Showing 108001 words to 111000 words out of 166068 words
da Umman su Muhammad a dai-dai lokacin da Shukuriyya ta fito dauke da tray ta doro waina da kili_kuli.
Nan da nan Umman ta karba ta koma kicin din ta juyo a roba ta fito mata dashi sai dai kafin ta zo har ta ja mota ta tafi. Ta dubi Yaya Bello da yake tsaye a bakin kofar falon tace
‘Laa! Kuma sai ka barta ta tafi bata karbi wainar ba Alhaji ai abun marmari ne kuma mutum ya gani.’
Yayi murmushi
‘Bata so karba ba. Ba zuwa tayi muyi magana ba zuwa tayi ta yi min rashin kunya kuma bata isa ba. Ina jin ya gaya mata na hana ya kai yara waje karatu shine ta zo kuma bata sami yanda take so ba, ko baki kula da yanda take magana bane?’
‘A’a ina kula sai dai da yake ni tunda ya kara aure haka muke da ita, da kyar take kulani don haka ni bata ma damuna shi yasa yanzun ma na zata nice bata son gani ashe kai din ma ka shiga gonarta.’
Ya juyo ya dawo cikin falon ta biyoshi a baya tana mita
‘To kai kuwa Baba ka kyalesu mana, tunda yana da kudin.’
Ya zauna sannan ya bata amsa
‘Ba zan kyalesu ba! Yusufa ai danuwana ne kuma idan yaransa suka lalace dole abun ya shafi zuri’armu. Da ma wasu nutsattsun yara ne da sai ace, musamman shi Saddikun. Bari su gama a nan din tukunna muga hankalinsu.’
‘Ai shikenan, Allah ya bada sa’a.’
--------
Tunda ta dawo daga gidan Yaya Bello Abba yaga yanda take cika tana batsewa ya san bata sami yanda take so ba, don haka ya kawar da kai kamar bai ganta ba. Haka ta karasa wunin tana ta faman kunci, tunaninta ma yanda zata gayawa yaran musamman Saddiku wanda yake ta faman murna yana gayawa abokansa wadanda yanzu yawanci suna level 2 cewa shi Dubai zai tafi kuma ba zasu rigashi gama degree ba.
Sai dai shi Abban yaji dadin wannan hukuncin kawai dai yana mamakin yanda tafi shakkar Yaya Bello fiye da shi.
Bayan Sallar isha’i ne suna zaune a falon sama har yaran suna hirarsu, Yusra ce ta shigo da sallama daga falon kasa. Kujerar da take kusa da ta Abban ta zauna, bata jima da zama ba tace
‘Abba wai yaushe zamu yi jarrabawar ne? Wadda kace zamuyi don samun admission a Dubai din.’
Ya kalleta
‘Oh, Mommy bata gaya muku ba ko? Ai an fasa zuwa Dubai din, na yanke hukunci da ke da Yayan naki kuyi first degree a nan BUK in ya so idan kun gama sai ku tafi duka kasar da kuke so don yin second degree. So yanzu idan result ya fito BUK za a nema, daman kin ga ita kuka cike a JAMB form ko?’
Nan take idonta ya ciko da kwalla, Mommy wadda take zaune a kusa da shi ta tashi ta shige dakinta. Yusran ta zumburo baki
‘Abba! Haba Abba, don Allah Abba ka bari mu tafi.’
‘An gama magana Yusra, nan din ma degree zakuyi irin na can so babu wannan zancen. Amma nayi miki alkawarin idan dai kika fita da first class to in Sha Allahu ko ban biya miki ba zan nemar miki scholarahip ki je UK ma kiyi masters kinga na can ya fi daraja.’
Ta share zafafan hawayen da suka gangaro kan fuskarta, ta tashi ta shige dakinsu na sama ba tare da tace masa komai ba. Ya bi bayanta da kallo yana jijjiga kai, ya san abun da haushi amma bai ji dadin yanda tayi masa hakan ba sai dai ya san wannan din dabi’ar uwarsu ce. Ya cigaba da hirarsa da suaran yaran, sai daga baya suka tashi kowa ya tafi makwancinsa.
