Showing 15001 words to 18000 words out of 166068 words
shiru na dan lokaci; to me ma zata boye musu? Ai gara ma ta gaya musu ubansu zai yi aure su san zaman da zasuyi da shi. Ko babu komai Yusra dama ta zama abokiyar shawararta tunda ta ga tunaninsu ya zo daya. Da dai Rukayya ce da sai ta boye mata don wannan sak halin ubanta ta yiwo, ko kuma halin Yaya Murja; don wani lokacin tabbas tunaninta irin na Yaya Murja ne.
Ta danyi gyaran murya wanda ya janyo hankalin Yusra ta dubeta, ta kawar da kai tace
‘Yusra Abbanku aure zai yi.’
A dan razane tace
‘Aure Mommy!’
‘Um, ya sami wata bazawara wai mai yara biyu shine zai aureta. Next week ma za a daura auren.’
Ta kara zaro ido
‘Next week Mommy? To ya akayi ba wanda ya sani.’
‘Hmm! Munafurci mana irin na da namiji. Ko nima ban sani ba sai jiyan yake gaya min wai asabar mai zuwa za a daura masa aure saboda tsabar wulakanci.’
Ta fara kada kai
‘Hmmmn! Amma gaskiya bazawarar na ta wanki kan Abba. Tab! To yanzu kuma ina yace zai sakata tunda bai bamu notice ba ai ba lallai mu iya kwashe kayan dakin kasa zuwa next week ba.’
‘Wai ya kama hayar wannan gidan na kusa da gidan su Mashkur, a nan zata zauna.’
Mamakin Yusra ya karu, ta ce
‘Kan bala’i! Har ya kama hayar gida amma sai jiya kika sani. Lallai abun babba ne Mommy.’
A daidai nan Sadik ya turo kofar ya shigo, ya tsaya a bayan kofar yana sauraron karshen zancen Yusra. Ya dubi Mommy yace
‘Menen babban abun kuma?’
Kafin mommy tace wani abu Yusra tace
‘Abba ne zai yaure next week ma za a daura auren.’
Shima ya zaro ido, ya karasa ya zauna kusa da Yusra yana fadin
‘Lallai, amma ko labari.’
Yusra tace
‘To Mommyn ma sai jiya ya gaya mata ai.’
Yayi 'yar gajeriyar dariya yace
‘Lallai, ashe akwai biki kenan.’
Yusra ta balla masa harara, ya dubi Mommy yace
‘Kin san fa irin auren nasa, wancan karon haka ya tashi mutane a tsaye kuma ya zo ya fasa. Ki sa masa ido kawai kiga gudun ruwansa.’
Mommy tace
‘Hmmm!’
Sukayi shiru na dan lokaci, Sadik ya karya shirun yace
‘Mommy jiya fa kince zaki bani dari biyar na saka data, ita na zo tuni.’
‘Ga jakata can ka dauka.’
Ta fada tana nuna masa jakarta wadda take kan mudubi.
Nan da nan ya mike ya dauki kudin ya fice. Ya bar su Mommy tana ta kara gayawa Yusra maganganun da zasu sa taga kamar Abba wulakanci yake so yayi mata shi ya sa zai kara aure.
Shi kuwa Sadik ficewa yayi yana mamaki, duk da ya san auren ba wani tasiri zai yi ba. Duk da haka yanzu kam ya san shi dai babu wata matar da zata zo tace zata bata masa rai ko tayiwa Mommy ba daidai ba; tabbas zai saita yarinya komai girmanta. Musamman da yake shi din dogo ne kuma yana da zati kamar mahaifinsa, don haka yake jin kansa komai ma zai iya.
……
Haka ta wuni ranar ba tare da walwala ba, shi kansa Abban Sadik din ya gane halin da take ciki. Sai dai da yake ya riga ya san tana da kishi kuma ya san yayi mata laifi sai ya kau da kansa yana fatan nan da wani dan lokaci zata huce.
Wajen karfe uku na yamma yara suka tafi islamiyya, ana yin sallar la’asar kuma Abbansu ya shirya zai fita don haka itama ta shirya tace ya sauketa a gidan kanwarta Suwaiba.
