Showing 144001 words to 147000 words out of 166068 words

Chapter 49 - UWAR SADIKU COMPLT BY SAKINA YAZID.txt

11 Jul 2024

25423

ya sa ta zata damuwar rasuwar ce don haka ta saka ta a gaba ta dinga bata baki tana yi mata nasiha har ta samu ta sami natsuwa. Ta sakata a gaba ta fara karatun wanda kusan tare suka yi shi.


Sai da akayi kiran Magriba tayi sallah taci abinci sannan ta koma gidan. Bata kula Yusra ba har dare yayi suka kwanta.


……….


Ranar Talata da safe kamar yanda Abba ya saba bayan ya shirya zai fita aiki ya tsaya a falo wajen Goggo Binta domin ya gaisheta. Bayan sun gaisa ta sanar da shi cewa gobe zata tafi, ba zata sami damar kara kwana ba. Sai dai tayi masa alkawarin idan an kwana biyu zata dawo. Nan ya nuna mata babu damuwa goben idan ta shirya Malam Ali zai kaita har can Sumaila shi da Saddiku, ya tabbatar mata da cewa kafin ma ta tafi Aishan zata dawo gidan.


Yayi mata sallama ya fice aiki.


Ya san Asiha ta riga tafi aiki don haka sai bayan da ya zauna a office sannan ya dauki waya ya kirawota, ya sanar da ita ya kamata da ta koma gida ta hada kayanta don daga yau zuwa gobe da safe yake so ta koma gidan Zahra saboda Goggo Binta zata tafi.


Bata iya ce masa komai ba sai dai tace masa idan ya dawo sayi maganar.


Sukayi sallama suka ajiye waya.


Haka ta karasa wunin ta a makaranta tana tunani rigimar da za ayi domin ita abu daya ta sani; ba zata zauna da Yusra da Nana ba domin Nana duk abinda Yusra ta sakata shi take yi.


__


Tun bayan rasuwar Zahra da Yaya Murja ta koma gida take tunanin makomar yaran. Ta yi tunanin Abba zai sa Aisha ta dawo gidan domin kula da su to amma hakan bai kwanta mata a rai ba. Bata san Aisha sosai ba sai ta hannun Zahra, a iya wannan sanin kuma bata taba jin wani alkhairi a kan Aishan ba. Hasali ma Zahran ta nuna musu cewa Aisha tana da sharri sannan kuma tana bin malamai sosai don ta mallake gidan. Don haka take jin bai kamata a bar ta da yaran ba sai dai idan hakan shi kadai ne zabinsu. Tana da labarai da yawa na irin haka yanda matar uba take mayar da yara kalar tausayi saboda rashin uwa kuma zata yi iya yinta ta tabbatar hakan bai faru da yaran Zahra ba; duk da ta san abu ne maii tsananin wahala.


Sun yi waya ta san gobe Goggo Binta zata tafi don haka yau ta tashi da niyyar zuwa gidan suyi sallama. Gidan Suwaiba ta fara zuwa don su tafi tare.


A dakin Suwaiban suka zauna ita Suwaiban tana canza kaya suna hira. Cikin damuwa Yaya Murja tacewa Suwaiban


‘Jiya da mukayi waya da Yusra tace Abbansu yace Aisha zata koma gidan amma dakin kasa ya sa a gyara mata.’


Suwaiba tace
'To Yaya ai idan ma dakin Ya Zahran yace ta shiga ba wani abu bane, na san ma hakan za ayi. Watakila dai yana jira ne ya sami lokaci a kwashe kayan a raba tun da ko ana so ko ba a so kayan da suke nata ne sun zama na magada.’


'Hakane. To ni zaman nake ji; kin san fa duk labaran da muke ji a kanta ba masu dadi bane, kamar dai daga abubuwan da Zahran take fada matar tana da fitna ga sharri.’


Suwaiban ta dawo ta zauna kusa da ita a gefen gado ta fuskanceta tace


'To Yaya mu ya zamuyi? 'Yaya dai nashi ne don haka yanda yake so haka zai yi da su. Don kuwa kin san babu makawa ita zai bawa rikon yaran nan wanda hakan shine daidai.’


