sallama ta tafi.

……….

An sallami Saddiku ya dawo gida inda zai karasa jinya, dakinshi na cikin gida aka gyara masa ba don yana so baya koma. Tun daga asibitin Rahama tayi musu sallama ta wuce gida akan idan ta huta gobe zata samesu a gidan.

Ranar da aka sallameshi washegari Amina ta gama cefanar da filin da Mommy ta bata takardunsa. Ko da aka gama ciniki akwai takarda da ake bukatar saka hannun mai fili don haka ta kawowa Mommy takardar har gida. Sadikun ta sa a gaba ya sa hannu a takardar ba tare da ta bari ya karanta ba balle ya gane ta mecece, burinta tunda dai sunansa ne a kan takardar filin kuma ya balaga ko daga baya idan zancen ya tashi to shi ya sayar da filinsa.

Naira miliyan hudu da dubu dari biyu aka sayi filin; a hakan ma ance don karami ne. Amma duk da haka naira miliyan uku da rabi Amina ta kawowa Zahran ta haye kan sauran, bayan ta gama godiya kuma ta tura mata dubu dari da hamsin tace ga tukuici da alkawarin idan an gama aikin ma zata kara mata idan an yi canji. Ta kirga kudinta dubu dari takwas da hamsin ta tafi tana murnar wannan kazamar ribar da ta samu.

Sai daga baya da Sadikun ya kara samun lafiya sannan Amina ta yiwa Zahra bayani shi malamin nata a can wani kauye yake a karamar hukumar Doguwa, Doguwan ma a cikin daji. Don haka ita Amina tana da amintaccen yaronta wanda shi yake kaita saboda nisa kuma ga hadari, nan suka saka rana a kan nan da sati mai zuwa idan an yiwa motar Amina service zasu je in ya so idan suka dawo suka huta sai suje wajen yaron Malam.

UWAR SADDIKU


Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)


29

Lokacin da aka kwantar da Saddiku a asibiti a dai-dai lokacin ne ake jarrabawar SSCE; wadda har an gama yiwa Saddiku rijista don ya gyara tashi wadda ya fadi English. Sai ranar da ya kwanta a asibiti ranar aka fara jarrabawar, don haka gaba daya Saddiku bai sami zana jarrabawa ko daya ba.

Tun a lokacin Mommy ta sami Abban a kan yayi magana da malaman makarantarsu Sadiku din za a samu mai yi masa amma yace sam bai yadda wani yayiwa Saddiku jarrabawar ba. Gaba daya ma kin saurarta yayi, domin daga baya ma da yaga tana neman ta zagaya ta bayan gida ayi masa jarrabawar ce mata yayi in dai shine zai biyawa Saddiku kudin jamia to ya san baiyi wata jarrabawa a wannan shekarar ba kuma ba zai karbi wani certificate mai dauke da kwanan watan wannan shekarar don nema masa admission ba.

Duk wanda take jin zasu goya mata baya idan tayi magana sai suce ta bari Sadikun ya sami lafiya tukunna. Don haka dole suna ji suna gani aka gama jarrabawa babu Saddiku. Ya tabbata sai ya sake bata shekara guda a gida, daidai lokacin ‘yan ajinsu sun gama level 1 sannan zai sami damar gyara jarrabawarsa lokacin zai kama tare da Yusra kenan wadda a halin yanzu za ta shiga SS 3.
__

Tun bayan da ya biyawa Zahra Umra kamar yanda ta zaba yake tanadin biyawa kansa Hajjin bana; sai dai a yanda ya shirya tare da Aisha yake so su tafi.

Saura abinda bai fi shekaru goma yayi retire ba don haka yana da niyyar idan sun gama aikin Hajji sai ya sako Aisha a jirgi ta dawo gida shi kuma ya wuce Dubai; yana so ya fara shigo da kayan electronics yana sayarwa a Nigeria zuwa lokacin da zaiyi retire ya zama babban dealer. Da fari yana jiran sai ya bude shago amma abokinsa wanda yake masa jagoranci a harkar yace ya shigo dasu haka sai a kama hayar waje a ajiye ana siyarwa a kan sari, yayi na’am da shawarar don haka ya gama lissafin zarcewa Dubai daga Saudiyya.

