Showing 174001 words to 177000 words out of 201092 words
Chapter 59 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt
da ƴan ta'adda suka fara kawo musu hari. Tun daga harbin da ya ji an ma Abbunsu, izuwa fitarsu daga gida, suka zauna a kango, har tafiyarshi zuwa siyar da wayarsa bai bari ba. Duk abin da ya faru a wannan ranar har komawarsa Maiduguri da motarsu da ta lalace a hanya, dawowarsu bayan ya siyo musu, harbin ƙafarsa da aka yi abinci duk ya rubuta.
Ta dafe kanta cikin mamaki. Tunani ta fara yi kodai ba na Uncle Noor ɗinsu ba ne? Sai dai kuma hotonsa da ta gani a next page ya tabbatar mata da cewa nasa ne. Amma kuma a ina ya samu suna Salman (Sans)? Tambayar da ta gaggauta yi wa kanta kenan. Ba ta kai ga samun amsarta ba ta buɗo shafin gaba. Nan kuma duk abin da ya faru washe gari ne a rubuce. Mutanen da suka zo suka tsotse man motarsa suka tafi da shi Maiduguri, kai shi asibiti da suka yi, zaman da ya yi a can har ranar da aka sallame shi.
A wannan gaɓar hawaye sosai Janan ke yi, mamaki bai gushe daga saman fuskarta ba. Ta sake buɗo wani shafin, sai ta ga hoton Sans ɗin wanda yake a cikin yanayi na damuwa. Daga ƙasa an rubuta
"Tun daga lokacin da na zama gurgu na tsani kaina, na tsani komai nawa. Kamar yadda fuskata babu annuri a wannan hoton, to haka na kasance tun sadda aka naƙasa min ƙafa."
Ta matse ƙwallarta, haɗe da buɗo next page. A nan kuma tafiyarsa ce daga Maiduguri har zuwa Katsina. Ƙalubalen da ya fuskanta a tafiyar, da kuma bawan Allah'n da ya haɗu da shi a mota wanda har ya saya masa abinci. Isowarsa tasha da fizge masa kuɗin da aka yi sadda yake kan keken guragunsa.
A shafin gaba kuma haɗuwarsa da Farouk Sardauna ne. Silar haɗuwar tasu da kuma taimaka masa da ya yi ya kai shi gidan gonarsu. Ta sake buɗo wani shafin, sai ta ga hoton Bobby wanda ya saki kyakkyawan murmushi a ciki, daga ƙasa an rubuta,
"He always smiles. He helped me, and never forget him in my mind. Ina fatar ranar da Allah zai kawo min hanyar da zan rama taimakon da ya yi min, ko da kwatankwacin wanda ya min ɗin ne."
Ta buɗo wani shafin. Date da time ne duka a rubuce na ranar da ya fara shan kayan maye. Ya rubuta,
"Ba na so, amma damuwa da ta yi min yawa ta sa na fara. Na kuma ji daɗin hakan, saboda ban ƙara shiga cikin damuwar rashin dangina ba tun daga sadda na zama drug abuser."
Shessheƴar kukanta ce ta tada Hanan. Cikin magagin barci ta yi firgigit ta buɗe idanuwanta.
"Janan whats wrong with you? Why are you crying?"
Ta yi saurin ɓoye diary ɗin, ta share ƙwallarta.
"Its nothing."
Ta ƙirƙiro murmushi. Zaune ta miƙe Hanan. Ta ce,
"There must be something wrong, Janan. Ke ɗin nan da ba kya kuka, amma look at your face, tears sun gama wanke cheeks ɗin ki. Janan kina da wacce ta fi ni ne?"
Ta gyaɗa kanta.
"To me ya sa za ki ɓoye min damuwarki? Mene ne kike ɓoyo da wancan hannun?"
Ƙarfafa kukan nata ta yi Janan, ta ce,
"Hanan akwai damuwa fa, damuwa mai girma. Uncle Noor..."
Ta kwashe duk abin da ta karanta ta sanar da ita, tare suka ci gaba da jimamin cikin kuka, sannan suka ci gaba da karantawa.
Abin da ke gaba rubuce shi ne haɗuwarsu da Annur mahaukaci a daji, da kuma ɗaukarsa suka miyar zuwa gidan gonarsu. Tafiyarsa ya haɗu da foster da ake cigiyarsa, sauya kayan Annur zuwa jikinsa, aske gashin kansa zuwa irin na kan Annur, yadda aka yi ya dawo gidan lokacin da Bobby ya kawo shi. Duk babu abin da ya ɓoye a diary ɗin.