Cikin damuwa Yaya Murja tace


'Hakane. Ni da tunanina ko ayi masa magana idan ba damuwa ya auri Rahama, kinga dama ta saba zama da yaran shi kuma ya saba zama da mata biyu shikenan sai ta rike yaran ‘yar uwarta.’


Ta dan zaro ido


'Yaya kada fa ki manta shi ba dan uwanmu bane don haka bamu da uko da shi, kuma ita Rahman idan bata yarda ba fa?’


'Ai ba mu zamu yi masa magana ba, idan muka kaiwa Baffa shawara su sai su shawarceshi. Ita kuma Rahma ni bana ma jinta; ya za ayi taki yarda ma? Kalli fa shekarun da ta dauka babu aure, ai ina ga ko musu ba zata yi ba tunda ko babu komai ta san ba zata je gidan Zahra ta sha wahala ba.’


'Hmm! Kada dai ki ballo ruwa Yaya.'


Ta mike ta saka hijabinta tana fadin


'Mu tafi Yaya don ina son na dawo kafin ‘yan makaranta su dawo.’


Suka fice suka nufi gidan Zahra.


Lokacin da suka je gidan yaran duka suna makaranta sai Goggo da Jummai, suna nan zaune a falon kasa suna gaisawa Saddiku ya fito a shirye. Bayan sun gaisa suka dan taba hira sannan yayi musu sallama ya wuce wajen da yake koyon computer.


Nan suka zauna suka cigaba da hira.


Duk yanda Yaya Murja ta so taji yanda zamantakewa take tsakanin Aisha da yaran nan bata sami wani abun aibi ba. Duk da Jummai bata san wani abu game da Aisha ba saboda kwata-kwata Zahra bata bada damar hakan ba, amma dai abubuwan da ta sani game da ita duk alkhairi ne. Don haka basu sami wani abu da zasu iya kamawa ba.


Suna Shirin tafiya Yusra ta dawo, bayan ta ajiye kayanta ta zauna a wajensu suka cigaba da hira.


Daga bakin Yusran ne Yaya Murja ta dan ji wasu bayanai na karya wadanda suka kara tabbatar mata da cewa Aisha zata iya cutar da yaran nan idan an barta da su. Kafin azahar suka yi musu sallama suka tafi; Yaya Murja tana kara tabbatarwa da Suwaiba cewa gara idan an kwana biyu suje su sami Baffa a yiwa Abban magana ya auri Rahma.


__


Sai da aka yi sallar la'asar sannan Abban ya samu ya baro office, aiyuka sunyi masa yawa musamman da yake ya dauki tsawon sati bai je aikin ba. Yana shiga unguwar ya wuce wajen yaran, bayan ya dubasu ya tabbatar sun tafi islamiyya ya wuce gidan Aisha.


Sai da yaci abinci ya huta sannan ya sameta a falo tana kallo, bayan ya zauna yace


'Wai ya naga baki fara hada kayan bane, kin san fa ya kamata a ce yau kin koma saboda Goggo ma ta san ba su kadai za a barsu na.’


Ta kalleshi suka hada ido, tayi murmushin yake. Ta hada tafukan hannunta ta ta rufe tsakiyar fuskarta da su tana kallonsa ta gefen idonta.


Binta kawai yakeyi da ido yana mamakin kalaman da take son fada da suka yi mata nauyi haka, a lokaci guda kuma yana mamakin abinda ya hanata ta fara kokarin bin umarnin da ya bata.


Sai da tattaro duk wani karfin hali da take dashi ta bude baki a hankali tace


'Kayi hakuri gaskiya ba zan iya komawa can gidan ba.’


Kallon da yake binta da shi ya sa ta dakata da maganar ba don iya abinda ta so fada kenan ba.


Tsananin mamaki ya bayyana a fuskarsa, yace


'Ban gane ba. To ya za ayi da yaran? Kin san dai idan sun dawo nan dakunan ba zasu ishemu ba sannan kuma nan din gidan haya ne wancan shine nawa. Don haka kinga dole haka zaki koma can din. Idan ma akwai wani abu da kike so a gyara a gidan a hankali za a mayar miki da shi yanda kike so ai ko?’


