Showing 21001 words to 24000 words out of 201092 words

Chapter 8 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt

mamaki, mamakin kalaman da ta ji suna fitowa daga bakin Amrah.


Kamar butum butumi Annur ya koma, bai d'auke kallonshi daga gare ta ba, bai daina mata kallon yaushe rabo ba, sai dai tabbas yana matu'kar al'ajabin furucin da ke fita a tsakanin lab'banta.


"Baki da hankali ne da zaki danganta Annur da wani gurgu?


To ta Allah ba taki ba! Bakinki ya sari d'anyen kashi.


Insha Allahu har abada Annur ba zai ta'ba zama gurgu ba.


Sai dai ki ga gurgunta a ta b'arahinki."


Hajiya Suhaila ce ta dakatar da ita da fad'in,


"Ya isa haka, Saddiqa! Wai sai yaushe ne zaki fara sanin darajar d'an Adam?


Sai yaushe ne zaki san irin darajar da Amrah take da shi a zuciyata?


Idan ma baki sani ba to yau ki sani, banbancinki da Amrah a zuciyata ba wani mai yawa ba ne.


Ina nata son da nake wa kaina irinsa.


Saboda haka, matuk'ar kina son farin cikina, to ya zama dole ki so abin da nake so. Ki so Amrah tamkar yanda zaki so Islam. Saboda wata rana ita ma ina sa ran zata dawo cikin zuri'armu."


Lokaci d'aya ya yi gaggawar sauke idanuwansa daga nata, ya fara k'ok'arin kawar da tunanin da yake.


"Barkanku da isowa." Hajiya Subaila ta furta, had'e da rungumar jikokinta 'yan biyu, masu kama iri d'aya.


Nadrah ce ta kalli Amrah had'e da sakar mata kakkausan murmushi ta ce,


"I guess, ke ce Amrah, right?"


Murmushin da Amrah ta yi ne ya tabbatar mata da hasashenta.


"Ai ko ba a fad'a min ba dama na san ke ce. Saboda yanda na karanci fuskarki da ta Noor a lokacin da muka k'ariso. Mu isa gida ko?"


Murmushi kawai Amrah ke yi ba tare da ta furta komai ba.


Duk irin mararin da take na ganin Hammanta, amma ta kasa yi masa magana. Kunyarsa take jin tana ratsa ko wace gab'a ta jikinta.


Kasantuwar dama da prado suka zo, hakan ya sa ta kwashe su su duka, in banda Saddiqa da suka tafi cikin motarsu ita da yaranta, banda Salmah da ta nace sai inda Amrah take zata bi.


Sai kusan la'asar sannan suka iso, take gida ya kaure da murna, yau dai family'n Iqra Al-Hussein sun yi had'uwar da suka jima basu yi irinta ba.


Sun samu har Islam ma ta dawo, a yamutse ta fito babban falon da aka k'awata da wasu manyan takardu da aka rubuta
*WELCOME BACK YAYA NOOR!* Wanda ba wata ta yi wannan aikin ba face Amrah, dama ta riga ta gama komai, sanda zasu fita ta bar ma Safina cewa ta bi ko ina ta lilli'ka mata takardun.


Haka aka yi zaman cin abinci, murna fal a fuskokinsu, sab'anin Islam da tun da ta ma Amrah kallo d'aya bata sake had'a ido da ita ba, tsabar tsananta da ta yi.


Haka yammacin ranar ta kasancewa wannan ahali, farin ciki sosai da nisha'di, wanda zan iya cewa Annur da Amrah sun fi kowa jin dad'in wannan yanayi.


Daf da magrib Amrah ta d'auko jikar kayanta cewa zata tafi gida, saboda wata tarbiyya da ta samu, a duk inda take, matu'kar magrib ta kunno kai to hankalinta na karkatowa zuwa gida.


"Momy ni zan tafi. Na gode 'kwarai." Ta furta a tsanake. Cikin magabarta dalla-dalla kamar 'yar koyo.


Salma ta taso da sauri ta rungume ta,


"Aunty dama ba a nan zaki kwana ba? Dan Allah mana ki kwana, wallahi zan miki fira mai dad'i."


Murmushi Amrah ta mata,


"Na baro Ummana da kewana ne. Insha Allahu gobe da na dawo daga School zan zo." Ta dafa kanta.