Kallon junansu suka yi, sun kasa tsayar da hawayensu. Mamaki bai gushe daga zuƙata da fuskokinsu ba. Hanan ta yi sauri ta buɗo shafin gaba.
Aikin da boka ya musu ne a farkon shafin, yadda aka jiyar da hankalin kowa, aka kasa ganin ko ɗison bambancinsa da Annur, da canjin aikinsa a kamfanin Dady daga mai zane zuwa ga CEO, rabuwa da abokan ainahin Annur, shaƙuwarsa da Bobby kaf sai da ya zana.
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!"
Hanan ta faɗa hannunta a ka.
"Why did you do this? Me ya sa za ka yaudari su Dady? A ina ka kai mana Uncle Noor ɗinmu?"
Kalaman da ke fitowa daga bakin Janan kenan cikin kuka. Suka sake buɗe wani shafin.
Haɗuwarsa da Maryama ne a jiki, ranar da daga kallo ɗaya ya fara ƙaunarta, faɗan da Dady ya masa a kan fara rugujewar company saboda sakacinsa, zuwansa wurin boka ya masa faɗa a kan true love, aikin da aka masa aka cire masa ƙaunar Maryama, duka ya rubuta.
Shafin gaba kuma damuwar da ya fara shiga lokacin da Farouk Sardauna ya fara ciwo ne. Farkon zuwansu likita da kuma gargaɗin da aka musu game da smoking. Tsanantar ciwon Bobby, da kuma damuwar da suka shiga sosai na ciwon nashi.
Next page hotonshi ne ya dafe goshinsa yana kuka sosai, a ƙasa ya rubuta
"Unforgetable day, the night that my best ever friend gone, and gone forever"
Da date da komai na ranar, ya kuma rubuta irin raɗaɗin da zuciyarsa ta shiga.
Suka sake buɗe wani shafin, alƙawarin da ya ɗauka na daina smoking da duk wani mugun hali ne a ciki.
Suka kalli juna cikin kuka sosai, duk da sun ji haushinsa daga farko, amma a nan sai suka fara tausaya masa. Bai kyauta ba abin da ya yi, amma idan aka yi la'akari da jalalar rayuwa da ya gani a baya, dole a ji tausayinsa. Suka sake buɗe wani.
Alƙawarin Bobby da ya so cikawa ne a jiki, sai dai hakan bai samu ba, ya haƙura da Maryama har abada.
Shafi na biyun ƙarshe suka buɗe, hoton shi ya duƙar da kansa ƙasa, ya rubuta,
"Hukuncin ƙarshe da zuciyata ta yanke min."
Suka buɗo shafin ƙarshe, wanda ya rubuta,
"I've decided to kill myself. Na so na taushi zuciyata, amma abun ya gagara. A lokacin da nake yin wannan rubutun, kuka nake sosai, na yi shi ne musamman domin duk wanda ya yi farko a karatun diary ɗin nan ya tabbatar cewa ba haka kawai Salman ya so kashe kansa ba. Rayuwar ce ta juye masa baki ɗaya. Farin-ciki ya ƙaurace masa. Ina roƙon duk wanda ya fara karanta diary ɗin nan, ya samu Dady da Momy cikin nutsuwa, kar ya tayar musu da hankali, sannan ya ba su su karanta. Idan kuma a cikin Dady ko Momy ne suka fara karantawar, ina mai roƙon gafararku, ku gafarta min na basajar da na muku, na zauna da ku a matsayin ɗanku da kuka haifa. Na gode ƙwarai da tarayyata da ku, ku ɗin mutanen kirki ne, wanda samun kamarsu a daidai wannan lokacin zai yi matuƙar wahala. Ɗan ku Annur yana raye, sai dai an masa kurciya, da ko ni kaina ban san inda yake ba yanzu haka. Please forgive me, once again."
Ya saka full stop a daidai nan.
Rungumar junansu suka yi su duka biyun, kuka sosai suke yi, suna matuƙar jin daɗi da Allah ya sa Sans ɗin bai mutu ba. Duk da abin da ya aikata, suna son shi a hakan, matsayi da darajarsa kuma suna nan a cikin zuƙatansu.
Rufe diary ɗin Janan ta yi, babba ne kamar girman photo album, sannan ta ajje a gefenta.
"Duk da kuskuren da ka tafka ka ba ni tausayi."