Tun kafin gari ya waye Yusra ta sanar da Saddiku abinda Abba yace, nan da nan ya rikice. Ya sami Mommy a dakinta ya sa mata kuka; yana tsugune a gabanta Yusra ta shigo ta zauna a gefen gado kusa da Mommy din. Ta kalli Saddikun ta kawar da kai, tace
‘Mommy don Allah ki yiwa Abban magana mana, wai me ma yasa zai canza magana bayan an gama maganar nan?’
Taja tsaki ta kawar da kai
‘Wai ubanku ne Bello yace ba zaku je Dubai din ba sai dai BUK, nima babu yanda banyi dasu ba don jiya ma da safe da na fita gidan Bellon naje. Yace wai a barku saboda tarbiyya, ko kuma tsabar bakin ciki ne oho! Tunda yaransa BUK sukeyi to dan kowa ma yayi BUK.’
Saddiku ya dubi Mommy yace
‘Wallahi Mommy na dade da sanin mutumin nan dan bakin ciki ne, ina ruwansa tunda ba da kudinsa za a je ba?’
Yusra tace
‘Uhm! Yanzu ai sai ya zuba ruwa a kasa ya sha tunda zamu zauna muyi BUK kamar yaransa. Mtsewww! Na tsani dan sa ido wallahi.’
Saddiku ya dora hannuwansa a kan gwiwar Mommy yace
‘To yanzu Mommy babu abinda zaki iya yi a kai?’
‘Da zan iya da tuni nayi, ka san shi da bakin taurin kai.’
Ya dafa kansa da hannuwansa biyu
‘Amma gaskiya ya cuceni Mommy, duk friends dina na gama gaya musu zan tafi Dubai amma gayen nan ya sa aka fasa. Allah ya isa wallahi.’
Tace
‘Ka barni da shi, zan yi maganinsa kwanannan.’
Nan suka gama hirarrakinsu suna ta zagin Yaya Bello. Daga baya suka sanar da Mommy cewa idan hakane ta yiwa Abban magana su in ba za a kai su Dubai din ba to sun fi son Maryam Abacha University. Duk da bata san yanda zai dauki wannan zabin nasu ba amma tayi musu alkawarin zata yi iya yinta taga a kalla sun sami nan domin ko babu komai dai kada suyi Jami'ar da ‘yayan Bellon suke yi wato BUK.
__
Kwanci tashi har an fara yiwa azumi lissafin abinda bai fi wata daya ba. Zuwa yanzu duk wanda ya ga Aisha ya san tana da damuwa, sai dai duk yanda ‘yan uwanta suke so su rabata da gidan Yusuf ta ki yarda. Suna nan dai ita da Amira, duk da bata rasa komai ba amma rashin ganin Abban yana damunta. Ko a hanya bata ganinsa, kusan kamar ma dai suna rayuwa a mabanbanta duniyoyi.
Bata taba fasa addu’a da sadaka ba, ga addu’ar karya sihiri wadda kullum sai tayi kuma Hajiya ma sai ta yi ta aiko mata da ruwan. Tun tana lissafin kwanaki har ta gaji ta daina; abinda ta rike kawai shine Allah ya amsa addu’arta lokaci kawai ake jira.
………..
Ranar Juma’a ce kuma da yake ta kama ranar hutun aiki Zuwaira, Zainab da Aisha da Zahida gaba daya su da yaransu sun hallara a gidan Hajiya. Don haka sai kaiwa da kawowa akeyi, Farha da Abdallah wanda yake shirin zana common entrance suma suna nan a cikin dangi. Mijin Zahida ne ya bawa Hajiya kujerar Umra wadda zasu tafi cikin azumi don haka kowa murna yakeyi.
Can wajen karfe biyar na yamma lokacin kowa ya fara shirin tafiya Yaya Abubakar shima ya shigo tare da babban yaronsa Abulkhairi. Bayan sun gaisa ya dubi Anti Uwani yace
‘Anti Uwani family meeting kuke yi ne aka wareni?’
