Showing 27001 words to 30000 words out of 201092 words

Chapter 10 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt

zauna ne ta fara bamu labari.


"Umma, yau na had'u da tashin hankalin da tun da nake a rayuwata ban tab'a shiga irinsa ba.


Na ga abin mamaki, wanda tun da nake ban tab'a ganin irinsa ba.


Umma na kasa gasgatawa, shi ne, ko ba shi ba ne? Na kasa amincewa, shi d'in ne dai ko kuwa wani mutumin ne na daban?..." tana kaiwa nan ta yi shiru a zancenta, ta dafe kanta da ke barazanar fashewa, ta ci gaba da fad'in,


"A dai-dai sanda na gama wa'azi, k'arfe biyar da rabi na baro gidan, amaryar da k'awayenta suka rako ni har bakin titi, suka tsayar min da keke napep sannan suka bani dubu uku.


Keke nalep d'in to ba mai tuk'in bane kawai zaune, su biyu ne har da wani a gefensa.


Duk da na yi addu'a sanda zan bar gida, na yi addu'a bayan fitowata daga gidan da na yi wa'azin, sannan kuma na yi addu'a a dai-dai sanda zan hau napep d'in. Na samu kaina da rashin natsuwa, gabana sai fad'uwa yake ban san dalili ba.


A titin ring road da ya kamata mu yi gabas daga shi, sai na ga sun zarce da ni.


Ganin haka ya sa na ce,


"Mallam, Gidan dawa fa na ce ku kai ni."


Daga mai tuk'in har na kusa da shi babu wanda ya furta min komai, babu wanda ko da kallona ya yi. Sai ma k'ara wutar napep d'insu da suka yi.


Salati nake ina ambaton sunan Allah, hankalina baki d'aya ya gama tashi, sai faman kalle-kalle nake.


Wata kwana na ga sun shiga da ni, daga nan suka ringa shiga lungu da sa'ko, har muka b'ulla wani k'asurgumin daji, wanda tun da nake a rayuwata ban tab'a sanin akwai irin wannan dajin a Katsina ba.


A dai-dai bakin wata gidan gona suka dakata, wanda ba shi ne ke tu'kin ba ya fara sauka, sannan wanda yake tuk'in ma ya sauka.


"Wai bayin Allah ina ne nan kuka kawo ni? Dan Allah ku rufa min asiri, ku taimaka ku fitar da ni daga wannan dajin."


Dariya suka k'yalk'yale da ita su duka biyun, kafin suka finciko ni da k'arfin tsiya daga napep d'in, suka isar da ni cikin gidan gonar.


A wani babban falo suka dire ni, ina kuka sosai, kuma har a lokacin ban manta da sunan Allah ba, ban daina neman taimako daga mahaliccina ba.


Cikin wani d'aki suka shiga, sai ga d'ayan ya dawo, d'ayan kuma bai fito ba.


Wanda ya fito d'in ne na ji yana waya, wayar da ta tayar min da hankali, ta sa gabana ya ringa duka da sauri-sauri.


"Oga mun zo kuma baka nan sai Yax kawai muka samu. An samu wata d'anya shakaf. Uztaziya ce sosai, dan fuskarta ma a nad'e take da nik'ab, ina jin a jikina zata maka sosai. Ehh zata maka sosai ma kuwa." Ya k'arasa wayar da dariya a fuskarsa.


Bayan wasu da'kik'u wanda ba zasu wuce goma ba, sai ga Ogan nasu ya iso, fuskata na kallon wata k'ofa ta inda wancan d'ayan ya shiga, har ya iso daf da ni ban sani ba.


Hakalina bai gama tashi ba, ban daina jin fargaba ba, sai a lokacin da idanuwana suka fad'a a saman fuskarsa.


Shi d'in kanshi da mamaki yake kallona,


"Ke ce?" Ya furta had'e da zaro ido.


Mik'ewa na yi ina gwada sa da yatsa, ido da bakina duk a bud'e suke,


"Kai....kai ne Ogan nasu dama?"