Hanan ta faɗa. Janan ta ce,
"Mu bari har da safe sannan mu kai ma su Momy su karanta ko?"
Hanan ta ce,
"Janan tunda dai bai mutu ba mu yi haƙuri mu binne maganar nan, ba mu san kalar hukuncin da su Dady za su ɗaukar masa ba. Kin ga ya ce idan aka kore shi daga nan bai san inda rayuwarsa za ta faɗa ba.
"Dole za a faɗa musu, Hanan. Idan har muka yi shiru to Allah zai iya kama mu da laifin yaudara. Na san halin Dady, kamar yadda na san halin Momy. Na tabbatar cewa ba za su ƙi shi ba. Za su masa uzuri, sannan kuma za su tashi tsaye neman Uncle Noor."
Hanan ta yi shiru, kafin ta ce,
"You are right Janan. But ni dai I can't tell them. Wallahi ba zan iya sanar da su ba, don ban san halin za su shiga ba bayan sun ji."
"Ni zan sanar musu, yanzu ma ba sai gari ya waye ba."
Hanan ta riƙo ta,
"Janan me kike shirin aikatawa a cikin daren nan? So kike yi ki hana su barci?"
"Hanan please let me tell them. Da safe kuma idan ya shigo ta yaya zan iya faɗa musu a gabanshi?"
Shiru Hanan ta yi kawai ta koma ta kwanta. Damuwa lulluɓe da zuciyarta, zullumi da fargaba take tsananin ji.
Ta sauka daga bisa gadon, haɗe da nufar ɗakin Dady.
Knocking ta yi a hankali ta ji shiru, hakan ya sa ta ƙara yi.
"Waye?"
Ta ji muryar Dadyn ya faɗa.
"Janan ce Dady."
"Lafiya?"
Ya ce bayan ya buɗe mata ƙofar ido a buɗe. Diary ɗin hannunta ya kalla.
"Me ya faru?"
"Dady akwai matsala."
Ta share hawayen da ya kuma sauko mata. Ya kunna wutar ɗakin sannan ya kama hannunta zuwa bakin gado. Motsinsu ya sa Momy ta buɗe idanuwanta, tana ganinsu ta gaggauta murtsukar idanuwan haɗe da tashi zaune tana tambayarsu abin da yake faruwa.
"Ni ma kaina ban sani ba Suhaila. Shigowarta kenan ɗakin tana kuka."
"Subhanallahi! Janan ba ki da lafiya ne?"
Ta gyaɗa kanta.
"Whats your problem? Where is Hanan?"
"Tana ɗaki."
Ta miƙo ma Dady diary ɗin.
"Dady I want you to please read this. Amma don Allah ba na so ku tashi hankalinku. Shi al'amarin Allah duk inda kake ba ka tsallake shi. Ku ɗauka a zukatanku cewa wannan ƙaddararku ce, kuma dole sai ta faru da ku."
Cikin mamaki da kiɗima Momy ta ce,
"What are you saying, Janan? Me ke a cikin littafin?"
"Ku karanta Momy. And calm down, idan ba ki nutsu wurin karatun ba ba lallai ki fahimci wabi abu ba."
Ta miƙe da kuka ta bar ɗakin haɗe da jawo ƙofar ta rufe.
*
WASHE GARI
Da sassafe ta tashi kamar kullum, ta nufi kitchen. Dankali ta fere ta yanka sannan ta tsane a kwando ta barbaɗa gishiri. Ta ɗora mai a kasko bayan ya yi zafi ta zuba dankalin. Tarugu da albasa ta yi grating sannan ta yayyanka hanta ƙanana-ƙanana. Ta zuba hantar a pan da ruwa kaɗan, ta saka kayan ƙamshi da albasa da maggi. Bayan ta dahu da zuba mai kaɗan a ciki ta soya sama-sama, ta juye tarugun a ciki ta hau suya. Ba wani soyuwa sosai ta yi ba ta zuba maggi da curry, sannan ta fasa ƙwai guda ɗaya a ciki ta hau juyawa. Bayan ta soyu ta juye a ƙaramin bowl, sannan ta kwashe dankalin saboda wuta kaɗan ta saka dana don kar ya soyu da wuri har sai ta gama sauce ɗin. Plate mai ɗan faɗi ta juye dankalin a ciki, ta nemi foil paper ta lulluɓe shi da bowl na sauce ɗin sannan ta kwasa ta kai dining. Electric water flask ta jawo daga jikin socket ta ɗora a table ɗin. Ta buɗe dining carbinate ta haɗo komai sannan ta nufi ɗaki.