D'aya daga cikin 'yan biyun Nadrah mai suna Janan ce ta taso ita ma da murmushi a saman fuskarta ta ce,


"Aikam dai Amrah da kin tsaya kin kwana. Zan rakaki yanzu ki tambayo Maman taki pls. I need you by my side. Kina burge ni saboda son da Uncle Noor yake miki."


Ajiyar zuciya ta sauke, tana k'ok'arin yin magana ne ta ji 'yar uwarta mai suna Hanan ta ce,


"Abeg let her go, Janan. Ke shisshihinki ke had'a ni da ke."


"Ehh d'in miye ruwanki?"


"Ya isa haka ni dai. Ku barta ta tafi yamma na mata. Bata da wadatacciyar lafiya ne kuma ga sanyi sanyin yamma na saukowa.


Amrah sannu da k'ok'ari, mun gode k'warai. Ki gaishe da Umman taki."


"To zata ji k'warai Momy. Sai da safe."


Mik'ewa Annur ya yi ya ce,


"Momy bara na raka ta, daga nan ma sai mu gaisa da Umma."


Kallonsa Amrah ta yi da murmushi, mai cike da soyayya ta ce,


"Allah Yaa Noor da ma ka barshi, ka zauna ka huce gajiya kawai. Gobe ba sai ka je ba?"


"An k'i a bari d'in. Wato ke kad'ai zaki ganta ni ba zan ganta ba ko? Sai na je." Ya bi bayanta.


Su Islam tamkar zasu fashe tsabar takaici, su dai sun tsani Amrah babu dalili. Ko kuwa dai kasantuwarta 'yar talakawa ce ya sa suka tsane ta? Allah masani.


Dai-dai ana kiran magrib suka iso, a lokacin ina d'ibarwa mallam ruwan alwala, wanda dawowarsa gidan ke nan.


Baki sake, fuska d'auke da murmushi nake kallonshi, kallon yanda ya koma a zahirinsa, ya zama cikakken mutum, tamkar wanda ba d'an shekara ashirin da biyar ba.


Shi d'in ma murmushi k'unshe a saman fuskrsa ya k'ariso ciki, har k'asa ya du'ka ya gaishe ni.


"Sannu Umma. Ina wuni?"


"Lafiya k'alau Annur. An dawo lafiya ko?"


Na fa'da har a lokacin fuskata bata daina murmushi ba.


"Alhamdulillahi Umma. Mun same ku lafiya"


Ya furta had'e da tashi ya isa inda mallam yake zaune, shi kad'ai sai kallon Annur yake yana murmushi.


"Lafiya lau fa."


Na bashi amsa.


Gaisawa suka yi da Mallam sannan ya mik'e.


"Bara na koma. A gajiye nake lis wallahi. Kuma akwai wani aiki da nake son yi a cikin daren nan."


A tare ni da Mallam muka furta "To Allah Ya hutar da gajiya."


Har k'ofar gida Amrah ta raka shi sannan ta dawo.


A ranar da suka cike kwana biyu da zuwa ne sai ga Annur da Janan sai kuma Salmah sun zo a cikin mota.


Jaye suke da wani babban akwati, wanda na rasa gane ko na menene.


Janan ce ta furta "Wannan tsarabar Amrah ce, daga Uncle Noor."


"To fa!" Na furta had'e da mayar da kallona ga Annur.


Tun ban fad'i komai ba ya gaggauta fita daga gidan.


"Wai duk Amrah kad'ai? Lallai a gaishe da Annur. Allah ya saka masa da alkhairi."


"Ameen Umma." Janan ta furta had'e da mik'ewa.


"Ban ga Aunty ba." Salmah ta fad'a tana wawware ido.


"Wai Amrah? Bata dawo daga makaranta ba." Na bata amsa.


"To idan ta zo a gaishe ta please."


Har k'ofar gida na raka su, na ma Annur godiya sosai sannan na dawo gida.


Bayan azahar ta dawo, a lokacin muka bud'e kayan muka hau duddubawa.


Kaya ne masu kyau, k'ananan kaya da kuma material irin na manyan yara. Takalma da jaka saiti biyu.


A take na sa ta ta kira Annur ta masa f
Godiya, na kuma shaida mata cewa ta fad'a masa, zamu zo har gida mu yi godiya.


Tun bayan dawowar Annur, rayuwa mai cike da k'aunar juna ta 'kara bun'kasa a zuciyoyinsu.


Soyayya suke mai cike da tsafta, wadda su kansu basu san cewa soyayya ba ce, sai dai kuma duk wanda ke tare da su, dole zai fahimci hakan.