Ta sake saita fuskarta ta dan jijjiga kai tana dubansa, suka dan yi jim suna kallon juna sannan tace
'Gaskiya ba wai gidan ne ba zan koma ba. Ka san dai raino abu ne mai wahala kuma mai nauyi, duk kwatancen da zan yi maka ba zaka gane ba. Gaskiya ba zan iya rike yaran bane ba wai gidan ne bai yi min ba.’


Ji yayi kamar ta buga masa guduma a ka, ya kalleta cike da tsananin mamaki wanda a hankali ya fara komawa fusata. Nan take itama ta bata rai ta kawar da kanta. Bayan ya gama kare mata kallo yace


'Ban fahimcekiba, kina nufin kice ba zaki zauna ki kular min da yara ba kenan? To ya kike so nayi da su? Haka za a barsu su cigaba da zaman kansu ke kuma gaki a nan a matsayin matata ko kuwa hakura zanyi da aikin na zauna na dinga kula da su?’


Ta sunkuyar da kai cikin murya kasa-kasa tace


'Ban sani ba, amma dai na san abinda ba zan iya ba. Kayi hakuri ka fahimce ni.’’


Cikin daga murya yace


'Ya za ayi na fahimceki Aisha, kina gaya min ba zaki iya zama da ‘yayana ba? Me suka yi Miki? Ko kuma kishin mahaifiyarsu ne zaki koma yi da su da har kike kyamatarsu haka?’


Wata zazzafar kwallace ta fado kan fuskarta; dama ta san babu wanda zai fahimceta musamman shi da yake so a yita kula da shi da ‘yayansa. Batayi magana ba don haka ya cigaba.


'Daman shi yasa tun farko kika ki zama a cikin iyalina? Kina nufin ni kadai kike so ba kya son zuri'ata Aisha? Wannan ai ba so bane. A kan idonki yaran suka zama marayu amma kice ba zaki iya kula da su ba ke ko ladan rikon maraya ba kya so? To ya kike so nayi da su?’


Tayi murmushi tare da share kwallar idonta, ta mika hannu ta dafa hannunsa dake ajiye a kan kujera. Ya kalli hannun nata sannan ya zare hannunsa tare da jifa da nata hannun. Gaba daya tsoron da yake zuciyarta ya fice don ta kula so yake yayi mata wata fassara da ban. Ta gaji da share kwalla don haka ta bari hawaye ya fara bin fuskarta, ta bude baki a hankali tace


'Tun kafin su zama maraya nake rikon marayu don idan ba na manta karatun islamiyya ba to wanda ubansa ya mutu shine maraya amma wanda uwarsa ta mutu musulunci baya kiranshi maraya don uba shine karshen gata. Ban san yanda zakayi da su ba amma dai na san kana da zabi kamar yanda musulunci ya tanada idan an sami irin wannan dangin uwa zasu iya rike yara, idan kuma lallai matarka kake so ta rike su to ai kana da damar da zaka kara aure ka sa matar a gidan. Ni bani da matsala da hakan. K..’


'Ke yanzu a kan ki zauna da yaran kin gwammace na kara aure? To naji kema kina da marayu, ai wannan ba zai zama matsala ba sai ki dauko su su dawo nan mu zauna tare. Wannan ma da kin yi magana ai da tuni suna nan.’


Tayi yake tace


'Daga baya kenan!’


'To don Allah su su Yusran me yasa ba Zaki iya rike su ba, yaran ma da kusan kowa ya iya kula da kansa? Me suka yi miki ko me uwarsu tayi miki da ya shafe su kika tsane su haka?’


Ta kula bata da wata mafita idan bata gaya masa gaskiyar abinda yake ranta ba. Ta muskuta kadan tace


‘Ba wai ba zan iya rike maka yara bane, hasali ma ko dan shege ka kawo zan iya rike maka shi har bayan ranka. Amma gaskiya ba zan iya zama da Yusra da Nana ba, idan ka cire su biyu zan iya rike sauran yaran.’