Ta samu Annur har ya gama shiryawa cikin ƙananan kayan da ta ajje masa. Sai famar zuba ƙamshi ɗakin yake yi, ya yi zaune ya ƙura wa wuri ɗaya ido. Magana ta masa har sau biyu bai ji ba. Ta tafa hannu a daidai fuskarsa ya zabura.
"Mi amor."
Ta ɗan cunno bakinta bayan ta zauna kusa da shi.
"Ka sha kyau sosai."
Ya yi murmushi.
"Tunanin me kake?"
Dariya kawai ya sakar mata, ya yaƙe duka bakin nasa.
"Anyways, lets go and have a break fast."
Ta ɗora tafukan hannayenta, shi ma ya ɗora nashi a kan nata. Tare suka nufi dining area ɗin. Dama ta yi wankanta, ta saka ƙananan kaya riga da wando amma rigar mai ɗan tsayi ta kai guiwa. Bayan sun zauna ta hau ba shi a baki, sannan ita ma ta ba kanta. Da haka har suka ƙoshi.
Saƙale da hannu suka dawo falo. Ta kunna kallo sannan ta nufi bedroom ta ɗauko wayarta. Tana dubawa ta ga missed call na Dr. Hamdan Ramat. Ta iso falon daidai sadda take latsa kiransa tana Allah-Allah ya ɗauka. Bugu biyu kuwa ya ɗauka da sallama. Amsa sallamar ta yi sannan ta gaishe shi.
"Maryam na kira ne in faɗa miki na taho ina hanya ma. Amma ban san yadda za mu haɗu ɗin ba. Tambayoyi ne kawai zan ma mara lafiyar kafin in gano haƙiƙanin damuwarsa ta nan ɗin. Daga nan sai a ba shi duk maganin da suka dace da shi."
"Ok Dr. Dama na fara tunanin ko za mu je gidan kawunsa ne, sai mu yi maganar a can."
"To babu damuwa. Sai ku yi saurin shiryawa saboda few KM suka rage min zuwa Katsina. Ga shi kuma ba kwana nake son na yi ba."
"To bari ma mu tafi yanzu, sai mu jira a can ɗin. Allah ya kawo ka lafiya. Na gode."
Har da ɗan rusunawa ta yi tamkar tana a gabansa ne. Tana gamawa ta latso kiran Kawu Marwan. Bai ɗauka ba sai ya katse sannan ya sake kiranta ta ɗauka.
"Uncle dama Dr. Hamdan ne ya kira ni yanzu, cewa ya yana daf da ƙarisowa cikin Katsina. Wai yau ɗin nan yake son barin garin."
"To ku jira yanzu in zo in ɗauko ku."
"Mun gode uncle."
Girmamawar da Maryama gare ta kaɗai ya isa ya siye mutanen da suke zagaye da ita.
"Yah Noor yanzu kawu zai zo ya ɗauke mu. Don Allah duk tambayar da likitan ya maka ka ba shi duk amsar da ka sani. Kar ka je ka yita yaƙe bakin nan haka nan, ba wani abu zai fahimta ta haka ba."
Ya ɗaga mata kai. Tashi ta yi ta nufi ɗakinta. After dress ta zaro daga cikin kayanta ta saka, sannan ta yi veiling da pink kashka. Koda ta fito wayarta na ringing. Uncle Marwan ta gani, da sauri ta ɗauka, ta ji yana ce mata su fito yana ƙofar gida.
Hand bag ɗinta ta saɓa sannan ta ce da Annur ya tashi su tafi. Ta datse ƙofar falon ta jefa mukullin a jakarta. Sadda suka je bakin gate ta shaida wa mai gadi cewa za su fita sai zuwa anjima za su dawo. Ya musu addua da fatar alkhairi sannan suka fice. Bai ko kashe motar ba suka same shi, ta buɗe wa Annur gaban motar ya shiga sannan ta rufe, ita kuma ta zauna a baya.
Suna isa gidan mai gadi ya wangale musu gate suka ƙarisa ciki. Ita ta buɗe ma Annur motar ya fito, sannan ta kama hannunsa suka bi bayan Uncle Marwan ɗin. Cikin gidan ya nufa da su. Ya samu falon babu kowa, ya basu umurnin zama su jira shi a falon.