*To fa! Me ke faruwa ne haka? Wanene wannan Ogan wanda suke satar 'yan mata? Me yasa yake mamaki dan ya ganta, hakan na nufin ya santa ke nan? Ita d'in ma da alama ta sanshi fa. What is happening? What do you think, readers?*


*Duka zaku samu wannan amsoshin a next page insha Allahu.*


_kar mu manta da ambatar sunan Allah a duk halin da zamu tsinci kanmu. Mu daure mu kira sunan mahaliccinmu, saboda shi ne kad'ai zai iya bamu kariya, zai kub'utar da mu daga halin da muka tsinci kanmu._


*Wattpadians, don't forget to comment on each line, and then vote after reading every page. Ina kallonku, masu karantawa basa voting, Ghosts ke nan. PrincessAmrah zaku yi searching don samun many books of mine. Thanks always*


Pinky durling💗
*RAZ 2*
[8/30, 3:35 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


1⃣8⃣


Sunkuyar da kansa ya yi k'asa yana mai murtsuka gashin kansa da duka yatsunshi.


Jin k'afafuwana kamar suna neman gagarar d'aukar gangar jikina yasa na gaggauta zama da k'arfi, idanuwana suna masu kawo ruwa.


"Esien!" Ya k'wala ma d'aya daga cikin yaran nasa kira.


Da hanzari sai ga d'aya daga cikin wanda suka sato ni ya wanzu a gabanshi, cikin wata murya ya ce,


"A mayar da ita, ta kwatanta maku gidansu ku kai ta, bana so ku mata wani abu kuma."


"An gama Oga." Ya furta had'e da komawa 'daki ya kira d'ayan abokin nasa.


"Kar'bi wannan takardar, daga nan ku tsaya chemist ku siyo min wannan maganin, har yanzu ina jin ciwo a k'afafuwan nan nawa, ina sauri ne ban tsaya na siyo ba."


Kar'ba ya yi sannan ya juyo da kallonsa gare ni, da alama cike yake da mamakin yanda Ogan nasu ya bijirewa tayinsu, shi d'in da a kullum yake jin dad'i idan ya ga yarinya budurwa, musamman kamilallu, wanda a ganinshi su ne zai samu zumarsu yanda yake so, ya lashe zumar cike da jin da'di, a 'karshe ya b'atar da su ba tare da sun san inda kansu yake ba.


"Mu je." Muryarsa ta dirar min a kunne, bayan tsawon lokacin da na lula a birnin tunani.


Bin bayansu na yi kai tsaye muka doshi waje, a daidai k'ofar fita ya dakatar da ni,


"Kar maganar nan ta fita matuk'ar kina son numfashinki."


Kai kawai na jinjina masa, har a lokacin ban daina ruwan hawaye ba.


Napep d'in na shiga, bakina bai daina addu'a ba, tunani da k'wak'walwata basu daina tababa a kan abin da na gani ba.


A cikin napep d'in ne abokan suke fira, duk da halin da nake ciki, duk da rabin hankalina baya tattare da ni, hakan bai hana ni mayar da hankalina gare su ba.


"Baabaa amma fa na yi mamakin Oga. Gashi dai abin da ya fi so, amma bai yi tsiyar ba."


Dariya wancan di'n ya k'yalk'yale da ita,


"Ina ganin dai ciwon k'afar nasa ne ya motsa. Baka ji har da magani ya ce mu siyo masa ba? Da alama shi ya sa ya sallame ta."


D'ayan ya ce,


"Zan iya yarda da hakan kam. Duk soyayyarsa da son falle sababbi dal a leda, amma ya bar garab'asa. Gaskiya Oga Sans akwai damuwa a tattare da shi."


Baki na bud'e ina mamakin sunan da suka k'ira sa da shi, ina mai jinjina sunan 'Sans' a bakina.


To waye shi? Wannan wane mutumi ne wanda kamanninsa iri d'aya da Yaa Noor d'ina? Duk ta k'are shi ne wanda na yawaita gani a asibiti. Shi ne wannan gurgun da nake gani a keken guragu tsawon shekaru da dama da suka gabata.


Amma kuma ta ya zan gasgata cewa ba Yaa Noor d,ina ba ne bayan kamar tasu babu banbanci?


'Ta d'abiu da sa'banin halaye.' Wani sashe na zuciyata ya bani wannan amsar.