Tayi dariya tace
‘A’a wa ya isa ya wareka? Nan da ka gansu duk dadin baki suka zo su yiwa ‘yar uwata zata tafi Umra su samu ta tafi dasu ni kuwa ina kallonsu da ni zata duk a Nigeria zamu barsu.’
Yayi dariya yace
‘Ai kuwa a Nigeria zaku barsu Anti Uwani don kema da taki kujerar nazo.’
Zahida tayi caraf tace
‘Allah Yaya da gaske.’
Ya daga kai
‘In Sha Allah na ma gama biyan kudin sai su tafi tare, nima don dai ban dade da komawa sabon office bane da dani za a.’
Nan take Zahida ta zabga guda, kafin ta dire Yaya Zainab ta harareta tace
‘To sarkin bidi’a, da an yi motsi sai ki kama wani nanannen hanciki.’
Suka kyalkyale da dariya.
Nan suka hau sabuwar murna gaba daya. Hajiya ma sai tafi Anti Uwanin murna domin sai da ta matse kwalla saboda jin dadi. Haka ta dinga sakawa Abubakar albarka tana addu’a Allah ya kara masa arziki.
Haka Anti Uwani ma sai ta rasa inda zata saka ranta don murna, tayi ta sa musu albarka tana musu addu’a. Ta matsa kusa da Hajiya ta dafa ta tace
‘Yaya, Yaya Kinga dana ko? Na rasa bakin godiya Yaya. Tunda kika haihu ban taba kukan rashin haihuwa ba, kullum godewa Allah nake da bai bari na sha wahalar goyon ciki ba kika sha mana wahalar ke kadai kika haifo min ‘yaya. Gashi nan kinyi shuka sai girbar alkhairi nakeyi hankalina kwance.’
Hajiya tayi dariya tace
‘Naga alama kam to ina binki bashi kenan na wahalar nakuda.’
Suka sa dariya gaba daya
‘In Sha Allah idan naje sai nayi dawafi sannan nayi miki addu’a Yaya; yanda kuke so na Allah ya soku fiye da haka kuma Allah ya karramaku fiye da yanda kuke karramin.’
Ta fara share kwalla, Zahida ta dafa bayanta yayinda Hajiya tace
‘To ga ‘yarki nan baure sarkin kuka zata tayaki muna murna zaku saka mu kuka.’
Suka sa dariya gaba daya.
Ana idar da sallar Magriba duk suka watse suka bar Aisha da Amira wadanda sai bayan sallar isha’i zasu tafi.
A nan falon Hajiya suka ci abinci suna ta hirarsu, sai da aka idar da sallar isha’i suka tashi tafiya. Lokacin Farha tayi bacci don haka Abdallah da Anti Uwani suka rakosu farfajiyar gidan.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
34
Babu yanda Zahra ta iya, tana ji tana gani aka fasa kai yaran Dubai karatu. Ta dai samu ta karfin tsiya ta takura Abban ya amince zai saka su a Maryam Abacha University. Yayi magana da Yaya Bello shima ya amince da haka, tunda dama abinda yake gaya masa shine ya kasance yaronka yana kwana a gida har sai ka ga yanayin fahimtarsa a rayuwa tukunna. Don haka nan da nan aka fara shirin shiga MAUN.
Sai dai kawai ta yiwa kanta alkawarin sai ta kai Yaya Bello wajen boka don ta fuskanci tunda yanzu dan uwansa ya kara kusanci da shi to lallai hukuncinta zai ci gaba da cin karo da nasa. Yanda take jin yanzu ta sami Abba a hannunta bata jin zata sake bari ya subuce mata, duk wata hanya da zata bi sai ta bi don ta tabbatar babu wanda ya sha gabanta a wajen Abba. Domin a yanzu ma gani takeyi kamar Abban yana bawa Yaya Bello wasu kudade ne.
__
Tun lokacin da ta gane aikin boka yayi tasiri take kula da motsin Aisha, musamman ta sami mai aikin gidan commissioner wadda dattijuwa ce take sa mata ido tana kular mata da motsin Aishan. Tana so ta san lokacin da Aishan zata bar gidan. Zuwa yanzu kusan watanni goma an sanar da ita Aishan tana na; ta kasa gane wanne irin naci ne wannan. Miji baya kula ki amma ace ba zaki bar masa gida ba? Ta dai bata daga nan zuwa babbar Sallah ta san in Sha Allahu zuwa lokacin ko bata gaji ba to tabbas kudin hayar gidan zai kare.