Bayan ya hau sama ya samu Yamaira a kwance fuskar nan tata ta gama kumbura da kuka. Ya ce,
"Wai ni kam Yamaira wannan kukan ba zai tsaidu ba haka nan? Ina amfanin abu guda tun jiya? Ni a tunanina za ki ɗaga hannu sama ki gode wa mahaliccinki da ya bayyana miki ƴan uwanki har biyu, ba tare da zato ko tsammaninki ba? Ki cire damuwar, don Allah. Ki sauko ƙasa ga su Maryama nan sun iso ita da Annur. Likitan wai yana bisa hanya."
Ta lallaɓa ta tashi zaune.
"Bari in samu watsa ruwa in sauko."
"Yauwa dai, please wipe the tears and let them go. Ki hanzarta shiryawa, na bar su falo su kaɗai."
Ya ɗauko Yesmeen suka sauka zuwa falo. Kallo ya kunna musu, tashar NTA suna kallon news. Yamaira ba ta wani jima ba ta fito cikin naɗin lafaya baƙa mai manyan zanen light blue. Duk da kukan da ta sha, amma hakan bai hana ta yin kyau ba.
Bayan sun gaisa ta koma kan kujera kusa da Maryama ta zauna. Ta ce,
"Ashe ma dai da wuri haka likitan zai zo."
"Wallahi kuwa. Ni ma kaina ban sani ba, a tunanina isowar yamma zai yi, kwatsam na ga kiransa cewa ya kusa ƙarisowa Katsina, kuma sai ya fara ganin Yah Noor sannan."
"Allah sarki!"
Ta kalli Annur. Wata irin nutsuwa take jin tana saukar dukkan gaɓar jikinta. Sosai take jin daɗi, take kuma ganin abun kamar a mafarki. A tunaninta ta rasa kowa nata, sai dai Allah da naShi lamarin, ashe har ma da ƙarin wanda ba ta sani ba. Iyayen nata dai ne ta rasa, rashi na har abada.
Sai ta ji hawaye na saukar mata, ta gaggauta share su don kar mai gidanta ya gan ta tana kukan.
Ƙarar kira Maryama ta ji a wayarta, ta duba ta ga Dr. Hamdan ne, ta gaggauta ɗauka da karawa a kunnenta.
"Ga ni na shigo cikin Katsina. Ga shi kuma ban san komai ba, so ɗaya na taɓa zuwa Katsinar ma tunda nake, kuma shekaru ba adadi."
"Ok Dr. To ko za ka samu mai kabu-kabu ne sai na masa bayani?"
"Tunanin da na yi kenan. Ina zuwa."
Ya tsinke kiran. Ba a daɗe ba ya sake kiranta. Suka yi magana da mai mashin ɗin, ta masa bayanin gidan, ya ce mata ya gane.
Minti ashirin da biyar ya isar da su gidan Alhaji Marwan. Ya sallami mai mashin ɗin sannan mai gadi ya buɗe masa gate kamar yadda Uncle Marwan ya umurce shi.
Mai gadin ya masa iso har cikin gida, suka shiga cikin falon tare.
Dr. Hamdan M. Ramat mutum ne mai tsananin ƙwarjini da kamala. Fari ne mai faraa, ya ɗan dattijanta sai dai ba sosai ba.
Ya shigo ya zauna fuskar nan tasa kamar koyaushe da walwala. Har ƙasa suka duƙa suka gaishe sa. Uncle Marwan kuma ya ba shi hannu da sakin fuska suka gaisa.
Kallo ɗaya ya ma Annur ya ce,
"Wannan ne mara lafiyar?"
Maryama ta amsa masa da ehh.
"Amma dai ya samu sauƙi ko? Ji idanuwansa fa. Kallar ni nan ka ji?"
Ya ɗora dukkanin idanuwansa ga Annur ɗin da shi ma shi yake kallo, sai dai yana ɗan kauce idonsa.
***
*Wash Allah! Na gaji. Iya wannan ya samu. Fatar dai kun ji daɗinsa. Kun ga dai yadda tafiyar ke ta gangara.*
*Wannan shafin sadaukarwa ne ga Teemah Sahabie. Sosai na ji daɗin kiran da kika min a waya jiya, musamman don ki nunar min da farin-cikin da kika ji na last page. na gode ƙwarai, Allahu ya bar zumunci.*
Thanks all.
Pinky durling💞
RAZ 2
[9/26, 12:03 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥*
_(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban