Showing 12001 words to 15000 words out of 201092 words

Chapter 5 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt

ta biyar da ita, amma ta tsaya tana fad'a mata maganganu, tana mata rashin kunya.


Wallahi, Allah ne Ya kyauta. Da a ce na tarar da su, suke mata fitsara, da duk abin da zai faru sai dai ya faru. Dan wallahi marin yara zan yi, in yaso sai mahaifin nasu, Alhaji Iqra Al-Hussein ya sa a d'aure ni, a kashe ni."


Mallam ya ce,


"Sai hak'uri ai. Komai na duniyar nan, sai ana kai zuciya nesa. Wata rana sai labari."


"Haka ne." Na fad'a had'e da share hawayena.


Pinky durling💗
*RAZ 2👌🏻*
[8/30, 3:31 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


0⃣9⃣


Jinjinar ban giram ga 'Yan *RAZ NOVELLA.* Fatan alkhairi a ko da yaushe. Na gode da k'warin guiwar da kuke bani. Keep it up dearies.❤


***


Haka dai muka yi yammacin wannan rana, baki d'aya rayukanmu, sun yi bak'i k'irin. Hankulanmu sun dagule.


Ko da dare ya yi, na ke ma Mallam magana cewa,


"Ni ina ga kaman mu dakatar da Annur daga zuwa gidan nan, hakan ne kawai zai saka mu a cikin kwanciyar hankali.


Ba zata yiu a ce saboda shi ana cin zarafinmu ba, k'aramar k'anwata tana fad'a min magana son ranta."


Mallam ya nisa, ya ce,


"Hakan da kika fad'a sam! Ba shi ba ne mafita.


Idan Annur ya zo gidan nan, korarsa zamu yi?


Kina ga kamar mun masa adalci idan muka hana shi zuwa inda muke?


Annur yaro ne har yanzu, wanda bai mallaki hankalin kansa ba.


Ya kamata mu masa uzuri, tun da ba shi ya miki ba, hasali ma, shi kanshi bai ji dad'in lamarin ba.


A ganina, idan har ya zo muka dakatar da shi daga zuwa, ba mu kyauta masa ba.


Ki duba ki ga sha'kuwar da ke tsakaninsa da yarinyar nan, ki ga halin da yake shiga duk sanda bata da lafiya. Kina ganin mun masa adalci idan muka raba shi da ita a lokaci guda?"


Share hawayen da suka zame min abinci, a duk yammacin ranar na yi, na dube shi, na ce,


"Mallam wannan fa abu ne wanda ya shafi martaba da mutuncinmu.


Matuk'ar muka bar yaron nan yana ci gaba da zuwa, bamu san me gaba zata haifar ba.


Idan yanzu yayarsa d'aya da k'anwarsa ne suka zo, gobe bamu san wa zai zo ba.


Wata k'ila mahaifiyarsa da mahaifinsa ne zasu zo.


Amma idan muka hak'ura da shi, shi ma sai ya ha'kura da Amrah, tun da dama tun asali bai santa ba bata sanshi ba. Kowa sai ya zauna a inda Allah Ya ajje sa."


"Gaskiya kika fad'a Murjanatu. Sai dai kuma fa ni ba zan ta'ba iya korarsa idan ya zo ba.


Zan dai bar miki wannan aikin, sai ki san yanda zaki yi da shi."


Daga nan ya gyara kwanciyarsa, ya tofa addu'ar bacci.


Ni ma kwanciyar na yi, amma fir-fir bacci ya k'i d'auka ta.


Da zarar na runtse idona, sai in tuna abin da Saddiqa da Islam suka mana.


Da zarar na fara tunanin yanda zan hana Annur zuwa, sai wata zuciyar ta nusar da ni darajar hak'uri.


Baki d'aya sai in ji zuciyata ta yi sanyi, ba zan iya tsayar da shi ba.


Ko ba komai Annur ya gama min komai, ya nuna tsantsar soyayyarsa ga gudan jinina, ya d'aura damuwarsa a kanta, ya sadaukar da lokacinsa a kanta.


Na masa adalci idan na raba su? Ita kanta Amrah, na mata adalci idan na tsayar da farin cikinta daga zuwa inda take?