"Ke mun zo Gidan dawa. Ta ina zamu bi?"


Muryar gardawan ta dawo da ni daga duniyar da bani na kai kaina ba, duniyar da tunane-tunane ce kawai ta jefa ni.


"Kwanar gaban shagon can zaku shiga."


Na fad'a da disasshiyar murya, wacce kuka ya gama dishasarwa.


Har gaban gida suka kawo ni, suka kuma k'ara bige min warning a kan kar maganar ta fita, kar na bari hukuma ta shiga, saboda komai zai iya faruwa da ni."


Amrah na kai wa wannan gab'ar ta dakata, tana shesshe'kar kuka sosai, jikinta sai faman rawa yake.


Cike da tashin hankali na jawo ta a jikina, ni d'in ma kukan nake sosai.


"Ya isa haka to. Ai gashi babu abin da ya same ki ko? K'arfin addu'a ke nan."


Ni d'in ma ban daina kuka ba.


"Gaskiya ba za a bar maganar nan ba. Ya zama dole hukuma ta shiga wannan maganar, ko dan gaba."


Mallam ya furta yana mai jinjina lamarin.


"Dan Allah Abba kar a shigar, wallahi ina tsoro."


Ta fa'da cike da muryar kuka.


"To ke ya kike ganin gaskiyar lamarin? Ni dai na tabbata ba Annur ba ne, na san Annur yaro ne mai hankali, yaro ne mai sanin ya kamata, wanda na yi imani da Allah ba zai kasance mai irin wancan halin ba.


Ga kuma babbar hujja, wancan d'in ma da kike fad'i gurgu ne, kuma ga wannan ma maganar ta kusa zuwa d'aya. Da alama dai kama ce mai tsanani suka yi. Kin san ana samun irin haka."


Cike da gamsuwa Amrah ta jinjina kanta,


"Na yarda da wannan bayanin Umma. Tabbas na san ba Ya Noor d'ina ba ne. Kuma dan ya nunar da alamun mamaki a lolacin da ya gan ni bai zama hujja a ce shi ba ne, tun da shi d'in ma na san shi a asibiti, shi ma ya san ni, mun sha had'uwa da shi, har gaishe ki ma yana yi. Da alama dalilin da ya sa ya sallame ni ba tare da ya min komai ba ke nan. Wallahi na yarda ba Hammana ba ne, wancan mutumin banzan dai ne. Fasi'ki, mazinaci, azzalumi!" Ta k'arisa da share hawayenta.


"Mallam tun da dai abun haka ne, kuma shi d'in bai mata komai ba, kawai mu hak'ura, mu barsu, akwai ranar da zasu ha'du da dai-dai ya su."


"Haka ne. Allah Ya tsayar nan to. Allah kuma Ya k'ara karewa."


"Ameen ya Rabb. Kuma sai fa da ta nunar da bata son tafiyar, kamar ta san abin da zai faru. Ni na tilasta mata tafiyar, ashe abin da zai faru ke nan."


Wani kukan ya sake kufce min.


"Ya kamata ku yi shiru haka nan. Babu abin da addu'a ta bari. Kuma na yarda cewa addu'ar da ta yi ne ya sa abin ya tsaya nan, har zuciyarsa ta sanyaya, ya iya tuna ma ya ta'ba ganinta.


Kin san mafi yawancin mutanen banza irin wa'innan, sun fi d'aukar mummunan hukunci a kanka ma sanda ka nunar da ka sansu. Amma hikima irin ta Allah, da taimakonSa sai suka sallame ta.


Lallai babu k'arfi babu dabara face a wurin Allah ma'daukakin sarki! Shi ya halicce mu, shi muke bautamawa, kuma shi ne maji k'anmu. Shi ne mai taimakonmu a duk lokacin da Ya ga dama. Shi ke kare mu a duk sanda muka nemi kariyarSa.


Babu babban butulci sama da neman taimako ko kuma agaji ga wanin Allah. Sau da dama wasu sukan butulce, su nema taimako ga d'agutu, wanda shi d'in kanshi sai Allah ya bashi iko.