Gashi dai k'aramin yaro, mai k'ananan shekaru, amma ya zama d'aya daga cikin manya manyan masu zane, wanda sunansu ya kewaye k'asar Nigeria.


Yau ta kasance ranar lahadi, wadda a yau ne za a gudanar da walimar saukar Al_Qu'ani mai girma ga su Amrah. Wanda suka samu nasarar haddace wa baki d'aya. Su biyar ne kuma kacal za a yi ma wa.


Wannan walimar babba ce sosai, wadda tana d'aya daga cikin walimu manya da za a gudanar a jihar Katsina.


Akwai manya manyan ba'ki wanda zasu halarci wannan walima, ciki kuwa har da gwamnan jihar, da wasu daga cikin masu fad'a a ji dake jihar.


Bakin Amrah bud'e yake, saboda kusan in ce ta kai shekara d'aya tana shirin tarar walimar, ta jima tana shirye shiryen yanda walimar zata kasnace.


Cikin jerin mutanen, Annur ne zaune cikin wata farar shadda, d'inkin babbar riga wanda ya amsa sunansa.


Bakinsa a bud'e yake, yana mai bibiyar duk wani motsi na Amrah, har a lokacin da aka fara gabatar da walimar.


_Kar mu yawaita dukan yaranmu masu sickler, saboda ita d'in cuta ce wacce take bin duk wasu k'asusuwa na jiki, take rage masu armashi, take neman dagula al'amurransu. Matuk'ar muka daki yaronmu, k'ashinsa zai iya samun matsala, wanda a k'arshe za a dawo ana regretting. Mu kula da kyau, sai mu san hanyar da zamu bi wurin horonsu._


A yi hakuri da ni, an mana ruwan sama ne wanda ya guyara mana wutarmu, abin dai sai hamdala.


Pinky durling💗
*RAZ 2*
[8/30, 3:34 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


1⃣5⃣


Bayan gabatarwa da aka saurara daga shugaban makaranta, sai sauraran karatun littafi mai tsarki daga d'alibai.


Amrah ce ta k'arshe, inda ta karanto wasiyyoyi da Allah mad'aukakin sarki Ya lissafo a cikin suratul an-am.


K'ira'a ce mai matuk'ar da'di, tamkar d"iyar larabawa haka take rero karatunta.


Bayan ta gama ne ta koma mazauninta, inda aka tanadar domin zaman mutum biyar d'in da suka hardace littafi mai tsarki.


Daga nan sai da wasu d'alibai suka fito suka rero 'yan wa'kok'i irin na larabawan nan masu matuk'ar dad'i, sannan ne aka kira Amrah, in da zata kira d'alibanta domin gabatar sa dirmar da ta shirya masu.


Babban abin burgewa a cikin wannan dirama shi ne; yanda yaran suke k'ananan yara, duk cikinsu babu wacce zata haura ma shekara bakwai a duniya.


Bayan sun kammala da harshen larabci ne, Amrah ta kar'bi loud speaker domin yin bayanin abubuwan da dramar ta k'unsa da harshen hausa.


"Kamar yanda muka gani, yara ne biyu a matsayin ma'aikatan asibiti, sai kuma yarinya d'aya wacce ita ce matsayin marar lafiya, ga kuma mutum biyu a matsayin uwa da uba.


Mun ga yanda aka nunar da ciwo yake addabarta, har wani lolacin take fita daga hayyacinta.


Kwatsam wata rana ciwon ya tasar mata, aka kai ta asibiti domin bata taimakon gaugawa.


Likitar farko ta nunar ma iyayen yarinyar cewa ai wannan yarinyar su ma cire rai da ita kawai, domin kuwa tata ta zo k'arshe. Wannan ciwon nata ba na tashi ba ne. Su koma gida da ita kawai su jira lokacin mutuwarta.


A wurin gardama ta b'arke tsakanin iyayen nata, yayin da mahaifiyarta mace ta kafe a kan bata yarda da maganar likitan ba, domin kuwa babu wanda ya san gaibu sai Allah. Sannan kuma ita cuta ba mutuwa ba ce.


Mahaifinta kuma ya kafe cewa lallai sai dai su koma gida, saboda shi d'in dama ya gaji da kashe mata kud'i a banza kullum ciwo sai ta'azzara kawai yake.


Likitar ganin cece-kuce d'insu ya dame ta ya sa ta kore su daga ofishinta.


Gida suka wuce kai tsaye, har a lokacin mahaifiyar yarinyar bata cire tsammani ba.