Maganar boka ta tuno da ya ja layi guda biyu yace mata tafiyar Aisha da Yusuf mai tsawo ce; yanzu haka tsawon kenan kuma in Sha Allahu sai ta ga karshen wannan tafiyar.
__
Kwanci tashi har azumi ya karaso; duk wani abu da Aisha take bukata na azumi haka ta dauki Amira suka je suka siya, kuma da yake Yaya Abubakar ya san halin da take ciki ranar da aka ga watan azumi sai ga sako ya aiko mata. Buhun shinkafa, dankalin bature, doya, kifi da suga haka aka kawo mata.
Ranar goma sha takwas ga watan azumi jirgin su Hajiya zai tashi tare da Aisha. Ranar sha biyar ga wata ta shirya suka tafi gidan Hajiya ita da Amira; bayan ta kwashe duk wani abu mai amfani nata saboda bata barwa kowa ajiyar gidan ba. Sai da ta kulle ko ina tayi addu’a sannan suka fito, har zata saka kwado a gate din ta tuna duk wanda ya zo yaga kwado daga waje ya san babu kowa a gidan don haka sai ta fasa saka kwadon kawai ta kulle da mukullin. Babu wanda take harka da su a kan layin don haka bata bukatar yiwa kowa sallama, ta ja motarta suka bar unguwar.
Ranar da aka dauki azumi na sha takwas da safe Aisha da kanta ta dauki Abdallah da Farha ta kaisu gidan Umma, kakarsu ta wajen Uba. Ba karamin dadi Umma taji ba don dama sun dade basu je mata kwana ba. Sukayi sallama a kan sai bayan Sallah idan ta dawo zata zo ta daukesu. Da yamma jirginsu ya tashi sai kasa mai tsarki, tana tsakiyar Hajiyanta da Anti Uwani.
____
Ranar da aka kai azumi na ashirin da biyar Baba Salamatu wato mai aikin gidan commissioner ta shigo gidan Zahra. Lokacin yara duk sun tafi masallaci sallar asham sai Jummai wadda take aiyukanta a kichin yayinda Mommy din take hutawa a falon sama. Bayan sun gaisa da Jummai ta hau saman ta kirawo Mommy.
Nan da nan ta sauko saboda ta san akwai labari tunda Sala ta zo. Bayan sun gaisa tace
‘Hajiya ina ga kanwarki dai ta bar gidan na fa.’
Ta ji dadi sosai a ranta, amma sai ta waske tace
‘Allah Sala, ko dai unguwa ta tafi.’
‘Kai gaskiya ba unguwa ta tafi ba Hajiya. Don Kinga fa tun azumi na kusan goma na daina ganin motsinta, almajiran ma da suke zama kofar gidan jiya sun tabbatar min bata nan don farkon azumi kullum da magriba sai ta basu sadaka amma yanzu an kwana biyu basu ga motsi a gidan ba.’
Ta dan yatsina fuska
‘Allah sarki, to na gode Salamatu. Dan jirani ina zuwa.’
Ta karasa tana mikewa tsaye, ta haye sama ta barta a nan.
Jimawa kadan ta sauko ta zauna a inda ta tashi, ta mikawa Salamatu naira dubu tana fadin
‘Ga abun sadaka kya sayi ko dan sabulu.’
Nan da nan ta washe baki da addu’a tana ta faman godiya, tayi mata sallama ta fice.
……….
Cikin walwala suka tashi ranar idi, nan da nan aka shirya yara kowa ya sha kwallaiya. Karfe takwas saura Abba ya fito ya zuba su a mota suka wuce masallacin idi.
Kafin su dawo an sauke tuwon Sallah.
Sai da kowa yaci ya koshi sannan Mommy ta ware na makota, Jummai ta dauka suka tafi tare da Nana da Ummi. Gidaje uku suka kai, gidan commissioner ne na karshe kuma shine cikon na hudun. Bayan sun gaisa da matarsa wato Dr. Maimuna wadda ake kira Mama suka bayar da tuwon, aka juye aka basu kwanukan da kuma tukwici.
Salamatu ta dauko kwanukan ta biyosu suna ‘yar hira da Jummai kamar zata yi mata rakiya. Kasa-kasa suke yin maganar don haka Ummi da Nana da suka wuce gaba basa jinsu. Salamatu tace
‘Wai ni Jummalo amaryar gidanku auren ya mutu ne?’
Jummai tace
‘Babu mamaki fa, don na manta rabon da maigidan ma yayi rabon kwana da ita; ko ba ayi shekara ba an kusa. Ina ga sakinta yayi ko kuma dai wata matsala aka samu.’
‘Gaakiya da alama, tunda kin ga ta bar gidan fa tun farkon azumi. Yanzu haka dai auren ya kare. To ko Uwar dakinki ce ta kar auren ne?’
Ta dan zaro ido
‘Ke salamatu! To ni ban sani ba in kin shiga gidan kya tambayeta.’
Ta tabe baki
‘Au na manta ke fa ba a sukan uwar Saddiku a gabanki ko. To ku gaida gida.’
Tayi musu sallama suka wuce.
Tun daga wannan lokacin gulma ta fara yawo a unguwar cewa Abba ya saki Aisha.
Bayan da su Nana suka dawo ne kuma Malam Ali ya kwashesu da tuwon gidan Hajiya suka tafi kai mata. Mommy ta riga ta gayawa Yusra cewa idan Hajiya ta tambaya Ina abincin gidan Aisha tace tare suka yi don haka suna ajiye tuwon ma kafin a tambaya Yusra ta cewa Hajiyan
‘Tare sukayi tuwon da Mommy da Anti Aishan.’
Ta yashe baki
‘Ai gara hakan ya fi.’
Bata jin dadi sosai saboda ciwon diabetes wanda tun goman karshe ya tasar mata saboda an hanata azumi tace sai tayi, don haka ta san ba cin tuwon zata yi ba. Nan ta bawa Yusra umarni ta kaiwa Anisa ta ajiye a kicin. Ta gyara kwanciyarta ta kara muryar rediyonta yayinda su kuma yaran suka fito tsakar gida suka cigaba da hidimominsu.
_
Bayan Sallah da sati daya su Aisha suka dawo Nigeria; tayi sallah kuma tayi addu’a a kan Allah ya karya wannan kulli da aka yi tsakaninta da mijinta, sannan kuma ta roki Allah ya saka mata ko ma waye yake mata wannan zaluncin kuma Allah ya toni asirin me yi mata hakan.
Tabbas ta sami natsuwa kuma ta dawo da wani sabon karsashi na zaman jiran lokacin da wannan asirin zai karye, in Sha Allahu ko zata rabu da Yusuf to ba yanzu ba sai dai idan ya dawo hayyacinsa yace ta tafi to tabbas a lokacin zata tafi.
Kwanansu biyar da dawowa Aisha tana hutawa a gidan Hajiya; an dauko su Abdallah duka ta basu tsarabarsu har sun je gidan ‘yanuwanta yawon zumunci.
Suna zaune a rumfar da take farfajiyar gidan suna hirarrakinsu, Hajiya ce a kashingide a kan tabarma yayinda Anti Uwani ke zaune a kusa da ita. Ranar laraba ce don haka Farha da Abdallah suna islamiyya. Aisha ta fito daga cikin gidan bayan tayi musu sannu da hutawa ta zauna a kusa da Anti Uwani. Bata dade da zama ba ta dubi Hajiya tace
‘Hajiya gobe ni da su Abdallah zamu je gidan Yaya Zainab, daga nan zan dauko ‘yata ranar Juma’a sai mu koma gida.’
Sai da Hajiyan ta tashi zaune sannan ta bata amsa
‘To Allah ya kaimu goben. Baku yi magana da Yayanki bane?’
‘Tun last week dai da yazo, ranar da muka je gidansa har muka taho