Saida ta ci kukanta ta koshi Suwaiba na bata hakuri sannan ta zaro katin daga jakarta ta mikawa Suwaiban tace
‘Tsabar wulakanci sai jiya na sani kuma bayan da fari ce min yayi basu ma gama daidaitawa ba.’
Ta dauki katin tana dubawa tana tabe baki, tace
‘Hmm! Maza ai sai hakuri lamarinsu, ga munfuncin tsiya.’
‘Wallahi zan yi maganinsu da shi da ita bazawarar tasa, zan ga shegiyar da zata zo gidana tace zata zauna da mijina lafiya.’
Haka suka dauki lokaci Suwaiba tana bata hakuri har ta dan sami natsuwa, ba jimawa kuma ta mike tana fadin
‘Bari kiga na tafi kafin ya shanya ni har yara su dawo daga islamiyya, na san yanzu haka wajenta ya tafi.’
Suwaiba ta mike tana murmushi
‘Ah! Yaya Zahra, shikenan kuma babu inda zai je sai wajenta.’
Tayi kwafa kawai ta nufo kofa, Suwaiban tayi mata rakiya sukayi sallama ta kamo hanyar gida. Sai da ta iso gida sannan ta kirawo shi tace masa ta koma gida ba sai yaje daukanta ba.
Babu kowa a gidan sai Jummai da take karasa wanke wanke, ta bata abinda zata dora mata na abincin dare ta haye sama.
Tana zama a daki ko mayafi bata cire ba ta kirawo Mallam ta sanar da shi aure ma saura kwana bakwai, tayi masa bayanin uzurin da Yusuf din ya bata. Bayan ya gama sauraronta yace
‘Ikon Allah, tabbas akwai wata a kasa don babu mamaki ba haka suka barshi ba. Yanzu haka akwai aikin da suka yi masa don ayi gaggawar daura auren. Amman kada ki damu, da kaina zan fara aikinki wanda mukayi magana yau din nan. Sannan kuma idan ban samu na gama ba to akwai abinda zan baki ki daga carpet ki saka ta daidai inda zata tsallaka idan an kawo miki ita, in dai ta tsallaka to da izinin Allah rana tana fitowa zasu fito tare ta bar gidan kenan har abada.’
Sai da tayi ajiyar zuciya tana murmushi saboda jin dadin wannan bayanin na Malam Hatimu mai almajirai, tace
‘Malam ka san fa da mutane za su zo,dole wasu ma zasu tsallaka ta wajen da ta bi.’
‘Kada ki damu ai lakanin da nasaba zai zo, ita kadai zai yi aiki a kanta. Ke dai ki turo min sunanta da na mahaifinta, idan da hali ma harda na kakanta kafin ranar Alhamis an gama aiki. In ya so sai ki aiko ko kizo ranar Juma’a ki karba. Ai tunda sun zo da fitna sai an tashi tsaye.’
‘Hakane Malam, in sha Allah zuwa gobe ma zan turo maka sunan nata. Sai kuma maganar abun sadaka ko?’
‘Ai kwarai kuwa, Zaki turo kamar naira dubu sittin don sai an sayi rago ma an yanka anyi sadaka da naman, idan aiki yayi sai ki cika dubu hamsin.’
Sukayi sallama tana ta yiwa Mallam godiya.
Tana ajiyewa ta kirawo Hajiya Amina ta bata labarin halin da ake ciki, ta sanar da ita akwai kudin da Abban yace zai bata idan ya bata zata rakata sayayya kuma ranar Juma’a zata rakata Gaya wajen Malam Hatimu. Sukayi sallama suka ajiye wayar.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
8
A zaune suke a garejin gidan Hajiya inda dama nan suka saba zama in ya zo zance, hirarsu suke cikin walwala. Ya dubeta sukayiwa juna murmushi, yace
‘Ni na ishi abokai da zancen zanyi aure amma ke ko ‘yar rawar kan nan da amare sukeyi ba kya yi.’
Ta kyalkyale da dariya
‘Kuma rawar kan me zanyi sai kace wata karamar yarinya?’
Ya kama haba
‘Wai ke ina zaki kai son girma ne? Har yanzu fa ashirin da ake kirga shekarunki.’