Kuka sosai nake, wanda na kasa tsayar da su, na kasa tantance ko na menene. Shin, na damuwar abin da ya faru ne? Ko kuwa na tausayin halin da Annur da Amrah zasu shiga idan suka daina ganin junansu ne?


Na sani sarai, ta Amrah mai sauk'i ce. Akwai yarinta a tattare da ita, ba zata jima ba zata iya mancewa da shi. Shekara d'aya ma idan ta d'auka bata ganinsa, zata manta da halittarsa a doron k'asa, matuk'ar ba maganarsa nake mata ba.


Shi kuma fa? Zai iya mantawa da ita? Ko kuwa zai iya cire k'aunarta daga zuciyarsa?


Kaina na dafe, had'e da had'iyar yawu da k'yar, na mi'ke tsaye.


Ko da na duba tsohuwar agogon da ke jikin bango, k'arfe sha biyu da rabi na dare ne.


Fitila na kunna, sannan na fita daga d'akin.


Ban-d'aki na nufa, na d"auro alwala sannan na dawo cikin d'aki, na hau jera sallolin da ko ni ban san adadinsu ba.


Ba ni ce da tashi ba sai kusan k'arfe ukun dare, sannan na hau gado, babu jimawa bacci ya d'aukeni.


Washe gari da safe, ina ta tsammanin zuwan Annur kamar yanda ya fad'a, amma sai bai zo ba, har goman safe ta wuce.


Ban yi mamaki ba, dan na san dama ba lallai ba ne ya zo, duk kuwa da yanda ya so zuwa d'in.


Abu wasa ba wasa ba, har aka yi sati biyu babu Annur babu alamunsa.


Tun abun baya damu na, har na fara damuwa.


Amrah kuwa, sunan da na koya mata take kiransa da shi, take yawan fad'i cike da damuwa,


"Hamma!" Take fad'i dare da rana. Wani lokacin tana kuka, wani lokacin kuwa har hijabina take d'aukowa tana bani, tana fad'in sunan Hamma, manufarta wai in kai ta inda yake.


Shi kanshi Mallam abin ya dame shi.


Ranar da Annur ya cika sati biyu bai zo inda muke ba, ya same ni da maganar, a tsakar fida da wani yammaci,


"Raina yana matuk'ar b'aci, zuciyata tana yamutsa, kaina yana dagulewa, a duk sanda na tuna da yaron nan.


Ban san me ya sa ba, ina jin rashinsa har cikin zuciyata.


Ina k'aunar Annur, ina tsannain kewar rashin zuwansa gidan nan.


To ni ma ke nan, ina ga Amrah? Ya take ji? A haka kuma dole ta bar abin a ranta, saboda yarintarta."


Baki d'aya jikina ya yi sanyi da kalamansa, ni kaina ina jin rashinsa har cikin raina, musamman ma idan Amrah na kuka, tana nemansa.


"Mallam ban san..." na dakata daga nan, saboda tozali da idanuwana suka yi da wanda muke kan maganarsa.


Da sauri Amrah ta ruga ta isa gare shi, ta rungume shi sosai kamar wani zai k'wace mata shi, tana fad'in,


"Hamma..." sai kuma ta yi shiru, ta sake kallonshi ta k'yalk'yale da dariyar da ke nunar da tsantsar farin cikinta.


A yanayinsa, dole mutum zai fahimci damuwar da yake cikinta.


"Sannu Annur." Na fad'a ina masa murmushi.


"K'ariso ka zauna mana Annur, zo ga tabarma nan." Mallam ya fad'a tare da gwada masa kusa da shi.


Zama ya yi yana d'auke da Amrah, ya gaishe mu.


"Kamar kana cikin damuwa, lafiya dai ko?"


Na tambaye shi.


"Umma akwai damuwa..." ya fashe da kuka mai tsuma zuciya, wanda har sai da ya karya min zuciya.


"Daddy'na ya ce zai mayar da ni Cyprus, inda Aunty Nadrah take aure.


Su Aunty Saddiqa ne suka kai masa zuga, wai bana karatu, kuma bana zuwa School, kullum wai ina nan gidan, wurinku.


Dady'na mutum ne mai son ilimi, yana son mu yi zurfi a karatu. Hakan ya sa ya yanke hukuncin tura ni can wurin yayata, wai in ci gaba da karatu a can, har lokacin da zan mallaki hankalin kaina.