Washe gari ta d'auke ta ta kai ta wata asibitin, inda suka tarar da d'ayar likitar can.


Ta mata bayanin lalurin yarinyar, take ta gamsu da bayaninta.


"Babu komai, ki kwantar da hankalinki, insha Allahu zata samu lafiya. ita cuta ai ba mutuwa ba ce, abin da nake so da ke dai kawai ki dage da yi ma 'yarki addu'a. Na miki alk'awarin kula da ita tamkar yanda zan kula da 'yata da na haifa da cikina."


Sosai mahaifiyar yarinyar ta ji da'di.


Haka wannan likitar ta ringa kula da yarinyar kamar yanda ta yi alk'awari. A k'arshe yarinyar ta tashi da k'afafuwanta, ta warke tas kamar bata tab'a yin ciwo ba.


Sai ga yarinyar da taimakon mahaifinta, ta zama rufin asirinsa, ta zama abar alfaharinsa a k'arshe.


Idan zamu auna wannan diramar, mu mata karatun ta natsu, zamu ga akwai tarin darussa a cikinta. Akwai abubuwan koyo da dama a cikinta.


Mun ga yanda likitar farko ta yanke k'auna daga rahamar mahalicci, bayan kuma Allah mad'aukakin sarki maji rok'on bayinSa ne.


Mun ga yanda likitar ta nuna masu tamkar ta san gaibu ne, bayan kuma La ya'lamul-gaibu illallah.


Daga cikin darussan wannan diramar, mun tabbatar cewa duk inda ake ba duka ake taruwa a zama d'aya ba.


Kamar yanda likitar farko ta kore su, sai gashi Allah ya had'a su da ta kirki. Ke nan dai kar mu zama masu yin jam'i ga komai, domin kuwa komai za a iya samun banbanci.


Mun 'karu da ilimin lallai cuta ba mutuwa ba ce, ganin mutum yana fama da ciwo, ba shi ba ne zai sa a yanke k'auna, domin kuwa Allah'n da Ya bashi ciwon, zai iya kawo masa sau'ki a ko wane lokaci. Sannan kuma kafin a saukar da cuta, sai da aka saukar da maganinta.


Duk irin ciwon da mutum yake fama da shi, kar ya zama mai gajen ha'kuri ga mahaliccinsa, ba wai rashin so ba ne ya sa ya d'ora masa cutar, a'a, yana neman ya k'ara kusanci gare Shi ne.


Yanzu idan muka d'auki wani misali; zamu ga so tari mutum yana fama da ciwo, a lokacin da yake ciwon, yana yawaita ambaton Allah, sallah a lokacinsa baya wuce sa. Ba dan komai ba, sai dan yana gudun kar mutuwarsa ta zo d'aukarsa bai gyara tsakaninsa da mahaliccinsa ba.


Amma idan zamu d'auko sanda baya ciwon, wata k'ila yana kwanaki bai yi zikiri ba, ita kanta sallar k'ila kullum sai lokacinta ya wuce yake yinta.


Ke nan wannan jarrabtar da Allah Ya d'ora masa na ciwo, ya k'ara kusanci a tsakaninsu.


Ina fatan wannan 'yar tak'aitacciyar dramar zata zama gyara a rayuwar mutane da dama wanda suka halarci wannan walima da ma wanda zasu kalla a gidajen talabijin.


Duk wanda suka zo wannan wuri, Allah Ya albarkaci rayuwarsa, Allah Ya biya masa duk kanin buk'atunsa na alkhairi.


Mun gode k'warai da gaske."


A lokacon da Amrah ta koma mazauninta, na ga da dama daga cikin mutane wasu na kuka sosai, wasu na share hawaye, wasu kuwa kallo guda zaka masu ka tabbatar lallai jikinsu ya yi sanyi k'warai da ainun.


Babban abin da ya fi tab'a min zuciya a kan bayananta shi ne; nata lalurin, yanda take fama da nata cutar a ko wane lokaci, amma a hakan ta gode wa Allah, har take nunar wa mutane muhimmacin d'aukar k'addara.


A lokacin na k'ara tabbatar da rayuwar Amrah mai kyau ce, kuma abar a yi koyi da ita.


Bayan an gama bayar da kyaututtuka ne aka bu'kace ta da ta fito, gwamnan jihar ya bata kyautar kujerar Makka, sannan da tarin envelopes wanda manyan mutane da dama suka aiko mata da ita. A dalilinta, an ba makarantarsu kyautar naira miliyan d'aya.


Murna sosai ga mutane, Amrah wadda ke jin abun tamkar a mma farki ta kasa furta komai, da gudunta ta isa inda nake, ta min rungumar da ke k'ara shauk'i a tsakaninmu, ina jin yanda bugun zuciyarta ke tafiya dai-dai yanda ake sonshi, hawayen farin ciki basu daina sauka bisa kumatunta ba.


Jin an sake kiran sunanta ya sa ta saurin sakina had'e da mayar da kallonta ga inda loud speaker ke fitowa.


"Ta sake samun kyauta daga wani bawan Allah. Wanda shi ya san lalurinta, ya bada izinin duk sanda ciwon nata ya tashi, kai tsaye ta je asibitin kud'i ta Dr. Dara, ba tare da an caje ta ko sisi ba.


Bawan Allah'n ya buk'aci kar a fad'i sunansa."


Wani kyakkyawan hawaye ne ke sake fita daga k'wayar idonta, saurin isa matakalar ta yi, ta karb'i takardar da aka bata, wacce ita zata zama shaidarta a duk sanda zata je asibitin.


Shugaban makarantar da kanshi ya mik'a mata loud speaker, cewa ta yi kalaman godiya had'e da bankwana, kamar yanda dama can haka aka tsara, ita ce zata yi su.


Da larabci ta ringa zubo bayani, cikin k'warewa tamkar dama can harshenta ne larabcin, bayan ta gama ne kuma ta koma da harshen hausa.


"Kalamai ba zasu iya fad'in iya halin farin cikin da muke ciki ba yau.


Babban abin farin ciki a fa'din duniyar nan, shi ne yau mutum ya wayi garinsa da hardace littafi mai tsarki baki d'ayansa, sannan kuma yake amfani da shi.


Mai girma gwamnan wannan jiha, mai girma wakilin sarki Mukhtar, manyan mutanen da suka halarci wannan taron, iyayenmu, yayyenmu, k'annenmu, a madadin wannan makaranta da d'aliban da ke cikinta, ina mai amfani da wannan dama domin mik'a sak'on godiyarmu. Mun gode k'warai, Alllah Ya saka da alkhairi, Allah kuma ya mayar da kowa gidansa lafiya.


Mu kuma Allah ya bamu ikon amfanar da kanmu da kuma al'ummah abin da muka karanta.


Rabbi Ya sa mai amfani ne a gare mu. Ba wai mun koya, mun hardace kuma mu barshi ya tafi a haka nan ba.


Mu sani cewa, matuk'ar muka sake bamu karantawa, to tabbas zamu neme shi daga kanmu mu rasa.


Na gode."


Ta mik'a sifikar ga shugaban makarantar.


Kabbara aka d'auka da k'arfi, wasu na k'ok'arin tashi domin barin wurin, wasu kuma sun bari har sai an yi addu'a sannan.


Sai bayan an fara watsewa sannan Hajiya Suhaila ta zo, cikin rashin jin dad'i take shaida min abin da ya hana ta zuwa da wuri, Baban su Annur ne zai tafi Abuja, kuma bai tafi da wuri ba.


Tare muka rankaya muka koma gida, ni da ita da k'annena Zulaihat da Fatima a cikin motarta, sai Amrah, da wasu k'awayenta mutum hud'u suka bi motar Annur, wanda murna ta kasa b'oyuwa daga kyakkyawar fuskarsa, yana mai matuk'ar jin dad'in wannan lokacin.


Bayan mun koma gida ne mutane suka ringa zuwa yi mana murna, gida ya cika sosai kamar ana biki ko suna.


D'inkuna kala biyu Hajiya Suhaila ta yi ma Amrah, masu matuk'ar kyau da tsada.


Haka rabar ta kasance mana, farin ciki sosai da murna, shi kanshi Mallam abin ya k'i b'oyuwa, a k'ofar gida aka shimfid'a masa manyan tabarmi shi da 'yan uwa da abokansa.


Bayan wata d'aya.


A lokacin ne shugaban makarantar su Amrah ya zo har gida a kan maganar kujerar Makkarta, wai maganar ta taso, har ma an ce ta zo za a mata passport nan da kwana biyu.


Sanda maganar ta riskemu a gida, sam! Amrah ta ce ita ba zata je ba. Wai sai dai ni ko mahaifinta wani ya karb'i kujerar, ba zai yiu ita ta je mu kuma bamu je ba.


Daga ni har mahaifinta sam muka k'i kar'bar wannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login