Kan sa ya kara kullewa, binta kawai yake da kallo. Ya gyara zama cike da bacin ran wannan rainin hankalin da Aisha take masa yayi ‘yar dariyar takaici yace


'Ah! Aisha kina bani mamaki. Yusra da Nana su kadai kika tsana? To me sukayi miki da ba zaki iya zama da su ba?’


Ta share hawaye tace


'Allah ya sani ban tsane su ba amma cutarwar da mahaifiyarsu tayi min tana da matukar yawa duk da kai ma ka san wasu sai dai ka ki gayawa kanka gaskiya.’


Ya bude baki zai yi magana ta dakatar da shi da hannunta ta cigaba


'Duk wata cutarwar da Zahra tayi min da Yusra take amfani, ban iya kai kara ba shi yasa ban taba gaya maka ba musamman bayan ka nuna mini yaranka masu tarbiyya ne ba zaka dauki laifinsu ba. Idan baka manta ba akwai lokacin da ka dinga kasa cin abinci na saboda yanda dandanon yake canzawa, to a wannan lokacin Yusra ake aikowa ta zo ta saka min sabulu a abinci wanda sai da Allah ya toni asirin ta na gane.
Yanzu ma kuma ranar da aka kwana uku da rasuwar mahaifiyarta tayi min alkawarin ba zata taba bari na maye gurbin uwarta ba kuma na tabbatar da gaske take.’


Ya nuna ta a raine


'Yanzu ke Yusran kike biyewa? Gidanta ne ko nawa da zaki kama zancenta?’


‘Ban iya rigima da tashin hankali ba kuma na tabbatar in dai da Yusra zan zauna to a cikin haka zan rayu. Ba zan iya ba, amma sauran yaranka gaskiya bani da matsala da su zan iya rike su kamar ni na haifesu.’


Ya ja tsaki ya mike a fusace, ya nunata da yatsa yace


'Wannan duk maganar banza kikeyi! Idan dai zamana kike a wannan gidan to na baki umarni gobe ki koma wancan gidan an gyara miki daki, idan kuma zaman kanki kikeyi to sai ki yi yanda kike so.’


Ba tare da ya saurari amsarta ba ya fice daga gidan.


Ta share hawaye ta bi bayansa da kallo; ta riga ta san daman ba zai fahimceta ba saboda yanzu abu daya yake so a kular masa da yaran ya koma harkokinsa. Itama zata so ace ta kular masa dasu amma bata shirya fada da Yusra ba don bata hango abun zai yi kyau ba.


Sai da ta gaji da share hawaye sannan ta tashi ta rufe gidan ta wuce daki inda tayi alwala ta kabbara Sallah domin ta san Allah ne kawai ya san halin da zuciyarta take ciki a yanzun.


UWAR SADDIKU


Written by


Sakina Yazid
(Innar su Amal)


42


Tana sane da cewa Goggo Binta zata tafi don haka gari yana wayewa bayan ta gama shirin tafiya aiki ta zubo sandwich din da ta yiwa yara a roba ta dauko abinda zata bawa Goggo ta nufi gidan.


A falon kasa ta samesu duka suna karyawa. Da gudu Sumayya tayi mata oyoyo ta fara surutu, Saddiku da yake zaune a dining table ya juyo ya gaisheta. Ta karasa ta zauna a kusa da Goggo a dai-dai lokacin da Yusra ta mike ta shige kichin. Cikin girmamawa suka gaisa da Goggo da sauran yaran, ta mikawa Rukayya robar sandwich din tana fadin


'Ga abincin break dinku Rukayya.'


Ta mikawa Goggo daya robar. Rukayya ta dauki robar ta shige kicin. A daidai lokacin Goggo ta dubeta tace


'To nifa yau bako zai yi halinsa, sai dai nace Allah yaji kan wannan yarinyar. Wadannan yaran kuma dama tare na ganku sai dai nace Allah ya zaunar daku lafiya.’


Tace


'Amin Goggo, mun gode.’


'Abban yace min yau zaki dawo dakinki ko?’