Ita kanta Aishan bata san zai biya mata aikin Hajji ba don bai gaya mata ba, ya bari sai ya gama komai ya gaya mata; duk da dai yana sane da cewa ta taba yin aikin Hajji.
__

Satin da aka gama service din motar Amina sun gama tsara tafiya Doguwa sai kuma Amina ta kwanta zazzabi. Abu kamar wasa sai da ya kai ta kwanciya a asibiti kwana biyu; aka tabbatar da cewa zazzabi ne na malariya ya kamata da yawa. Wannan ya sa dole suka dakata da tafiyar.


Bayan an sallameta daga asibiti kuma akwai ‘yarta ta fari Asiya wadda take aure a Abuja, shekara kenan da yin aurenta sai a lokacin tazo ganin gida hadi da dubiya ga tsohon ciki; don haka dole suka kara daga tafiyar har Aminan ta kara samun lafiya kuma ta sami mai zama da Asiya. Tunda wannan tafiyar idan sun tafi da sassafe to da isa gari da samun ganin bokan zuwa dawowarsu gida wuni guda ne, don wata ran sai anyi isha’i take dawowa gidan.
__

A zaune yake a kan gado ya mike kafa ya dora computer a kan cinyarsa yana aiki yayinda ita kuma take kwance a rub da ciki a gefenshi. Kanta yana daidai wajen kafafunsa tana karanta littafi a waya kuma a lokaci guda tana wasa da yatsun kafarsa.

Ba tare da ya daina kallon computer ba ya kirawo sunanta

‘Aeesh.’

Itama bata dauke idonta daga kan wayar ba ta amsa

‘Yes My love.’

‘Na biya mana aikin Hajji fa, ni da ke zamu tafi nan da kwana goma. Gobe da safe ki shirya mu fita don takardunki ba a gama hada su ba da passport dinki kuma a goben nake son mu gama tunda kinga lokaci ya dan kure.’

Da hanzari ta mike ta dawo dai-dai fuskarsa, suna hada ido ta kyalkyale da dariyar da ta sashi dariya. Tace

‘Allah Habibi? Kai amma nagode. Allah ya kara arziki.’

‘Amin.’

Mamakin murnar da takeyi yake, musamman da yake ya san ta taba zuwa aikin Hajji bai zata abun zai rudata haka ba. Yanda kuma yaga tana murnar sai shima ya kara jin dadi, ya dinga binta da kallo yana murmushi.
Ta lalubi wayarta a inda ta yar da ita tana fadin

‘Bari na gayawa Hajiya.’

Har ta dauko wayar sai kuma ta sake jefar da wayar, ta dauke computer daga kan cinyarsa ta ajiye a gefe sannan ta rungumeshi. Suka dan dauki lokaci a haka sannan ta sakeshi ta kalli fuskarshi tace

‘Nagode sosai Yallabai, ba zaka gane yanda na ji dadi ba. Zan je na yiwa Abbana dawafi nayi masa addu’a.’

Ta sake kallonshi suka hada ido tace

‘Mijina ma zan yi masa addu’a Allah ya sa kada yayi min kishiya.’

Ya kyalkyale da dariya yace

‘Uhm! Wato gwano baya jin warin jikinsa.’

Ta wurkila ido tace
‘Dama shi gwano baya wari mutane ne da jiye-jiye.’

Ta dauki wayar ta mike tsaye ta barshi yana dariya.

Shima ya mika hannu ya dauki kwamfutarsa wadda ta ajiye masa a gefe ya cigaba da aikinsa.

Gaban mudubi ta koma ta tsaya, sai dai madadin ta kirawo Hajiya kamar yanda ta fada sai kawai ta kirawo Zahida. Tana dauka tace

‘Hida guess what?’

‘Ki fada min kawai sarkin jan rai.’

‘An biya min Hajjin bana da ni za a je.’

‘Aaaah!’

Suka fasa ihu a lokaci guda sannan suka kyalkyale da dariya.

Suka karasa magana suna ta murna.


Tana ajiye wayar yace

‘Wai ke da Zahida ba zaku daina yiwa mutane ihu ba?’

Ta sa hannu ta rufe bakinta tana dariya

‘Mantawa mukayi fa.’

Ta dawo gefen gadon ta zauna ta cigaba da waya tana gayawa ‘yanuwanta abun alkhairi.

Ranar haka Aisha ta kwana cikin tsananin murna; babban abinda yake kara sakata farin ciki shine zata je ta yiwa Abbanta da Mustafa addu’a. Sannan kuma zata kara rokawa kanta tsari domin ta kula idan dai zata cigaba da zama da Uwar Saddiku to tabbas tana bukatar tsari daga Allah.
………

Washegari suna zaune a falo suna cin abincin safe suna ‘yan hirarrakinsu ya dubeta yace

‘Idan muka gama aikin Hajji sai na sako ki a jirgi ki dawo gida, ni kuma na wuce Dubai. Akwai Abdurrahman zamu hadu da shi a can sai mu sayo kayan nan da nake gaya miki.’

‘Ma sha Allah, Allah ya nuna mana.’

Suka dan cigaba da cin abincinsu.

Jimawa kadan ta kurbi shayinta tayi gyaran murya tace

‘Alhaji.’

Ya kalleta da mamaki saboda ba haka ta saba kiransa ba, tayi murmushi tace

‘To ka tafi dani Dubai din mana, ai ko jaka ma na rike maka ko?’

Ya ajiye cokalin da yake hannunsa yana kallonta yana murmushi, ta cigaba

‘Kuma ma ya za ayi ace kamar kai ka tafi Dubai ba tare da ni ba, haba mana. Ai ko jaka ma sai na rike maka kuma in ka gaji ma ko tausa ai nayi maka.’

Ya jijjiga kai yana murmushi yace

‘Small girl. Wai ni zaki tsara ko?’

Ta dauko kwanon dankali ta ta dawo kujerar kusa da shi tana zumbura baki

‘To ba sai ka tsaru ba. Don Allah mu tafi tare kawai, ya za ayi ka tafi Dubai kai kadai wai sai kace baka da gata.’

Ta karasa tana kwantar da kanta a kafadarsa.
Ya shafa kumatunta yace

‘Nima ina son naje da ke amma dai ba yanzu ba, yanzu gaba daya kudin zan tattare nayi sayayya. Idan abun ya kankama wata rana zamu je dake.’

Ta langabe kai

‘Bari dai nayi Sallah nayi addu’a, watakila ka taka kulli kafin lokacin sai kaga mun tafi tare.’

Shima yana son tafiya da ita don ya san zai huta sosai, to amma tashin hankalin da Zahra zata yi masa kadai ya isheshi sannan kuma kamar yanda ya fada kudaden hannunsa bazasu kai ya tafi da Aisha ya kashe mata kudi yanda yake so ba; kwata-kwata ma kwana biyu yake son yi a Dubai din ya wuto Nigeria.

Haka suka karasa cin abinsu suka tashi.

Ita kuwa Aisha tana nan ta dana tarko don gaskiya tana son zuwa Dubai don haka ba zata bari damar nan ta wuce ta ba.
__

A zaune yake a falon yana hutawa da yake ranar Lahadi ce, tana zaune a gefensa yayinda Sumayya take wasanninta a gefe guda.

Ta dan yi gyaran murya tace

‘Um dama ina so na gaya maka, mijin yayar Amina ya rasu zamu je mata gaisuwa a gidanta da yake garin Doguwa.’

Da mamaki ya kalleta

‘Kin san nisan kauyen nan kuwa? To ke da wa zaku je?’
‘Ni da Aminan ne, a motar ta ma driver dinta zai kaimu.’

‘Ohk. To babu damuwa amma dai da kin bari sai next weekend, dama ina son gaya miki nextweek zan tafi aikin Hajji tare da kanwarki.’

Bata san yana shirin tafiya Hajjin ba don haka ta dan yi mamaki. Ta gatsina baki ta dan yi murmushi

‘Kuma da gaggawa haka? Allah ya kai ku lafiya Allah ya amsa ibada. Kace mu kadai zamuyi Sallah a gidan kenan.’

‘Eh daga ke sai yara ba, amma da an sallace zata dawo ni kuma na wuce Dubai na gaya miki zan je Dubai.’

‘Ok, tafiyar ta zo kenan? To Allah ya sa a je a sa’a.’

‘Amin ya Allah. Kinga idan muka tafi sai ki sami damar zuwa gaisuwar ko? Amma fa sai kin dinga hakura da fita tunda kin ga Saddiku bai gama warkewa ba.’

‘Eh kusan daga wannan din ma babu wata fita da zan sakeyi in Sha Allah sai dai ko gaisuwar Sallah in Sha Allah.’

Suka karasa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login