Mamana kanta hakan bai mata dad'i ba, saboda yanda ta kula da bana so, ita kuwa tana son abin da nake so." Ya yi shiru daga nan, saboda kukan da ya ci k'arfinsa.


Da k'yar ya iya ci gaba da,


"Bana son rabuwa da Amrah, na so na kasance tare da ita, na kula da ita ko dan ciwon da take tattare da shi.


Na so a ce ta girma a gabana, in kula da ita, in k'aunace ta kamar yanda yayanta na jini zai mata.


Sai dai kuma kash! Hakan ba mai yiuwa ba ne, an b'ata min tsarina a kan yanda na so gina rayuwata."


Ya share hawayensa da hab'ar rigarsa, sannan ya ci gaba,


"Ina son Amrah, Ummah. Bana son abin da zai raba ni da ita. Ina so ku min wata alfarma guda d'aya, wacce in har kuka min ita, kun gama min komai."


Cikin kuka na ce,


"Ina jin ka Ann..nur.." na yi k'ok'arin shanye kukan da ke son hana ni magana.


"Kasantuwar Amrah yarinya ce, wacce babu wuya zata iya mantawa da ni.


Ina son ku yi bakin k'ok'arinku, na ganin bata manta da ni ba.


Na sani abu ne mai wahalar gaske, amma ina son ku min wannan alfarmar."


Cikin k'arfin hali da nuna jarumta Mallam ya ce,


"Na maka wannan al-k'awarin, Annur. Da yardar Allah Amrah ba zata tab'a mantawa da kai ba.


Zata sanka ko da ba a baki ba, a suna ma kawai.


Zamu ringa k'ok'arin sanar da ita irin halaccin da ka mata a yarintarta."


Sallama muka ji, muryar wani dattijo ne.


Mallam ya amsa sallamar had'e da mik'ewa yana shirin fita.


"Annur baku gama ba? Har Yallab'ai ya kira ni yanzu, na ce masa motarmu ce ta d'an tsaya." Mutumin ya fad'a da d'an k'arfi, yanda Annur zai ji.


"Ina zuwa Baba Amadu."


Ya kama hannuwan Amrah duka biyun, kuka sosai yake, kamar wanda aka duka.


Ita ma Amran kaman ta san abin da yake faruwa, ta dai gan ni ina kuka, ga kuma babban abokinta ma yana yi. Kukan take sosai kamar ranta zai fita.


"Ina k'aunarki Amrah. Ban so a raba mu ba a dai-dai wannan lokacin.


Na so na kasance tare da ke, na so na kula da lafiyarki, amma Allah bai nufa ba.


Dan Allah Amrah kar ki manta da ni, kar ki manta da Annur Iqra Al-Hussein a rayuwarki.


Ga wannan, kud'ina ne da abokin Dady'nmu ya tab'a bani sanda na je gidansa kwanakin baya, babu wanda ya san da su, ko Momy'nmu kuwa. Ina ta ajiyarsu ne, kamar na san abin da zai faru.


Naki ne halak malak, duk sanda wata buk'atarki ta taso, tun daga kan magani har sutura, a miki amfani da su." Ya zaro rafar dubu d'ari daga cikin wata bak'ar leda, ya damk'a ta ga Amrah.


"Na tafi. Sai wata rana.." kuka ya ci k'arfinsa.


Da gudu ya bar gidan, mallam na k'iransa amma ko waigowa bai yi ba.


_My fans, how was this chapter? Very touching ba? Soyayya ke nan. Comments d'inku yana 'kara min k'warin guiwa a ko wane lokaci. Amrah loves you irin over d'in nan.😍_ share to your friends


Pinky durling💗
*RAZ 2👌🏻*
[8/30, 3:31 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


1⃣0⃣


Wani irin kuka na fasa tamkar k'aramar yarinya, wanda duk jarumtar Mallam kasa bani hak'uri ya yi, shi kan shi kukan zuci yake, wanda a fuska kawai zaka iya fahimtar haka.


Jawo Amra da ke kuka kamar ranta zai fita na yi, na d'ora a cinya sai faman rurrugarta nake. Cikin kuka na ce,


"Ki yi ha'kuri Amrah. Duk da ba lallai kin san abin da yake faruwa ba, sai dai na san dole jikinki zai baki, rashin masoyinki na gaskiya.