Cikin sanyin murya tace


'Eh, sai na dawo daga aiki.’


'To a dawo lafiya. Ni dai nan da awa daya ma na tafi in sha Allah.'


‘'To Goggo mun gode, Allah ya kara lafiya.’


Ta kawo kudi naira dubu goma ta ajiyewa Goggo tana fadin


'Kya yi tsaraba a hanya Goggo, a gaida mutanen gidan.


Nan da nan Goggo ta fara godiya tana saka mata albarka. Ta mike ta nufi kofa bayan tayiwa yaran sallama tana tuna musu gara su fito kada su makara.


Ta kofar kicin Yusra ta fita tsakar gida don haka babu wanda ya san tana waje. Dai-dai lokacin da Aishan ta kusa karasawa bakin kofar dai-dai lokacin Yusra ta shigo falon. Iya karfinta ta bangaji Aisha da kafada har saida Aishan ta danyi baya. Ta kalleta sama da kasa ta wuce. Cikin sanyin jiki itama ta fice daga falon, ta tsaya a bakin gata ta hadiye malolon bakin cikin da ya tokare mata makogoro ta share kwallar takaicin da ta gangaro daga idonta; ya ma za ayi ta zauna da Yusra?


Babu wanda ya ga abinda ya faru sai Saddiku wanda yake kan dining table. Ya jijjiga kai ya cigaba da cin abincinsa, yana mamakin yanda Yusra ta zama marar kunya domin shi kansa ba kyale shi tayi ba tun lokacin da ya dawo daga makaranta.


Kafin Aishan ta fice daga gate din Abba ya sauko daga sama ya yiwa yaran magana su fita a kai su makaranta. Bayan sun fice ya gaisa da Goggo yana tambayarta ita da wa ya jiyo hirarsu. Tace


'Ni da diyata ne Aisha, ka ga abun arzikin ma da ta kawo min.’


Ta nuna masa kudin da Aishan ta bata sannan ta cigaba


'Tace idan ta dawo daga aiki ai zata dawo dakinta. Sai ayi ta hakuri, Allah ya ji kan mahaifiyarsu kuma Allah ya baku hakurin rashi gaba daya.’


Ya amsa sannan ya mike ya koma sama.


Wannan maganar da Goggo ta sanar da shi ta kara masa nutsuwa, duk da daman ya san Aisha ba zata ki bin umarninsa ba. Sai da ya jira Goggo ta shiga mota Malam Ali ya ja su ita da Saddiku sannan shima yayiwa Jummai sallama bayan ya sanar da ita ta sake share dakin da aka gyarawa Aisha sannan ya fice.


—------


Haka Aisha ta wuni a wajen aiki zuciyarta babu dadi, duk wanda ya kalleta sai ya tambaya ko bata da lafiya. Abu daya take jaddadawa kanta shine ba zata zauna da Yusra ba, idan Abba ya matsa mata tabbas zata iya hakura da aurensa.


Ana tashi daga aikin ta kama hanya ta koma gidanta, bata da niyyar barin gidan don haka ta cigaba da harkokinta kamar yanda ta saba.


Wajen karfe uku lokacin da su Rukayya zasu tafi islamiyya ta ja Ummi da Sumayya suka shiga gidan Aishan. A take Nana ta koma gida ta gayawa Yusra wadda tayi alkawarin idan suka dawo sai ta koyawa Rukayya hankali don ba zata barta ta dinga karya dokar Mommy ba ko da bayan ran Mommy din ne.


Suna shiga bayan sun gaisheta Rukayya tace


'Anti Abba yace yau zaki dawo gidanmu fa ko an fasa ne?’


Ta kalleta tana murmushi, bata san amsar da zata bata ba don haka tace


'Ba'a fasa ba amma zan dan fita tukunna sai dai kafin ku dawo na dawo.’


'To Anti.'


Ta aika Rukayya kicin ta dauko musu biskit ta bawa Ummi da Sumayya suka yi mata sallama a kan idan sun dawo zasu sameta a gidansu suka fice.
Ta bi bayansu da kallo cike tsananin damuwa; da ace su ukun nan ne kadai yaran

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login