‘Kuma dai ni ba yariya bace ai.’
Yayi dariya
‘To yanzu dai me kika shirya a bikin, me kike bukata?’
‘Babu komai, duk na gama wani shiri.’
‘Kinyi shirin zama amaryar Yusuf?’
Tayi dariya, suka hada ido.
Tayi sauri ta sunkuyar da kai saboda yanda yake kallonta. Suka yi shiru ba tare da ta amsa ba, ya katse shirun
‘Sai fa kin bani amsa in ba haka ba sai dai muyi ta zama a nan.’
Murmushi kawai tayi ta sake sunkuyar da kai, don haka shima yayi shiru ya zuba mata idanu. Ta dago suka hada ido ta kawar da kanta tana murmushi tana ta juya wayarta wadda take hannunta.
‘Aisha.’
Ya kirawo sunanta a hankali.
Ta dago ta kalleshi ba tare da ta amsa ba, yace
‘Kina so na kuwa Aisha.’
Ya sake zuba mata ido har tana jin motsin kwayar idonsa a kan fuskarta, kallon da yake mata ya sa ta tabbatar sai ta amsa tambayar. Ta bude baki a hankali tana murmushi tace
‘Um.’
Yayi dariya yace
‘Ban ji ba.’
Ta dago ido itama tana murmushi tace
‘Saboda tsokana ko?’
‘To kin shirya zama amaryar Yusuf?’
‘Na shirya.’
Yayi murmushin da yake nuna har cikin ransa ya ji dadin kalamanta.
Suka cigaba da hirar tasu duk da yawanci shiru sukeyi shi yayi ta kallonta ita kuma tayi ta satar kallonsa suna yiwa juna murmushi.
Shi Yusuf ba mutum ne mai yawan hayaniya ba ita ma kuma Aisha bata da surutu kuma ga miskilanci, don haka sai suyita kallon kallo suna musayar murmushi.
Jimawa kadan ya mike yace
‘Bari na tafi kada yayarki ta rufe min kofa.’
Tayi dare tace
‘Ashe dai ana tsoronmu.’
‘Ai dole ne, ku din hukuma ne sai lallashi.’
Ya fara tafiya suka jera zuwa waje don tayi masa rakiya, suna cikin tafiya ya bude wayarsa ya dubeta yace
‘Gaya min lambar account dinki mana na saka miki ko naira dari haka kya sayi goggoro.’
Tayi dariya, ta karanta masa account number din da sunan bankin.
Suna karasowa bakin motarsa taji wayarta tayi kara, tana dubawa ta bude baki tana kallonsa saboda sakon da ta gani. Ya gyara zamansa a mota yayinda tace
‘Yallabai kudin nan ai yayi yawa sai kace goggoron gwal zan siya?’
‘To ki saya harda janbaki.’
Tayi dariya
‘Nagode Allah ya kara arziki.’
‘Amin amaryar Yusuf.’
‘Ka bari dai a daura.’
Sukayi sallama ya kama hanya, yana tuki yana murmushi.
Kafin ya tambayeta maganar abinda take bukata wajen biki ya riga ya ya ke ko nawa ta nema iya dubu dari zai bata, amma sai ta ma ki yarda ayi zance. Shiyasa ya tura mata da dubu dari biyu, ko babu komai ta cancanci hakan don yana sonta sosai.
Dabi’unta suna burgeshi gata da kunya, shi kuma a rayuwarsa yana son mace mai kunya.
Yana tuki yana ta tunani har saida ya kusa zuwa gidan Suwaiba sannan ya tuna Zahra tayi masa message cewa ta koma gida, yayi murmushi ya karkata kan motar ya dau hanyar gida.
------
Haka aka cigaba da shirye shiryen biki; duk wani abu da ya kamata a yiwa amarya ‘yan uwanta sun tsaya a kanta anyi. Duk da yaron cikin da Zahida take dauke da shi haka ta dinga rakata wajen gyaran jiki, suka je saloon aka rangada mata kitso a dogon gashinta. Duk lokacin da tayi kamar zata shiga damuwa sai su taru suyita lallabarta.