Annur ya tafi ke nan, bana tunanin zai sake waiwayarki.


Ba wai ke kad'ai ba, ni kaina cike nake da zullumin kewar Annur da na tabbatar sai na yi ta.


Sati biu kawai da ya yi bai zo ba, ji na yi kamar in bi shi. Gashi yanzu zai yi tafiyar da ba lallai na sake ganinshi ba.


Tabbas Annur yaro ne d'an halak, wanda samun kamarsa zai yi matuk'ar wahala a dai-dai wannan lokacin.


Shekararsa goma sha uku, amma halayensa kamar sun fi na yawan mai shekarun nasa."


Na kuma fashewa da wani kukan, zuciyata sai tafarfasa take, ina jin kamar na kira Annur ya dawo gare mu, kamar na hana sa wannan tafiyar.


Sai dai kuma bani da yanda zan yi, domin kuwa k'addara ta rigayi fata.


Hukunci ne wanda mahaifinsa ya yanke, bani da yanda zan yi face hak'uri.


*BAYAN SHEKARA TAKWAS*


A dai-dai wanan lokacin ne Amrah ta cika shekara goma a duniya.


A iya tsawon wannan shekaru, wahala iya wahala tana yinta, saboda baki d'aya yanda muka d'auki sickler d'inta ba haka ba ne.


Wahala sosai take bata, ashe irin mai tsananin nan ce da ita.


Kullum cikin zarya asibiti muke, tun muna damuwa, har Allah Ya saka mana tawakalli a zukatanmu. Ita kanta yarinyar, ta saka ma ranta dangana.


Ranar wata laraba, da yammaci, misalin k'arfe shida na yamma,


Da gudu Amrah ta shigo, har tana cin tuntub'e.


"Umma.." ta fad'a cikin shesshekar gudu.


"Bi a hankali mana Amrah. Na sha fad'a miki cewa ki daina irin wannan gudun, wanda har zai sar'ke ki amma bakya ji. Me ya faru ne?"


"Umma wata mata ce, gata can sun faka motarsu a k'ofar gidanmu."


Dafe baki na yi, na ce,


"To fa! Wannan wace mata ce a cikin mota haka? Ko ta yi b'atan hanya ne? To Allah dai Ya sa lafiya."


Tun bamu kuma fad'in komai ba sai ga ta ta shigo ciki.


Mahaifiyar Annur ce, sanye cikin kaya na al-farma.


Fuskarta a sake ta yi sallama, sannan ta k'ariso daga ciki


"Marhabun da Hajiya Suhailah. Maraba maraba. Iso mana Hajiya."


Da fara'arta kuwa ta iso inda nake, ina k'ok'arin shimfid'a mata tabarma amma ta dakatar da ni,


"Ga kujera nan bari na zauna a kai kawai, babu damuwa ai." Ta sakar min murmushi.


Zama na yi a k'asa, na gaishe ta ta amsa da sakin fuska.


"Maman Amrah kin gane ni kuwa?" Ta fad'a tana kallo na.


"K'warai ma kuwa Hajiya. Ba mahaifiyar Annur ba ce?"


Jin na ambaci Annur ya sa da sauri Amrah ta iso gare ta, ta duka har k'asa ta gaishe ta.


"Lafiya k'alau Amrah. Lallai yarinya ta girma k'warai da ainun.


Ya k'arfin jikin naki?"


"Alhamdulillah! Jiki ya yi sau'ki sosai Mama. Ina fatan tare kuke da Ya Noor, saboda a ko da yaushe Ummah ce min take wai Ya Noor zai dawo gare ni, kuma gashi har yanzu bai dawo ba." Ta b'ata fuskarta alamun damuwa.


Dafa kanta Hajiya Suhailah ta yi, ta murmusa sannan ta ce,


"Annur zai dawo insha Allahu nan ba da jimawa ba. Ke dai abin da nake so a gare ki, kawai ki dage da addu'a. Allah ya shawo kan Dady'nsa, ya amince ya dawo gare mu.


Ni kaina ina cike da kewar yarona, ina son ya dawo ya ci gaba da rayuwa a gabana."


"Mama, har cikin zuciyata nake jin Ya Noor, nake mararin ganinsa.