Me zai hana duk sanda muka samu kanmu a cikin tashin hankali, mu ambaci "INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!"? Ita ce kalma mafi girma, wacce ya kamata mu ambata a duk sanda wani tashin hankali ya riske mu.


Kin kyauta sosai y'ata, kin buk'aci taimako ga Allah kuma Ya taimake ki. Ina alfahari da ke, ina alfahari da baki d'aya halayenki, ina alfahari da iyalina."


Ya 'karashe maganar da murmushi shimfi'de a saman fuskarsa.


Take muka manta da duk wani tashin hankali, muka ci gaba da rayuwarmu kamar kullum, tana min labarin yanda wa'azin auren ya kasance.


Tun daga wannan tashin hankalin da muka shiga, bamu sake samun kanmu da shiga wata damuwa ko matsala ba, Annur kuma dama na fad'a ma Amrah ko da wasa kar ta masa tad'in. Tun da dai mun tabbatar cewa ba shi ba ne, kawai dai mai kama da shi ne. Na tabbatar idan muka fa'da masa ba zai ji dad'i ba, kuma zai yi bincike sosai har a gano mutanen, bayan kuma mun saki maganar, gwara dai mu barsu da duniya, saboda ta fi bagaruwa iya jima.


Haka kwanaki suka ci gama da gudanya, har su Amrah suka fara zana jarabawar WAEC.


Ranar da suka fara ne ta dawo cikin yanayin zazzab'i, irin mai zafin jikin nan sosai, wanda ko rintse idonta cikin wani hali take yinsa.


Mallam Mu'ammar ne da kanshi ma ya dawo da ita bisa mashin d'insa, bayan sun fito daga exams.


A yanayin da na ganta, sai da hankalina ya tash, gabana ya ringa fad'uwa.


"Me ya faru da ke?"


Na gaggauta tambayarta.


Tab'a fatar jikinta da na yi ne ya bani amsar tambayar da na mata, tun kafin ita d'in ta amsa min.


"Subhanallahi! Lafiya lau fa kika fita Amrah. Ko kin shiga ruwan saman nan da aka yi ne"


A daburce na sako zancen, ina mai sake tab'a jikinta.


"Umma an caccanza mana hall ne har sau uku, daga farko aka kai mu Class, sai aka sake canza wani, a 'karshe kuma aka kai mu exam hall. Kuma duk a cikin ruwa muka yi yawon. Tun daga sannan ne na ji jikina ya mutu, zazzab'i mai zafi yana sauko min, da k'yar ma na rubuta jarabawar."


Ta k'arisa maganar tana mai yin hamma, irin mai nuna yanayin zazzab'in nan.


"Aikam tashi zaki mu tafi asibiti, tun da wuri ma.." ban rufe baki ba muka ji sallamar Annur.


Sanye yake da suites ba'ka'ke, sai light blue riga mai dogon hannu daga k'asa, neck tie di'nsa bak'i mai di'go di'gon light blue d'in.


Amsa sallamar tasa na yi, ina mai k'oka'rin k'irk'iro masa murmushi.


Bayan mun gaisa da shi, Amrah ma ta gaishe shi ne yake tambayar lafiya? Dan ya kula da yanayin namu.


"Ehh to, ta dawo exam ne ka ga ko uniform ma bata cire ba. To kuma zazza'bi take sosai, ga hawaye nan sai fita suke da kansu. Yanzu haka shawarar kai ta asibiti ma nake."


Kallonshi ya miyar ga Amrah, cike da soyayya, kallo mai nuna zallar tausayi, k'auna da kuma irin kewarta da ya yi.


Kalar idanuwan nasa ne suka sauya, daga farare tas da suke, zuwa jajaye. Haka yake, a duk sanda zai tarar Amrah bata da lafiya, kuka ne kawai baya fasawa.


Cikin wata irin murya ya ce,


"Ta shirya zan kai ta Umma."


Maganar da ya yi ce ta sa na tuno zancen da nake so mu yi da shi, wanda na jima ina yi masa amma ya yi kunnen uwar shegu da ni.


"Yauwa, Annur ba dai zan gaji da rok'onka ba, dan Allah..."


Saurin dakatar da ni ya yi,


"Wallahi Umma bana jin zan iya yin awon genotype. Ina ji a jikina ni ba AS ba ne, AA ne da ni. Ban san ya zan yi ba idan na yi wannan awon aka ce ina da AS, ban san wane hali zan shiga ba. Bana jin kasantuwar Amrah SS zai sa na hak'ura da aurenta."


Gya'da kai na yi ina kallonshi. Cikin k'wayar idonshi na kalla, na karanci yanda soyayya ta makantar da shi, ta sa baya ganin komai sai Amrah. Soyayya ta kurumtar da shi, ta sa baya jin maganar da nake masa a kan wannan awon. Sosai na fahimci yanda soyayya ta jirkitar da tunaninsa, ta sa ya kasa gane muhimmancin wannan awon.


"Amma Annur, baka tunanin halin da yaranku zasu shiga nan gaba? Me kake tunani idan yaran da kuka haifa suka shiga cikin hali irin na Amrah, ko kuma ma wanda ya fi nata?"


"Wannan ba abun damuwa ba ne Umma. Zamu iya tsaida haihuwar ma baki d'ayanta. *AMRAH NAKE SO* ba wai abin da zata haifa min ba.


Wallahi ko AS nake da shi ba zan iya hak'ura da ita ba. Bana jin zan yi rayuwa mai kyau ba tare da Amrah ba. Bana jin zan ta'ba yin aure matu'kar ba Amrah na aura ba. Saboda haka, Umma, awon genotype bashi da wani tasiri a gare ni. Dan Allah yau dai a tsayar da maganar nan. Tun kafin a saka ranar aure muke yinta, Umma ta gagara k'arewa, har gashi yanzu bai fi mana watanni uku a d'aura aure ba."


Jin ya dakata daga nan, ya sa na dafe kaina, baki da'ya jikina ya yi sanyi.


"Ai shi ke nan. Amrah tashi mu tafi. Bara na d'auko makullin gidan a d'aki. Amma ki fara kiran Abbanki ki sanar masa."




_Addu'a na sauk'ak'a masifu da bala'iku sosai. A duk halin da zamu tsinci kanmu, na ciwo ne ko kuma wata damuwa, kar mu manta da INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!_




Pinky durling💗
*RAZ 2*
[8/30, 3:36 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


1⃣9⃣


Bayan mun isa asibitin ne muka buk'aci a had'a mu da Dr. Xarah ko kuma Dr. Rabiatu, amma aka shaida mana Rabiatu bata nan, dole sai dai Dr. Xarah.


Bayan mun shiga Ofishin nata, kallo d'aya ta ma Amrah ta tabbatar da bata jin dad'i.


"Sannu Amrah." Ta furta cike da tausayi.


"Jikin dai kuma" ta jinjina kanta.


"Wallahi kuwa Dr. Daga makaranta ta dawo min haka. Wai ruwa aka saka suka shiga wurin canjin hall, har ruwa ya mata duka."


"Subhanallahi! To Allah Ya kyauta gaba."


Ta zaro lokar dake gaban teburinta.


"Ungo thermometer, ki saka a armpit d'inki."


Karb'a ta yi kuwa ta saka, ta d'an jima kafin ta nemi ta fiddo ta.


"Subhanallahi! Temperature d'inta har ya haura ma 47. Lallai zazza'bi ya shige ta sosai. Bara na rubuta mata magani. Ku tsaya ku karb'a sannan a mata awon jini, idan ya sauka dole a tarbi abun, a mata k'arin jini."


Ta hau rubutu.


Bayan ta gama ne ta mik'o min takardar, tare da yi mana fatan alkhairi.


Har zan fita ta dakatar da ni,


"Maman Amrah wai yaushe ne ma aurenta?"


Murmushi na yi na ce


"Wata biyu ne da 'yan makwanni suka rage. Insha Allahu idan ya matso zan zo na sanar miki."


"To Allah Ya kaimu. Ina fatan dai an san genotype d'in angon nata." Ta furta a hankali.


Kallona na mayar ga Annur, ina k'ok'arin magana ne ya yi caraf ya ce


"Ehh, an yi Dr. AA ne da shi"


"To masha Allahu. Haka ake so ai." Ta fad'a.


Bankwana muka mata sannan muka fita.


D'akin magani muka fara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login