Su kuwa Abdallah da Farha murna ma sukeyi za ayi wa Mamansu biki, Abdallah ne kawai ya kan dan nuna damuwa idan yaji ana Mamansa wani gidan zata koma. Shima a hankali Hajiya ta dinga kwantar masa da hankali don haka kowa shirin biki kawai yakeyi a gidan.
Zuwa ranar Alhamis amarya ta dau kyalli, ranar Alhamis din da safe kannen Hajiya tare da matar Baffa suka hadu da su Zainab suka tafi kafi. Tsaf suka gyare gidan amarya suka kunna turaren wuta, gida ya dumame da kamshi. Ko ina yayi fes, dakuna uku da falo ga kitchen sannan kuma da fili inda za a iya ajiye mota daya.
Ba a ce dasu su shiga gidan Uwargida ba don haka ma da suka ji yunwa sai Zainab ta fita ta siyo musu abinci, suka ci suka karasa aikinsu suka koma gida.
……..
Ya riga ya gayawa ‘yan uwansa ba za ayi taro ba don haka mata basu zo gidan ba sai wadanda suke zuwa gidan Hajiyarsu Allah ya sanya alkhairi. Kannen Hajiya mutum biyu da kuma kanwar mahaifinsa tare da matar Yayansa Bello sune zasu je daukan amarya kuma ya riga ya sanar dasu idan sun daukota kai tsaye su wuce da ita gidanta, idan ya zo da kansa zai kaita wajen Zahran.
Sai da ya gama duk wani shiri nasa na tarbar bakinsa 'yan daurin aure sannan ya kama hanyar gida, lokacin dare yayi don har yara sunyi bacci.
Haka Zahra ta tare shi babu yabo babu fallasa don kawo yanzu ta kasa danne kishinta wanda bakin ciki ne yake kara mata shi; musamman idan taga yanda yake ta rawar kai a kan auren. Bayan ta ajiye masa abincin dare ta dubeshi tace
‘Bari naje na kwanta don gobe mu da hidima saboda baki duk da dai ba taro za ayi ba.’
Tambayar ta bashi mamaki ya amsa yana kallonta
‘Hidimar me kuma? Ai ba wani taro don su Hajiya ma na gaya musu ba sai mata sun zo ba daga baya sa zo.’
Ta dan faki idonsa ta gatsina baki wanda tayi saurin biyewa da murmushin yake
‘Eh ai nima ka gaya min, amma ai naga idan aka dauko amarya wajen uwargida ake fara kaita ayi nasiha kafin a kaita dakin miji, shi yasa zamu gyara gidan kuma na tanaji abun tukuici.’
‘Oh, wanna ai nace ba sai sun kawota ba daga baya na kawota kawai.’
Ta kalleshi yayinda ya cika baki da lomar abinci yana kallon wayar hannunsa.
Tanada nata tanadin da tayiwa wannan zuwan na amarya amma zai rusa mata aiki, gaskiya ba zata yarda ba. Idan shi ya kawota ba lallai tayi abunta a sirri ba sannan kuma ba lallai ya kawota a daren ba; ita kuwa a wannan juma’ar take so ayi ta ta kare. Ta danyi gyaran murya tare da bata rai
‘Uhm! Ashe fa naku tsarin da ban ne. Naga dai abun karramawa ce da girmama uwargida tunda iyayenta ne da iyayenka zasu kawota, idan basu kawota sun nuna mata mu zauna lafiya ba ai dole tazo ta kalleni banza banza…'
Ya ajiye cokalin hannunsa ya hadiye abincin bakinsa da sauri ya tari numfashinta
‘A’a ai ba zata yi haka ba, nima ba zan barta ba ai kuma fa…'
Ta tabe baki itama ta katseshi a daidai lokacin da kwalla take fadowa daga idonta
‘Um um ai ba sai kace komai ba wanne bari kuma? Tun yanzu ka fara raba kan gidanka! Ka ce ba zata shigo cikinmu ba ni da ‘yayanka, yanzu kuma kace ba za ma a kawota a nuna mata girmana ba, ai shikenan ku yi zamanki ku biyu nima na koma cikin ‘yan kallo.’
Ta juya da hanzari ta nufi hawa sama, ya mike tsaye yana kallonta da mamaki da damuwa
‘Haba Zarah…'
Kafin ya karasa ta haye sama tana share hawaye, ya koma ya zauna a kan kujerar kamar wanda aka tunkuda, ya bi hanyar da ta bi da kallo yana mamaki.
Tabbas Aisha ce ta nuna ta fi son gidanta ita kadai kuma da ya gayawa Zahra bata nuna damuwa ba, amma yanzu shi da kansa yace ba sai an kawota ba saboda gudun ayi wani abu da zai tada rigima. Ya ma riga ya gayawa Aishan da Yaya Zuwaira cewa idan an daukota a kaita gidanta kai tasye.
Ya dafe kai yana mamakin Zahra, wai shi da kansa ya tarwatsa gidansa kuma anki a girmamata. Ya ma za ayi tace haka bayan duk wannan kaffa-kaffan da yake yi dominta ne?
Ya ture kwanon abincin ya mike ya bi bayanta.
Kamar yanda ya zata a dakinta ya sameta, tana zaune a gefen gado tana tunani tare da fitar da hawaye; ta riga ta karbo layar da Malam ya bata ta sa a wajen da amarya zata tsallaka kuma a ranar Malam yace tayi don da gari ya waye amarya ta bar mata gidanta, idan ba a kawo mata amaryar ba ya za ayi ta samu wannan damar?
Da yake bata hade kofar dakin ba har ya shiga bata sani ba saboda nisan da tunaninta yayi, sai da yayi gyaran murya sannan ta dawo hayyacinta.
Ta yi sauri ta share hawayenta ta mike tsaye tana kokarin shigewa bandakinta, yayi sauri ya kara taku biyu ya riketa.
Ta juyo ta gefe tana kallonsa tana kokarin saita fuskarta.
‘Mm! Bandaki zan shiga.’
Bai bata amsa ba ya riketa ya zaunar da ita a gefen gadon ya zauna a kusa da ita sannan yace
‘Kiyi hakuri ki fahimceni, da kai a nace kada a kawota saboda kin san halin mata ban sa da su wa za a taho ba daga can gidan nasu. Amma idan dai wannan ne ya bata miki rai to ki daina damuwa za a kawo miki ita nan, tunda dama su Goggo Habiba ne zasu daukota. Shikenan?’.
Ta kawar da kai tare da gyara zama
‘Ni bani da wata damuwa kuje kuyi yanda kuka tsara kawai.’
Ya tsattsareta da ido, har sai da ta sunkuyar da kai sannan yace
‘Ku cigaba da shirin tarbar amarya, za a kawo miki ita idan kuka gama sai su kaita nata gidan. Shine tsarina.’
Ta amsa murya kasa-kasa
‘Uhhm!’
‘In akwai wani abu da kike bukata sai kiyi min magana.’
Tayi shiru na dan lokaci, har zai tashi tayi gyaran murya tace
‘Dama akwai kudi da zan bawa amaryar kyauta kuma sababbi ake bayarwa, to na bada naira dubu goma a samo min sabbinsu har yanzu ba a kawo ba, ban sani ba ko zan samu a wajenka.’
‘To babu damuwa, idan kika shigo sai na baki akwai wasu da na canza.’
‘To na gode, Allah ya sanya alkhairi.’
Ya mike ya fice ya ja mata kofa. Ta bi kofar da harara da murguda baki kamar yana wajen tace
‘Asabar i yanzu ka dawo hayyacinka.’
Ta mike ta shige bandaki don ta wanko fuska.
____
Tun da aka ce an tafi kafi Aisha ta sake shiga damuwa, kana kallonta zaka ga ta wani firgice. Hajiya tana kula da ita sosai don haka ta cewa Zahida kada ta bari su rabu, ta dinga bata hakuri tana tauson zuciyarta. Ko da su Yaya Zainab suka dawo daga kafin ma kin zama tayi a inda suke, da yake sun ganeta sai kawai kowa ya fita harkarta.
Duk a gidan suka kwana ana ta hira da kuma shirin biki. Gari yana wayewa Aisha ta kara firgicewa, hawayen da take makalewa ma yau kyaleshu tayi. Tana hawaye