Duk da ban sanshi ba, ba zan iya tuna komai game da shi ba, amma fa ina jin sa har cikin raina, kamar yanda na tabbatar shi ma ina ransa.


A yanda nake jin labarinsa a bakin Ummana da kuma Abbana, Ya Noor mutumin kirki ne, wanda ya nuna min zallar soyayya, ya kula da ni, sannan kuma ya bani lokacinsa.


Dan Allah Mama, ko a hoto ne ki gwada min shi, yau rana d'aya tal, in ga fuskar wannan bawan Allah, mai tarin halayen kirki.


Shekaru kusan hud'u ke nan ina fatan na ganshi ko da a mafarki ne, ko kuma a hoto, amma Allah bai karb'i du'a'ina ba, sai ga ki yau Allah ya kawo ki har inda muke."


Murmushi Hajiya Suhailah ta yi, ta ce,


"Abin da ya kawo ni ke nan Amrah.


Annur ya jima yana rok'ona a kan na zo gidanku, na had'a ku ko da a waya ne ku gaisa, amma ina guje wa maganarsa. Ba dan komai ba, sai dan sanin halin Dady'nsa da na yi. Matuk'ar ya fahimci wani abu to komai zai iya faruwa, saboda shi d'in bai had'a ilimin yaransa da komai ba.


Ganin halin damuwar da yake a ko da yaushe, ya sa yau na amince da buk'atarsa, zan kuma yi masa yanda yake so." Ta sake yin wani murmushin had'e da zaro wata leda mai d'an girma daga cikin jakarta.


Mik'o ta ta yi ga Amrah, ta ce,


"Waya ce wannan ya sa na siya miki, wai yana son ku ringa waya a kai a kai, kuna gaisawa, yana kuma jin halin da kike ciki.


A cikinta akwai hotunansa da dama ya turo, idan kin bud'e zaki gani."


Tsalle Amrah ta yi cike da murna ta karb'a wayan, a k'irjinta ta d'ora sai faman fara'a take, ta ma kasa furta komai tsabar murna.


"To ke baki iya godiya ba ne?" Na fad'a cike da mamakinta.


"A'a maman Amrah, bar ta ta yi murnanta. Shi d'in ma ya ji dad'i sosai sanda na amince masa." Ta fad'a had'e da mik'ewa.


"Ni zan wuce, sai kuma Allah ya sake dawo da ni. Sannan kuma ina neman wata al-farma a wurinku."


Da sauri na ce,


"Allah Ya sa zan iya, Hajiya."


"Dan Allah ki ringa turo min Amrah tana gaishe ni, lokaci zuwa lokaci.


Ina son yarinyar, ko dan soyayyar da Annur yake mata, ita ma kuma take masa.


Sannan kuma duk sanda kuke da wata matsala ko kuma damuwa, kar ki ji komai, dan Allah ki same ni da maganar, insha Allahu zan warware miki ita.


Amrah dai 'yata ce tamkar Annur, yanda nake jinsa haka ita ma nake jinta a raina, banbancinsu ba wani mai yawa ba ne.


Dalilai da dama ne suka hana ni waiwayarku, tun bayan tafiyar Annur.


Ciki kuwa har da rayuwar k'unci da na shiga, a lokacin da aka tafi min da yaro. Na ji a raina, bana son ganin duk wani abu da ya dangance shi, saboda tuno min da shi da yake.


Baki d'aya komai na shi na kyautar, saboda bana son gani.


Shi ya sa na ji ba zan iya zuwa wurinku ba, guje ma tada tabon da ke k'ok'arin warkewa.


Hatta da abokanansa na hana su zuwa inda nake, saboda gani nake idan har suka zo, zana ringa masu kallon kamar zan ga Annur a tare da su, bayan kuma ba haka ba ne.


Abu na biyu kuma, rabamu da ku da Dady'nsa ya yi, ya mana iyaka da ku ne saboda yaronsa, kuma na san halinsa sarai, matuk'ar ya ga wani abu yana shiga a tsakaninmu, to tabbas komai zai iya yi maku..."


Da sauri na dakatar da ita, jin ta yi wannan maganar ya sa na ce,


"To kuma Hajiya a haka ne kike so Amrah ta ringa kai miki ziyara?"


Murmushi ta yi,


"Ko za a tsare Dady'nsu a ce ya gwada Amrah bai santa ba. Bana ji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login