Showing 15001 words to 18000 words out of 201092 words

Chapter 6 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt

ma ko sunanta ya rik'e har tsawon wannan lokacin.


Kuma shi 'din ba mazaunin gida ba ne, yana da manya manyan kamfanoni a Kaduna, da kuma Abuja, wanda suka danganci magani.


Kin ga kuwa ina ya ga wani lokacin zama gida, bare har ya kula da masu shiga da kuma masu fita? Har kuma ya iya tantance Amrah, a matsayin yarinyar da Annur ke so, har ya sadaukar da lokacin karatunsa a kanta?


Kar ki ji komai Maman Amrah, wannan mai sauk'i ne.


Ni dai kam ina son Amrah, kuma na miki al-k'awarin zuwanta inda nake ba zai tab'a saka ku da na sani ba, face shak'uwa da zata k'ara shiga tsakaninta da Annur, wanda nake fatan ya kai su ga yin aure duk sanda suka gama mallakar hankalin kansu."


Ajiyar zuciya na sauke, sannan na ce,


"To Hajiya, su kuma fa 'yan uwansa?


Ina nufin Saddiqa da Islam. A sanina dai su ma d'in basa k'aunar Amrah, saboda suna ganinta d'iyar marasa arzik'i.


Kina ganin kamar ba zasu ci zarafinta ba idan tana zuwa gidansu?"


Komawa ta yi ta zauna daga kujerar da ta tashi, ta ce,


"Maman Amrah ke nan. Ai Saddiqa ta dad'e da yin aure, kusan shekara bakwai ke nan, tana Bauchi a can take aure. Yanzu haka yaranta biyu fa.


Islam kuma tana India, a can take karatun medicine. Bata zuwa k'asar nan sai bayan shekara guda guda.


Dan haka dan Allah kar ki damu. Ina son Amrah ta shak'u sosai da ni, in bata gatan da ban ba ma yarona Annur ba."


Sai a lokacin na samu kwanciyar hankali, na murmusa,


"To insha Allahu kuwa Amrah zata ringa zuwa tana gaishe ki duk ranar jumu'a.


Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba,


Kin san ita d'in yarinya ce mai yawan ciwo, saboda sikilar da ke gare ta


Da wuya ta cika sati d'aya da lafiya, ba tare da mun je asibiti ba.


Kin ga ke nan, ba ko yaushe ba ne zata samu damar zuwa, saboda yanayin jikin nata."


Hajiya Suhailah ta ce,


"Haka ne Maman Amrah. Ina mata fatan samun lafiya. Uban-giji ya bata lafiya, ya kawo mata k'arshen wannan wahala ta ta."


"Amin." Na fad'a sannan na mik'e, ganin ita ma d'in ta mik'e.


Hijabina na ciro daga bisa igiya, na saka.


"Amrah ba zaki mata bankwana ba?"


Na fad'a ina kallonta.


Kunya ta ji da gudunta ta shige dak'i, wai tun daga sanda Hajiya Suhaila ta ambaci aure a tsakaninta da Annur.


Har k'ofar gida na raka ta, wata irin b'arkekiyar mota ce aka kawo ta ciki, wadda daka ganta ka san lallai naira ta zauna masu.


Sai da ta shiga mota sannan muka sake yin bankwana na dawo gida, zuciyata cike da k'aunar matar, ta matuk'ar burgeni.


Yana da wuya a samu matar mai kud'i kamar Alhaji Iqra Al-Hussein, kuma tana son talakawa irinmu.


_A yi ha'kuri jiya ba a ji ni ba, mun samu matsalar wuta ne._


Pinky durling💗
*RAZ 2👌🏻*
[8/30, 3:32 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


1⃣1⃣


Ko da Mallam ya dawo na shaida masa abin da ya faru, ba kad'an d'in murna ya yi ba.


Sosai ya nuna farin cikinsa a fili, dan a zahirin gaskiya, zan iya cewa Mallam ya fi ni damuwar rashin Annur.


"Amrah kawo wayar mu ga" ya fad'a yanda zata ji, saboda tun sanda Hajiya Suhailah ta tafi Amrah bata sake fitowa ba, sai yanzu da mallam ya shigo ake kiran sallar magrib.


Fitowar kuwa ta yi, hannunta rik'e da kwalin wayar.


"Ga ta Abbah.." ta mi'ko masa.


Kar'ba ya yi kuwa, nan ya saka sim card d'in da ke cikin pack d'insa, sannan ya saka batirin ya rufe da marfi.


Waya ce Nokia asha, kalar ja, mai matuk'ar kyau da d'aukar ido.


Kasantuwar Mallam ma yana da waya, ya san kanta, ya sa bai wani sha wahala ba wurin had'a komai yanda ya dace.


Ko da ya kunna, hoton Annur ne a saman walfefar wayar, ya yi wani irin k'ayataccen murmushi.


Kyakkyawar fuskarsa ta amsa wani irin k'asumba, irin wadda matasa ke tarawa take masu matuk'ar kyau.


Gashin kansa kwance yake luf luf, ya tara suma da alamun ya jima bai yi aski ba.


Baki d'aya halittarsa ta gama fitowa, tamkar yaron larabawa haka ya koma.


Da murna k'warai Mallam ya mi'ke tsaye, donshi har yana k'ok'arin kawo ruwa tsabar farin ciki.


"Annur haka ka koma? Allah sarki yarona!" Yana sake kallon hoton.


Da murna ni ma na ce,


"To ka bani nima na gani mana."


Mik'o min wayar ya yi,


"Yaro ya zama saurayi son kowa k'in wadda ta rasa.


Murjanatu taya ni kallo dan Allah."


Kamar wasu kid'mammu haka muka koma, farin ciki kuwa ko d'anmu ne na cikinmu iyakacin wanda zamu yi ke nan.


"Umma kawo ni ma na ga Yaa Noor d'in." Amrah ta fad'a, ita kanta da fara'a k'unshe a saman fuskarta.


Mik'a mata na yi, ta dube shi da kyau.


"Umma ai na san wannan..." ta fad'a cike da mamaki.


"Shi ne Yaa Noor d'in?"


Cike da mamaki na kalle ta, na ma rasa abin da zan fad'a.


"Wallahi Umma da gaske nake na san shi. Yanzu wai baki tab'a kula da shi ba a asibiti idan mun je wani lokacin?"


Mallam ne ya iya fad'in,


"Anya kuwa Amrah? Ko dai mai kama da shi ne kike gani? Annur fa baya k'asar nan."


Sake dubar hoton ta yi, cike da yak'ini ta ce,


"Wallahi Abbah na san shi. Kusan sau biyu ko sau uku ina ganinshi a asibiti.


Ranar farko ma a wurin ganin likita ne na ganshi,


Rana ta biyu kuma cikin keken guragu na ganshi. Na ukun ne dai ba zan iya tunawa ba, amma kam tabbas wannan ne nake gani."


Ganin bil-hak'ki take, ya sa na ce,


"Wai wace irin magana kike ne Amrah?


Kin san shekarar Annur nawa rabonsa da k'asar nan?


Kusan fa shekara bakwai ko takwas ke nan.


Ba a kama ne a duniya?


Wata k'il dai mai kama irin ta shi ce kika gani."


Mik'o min wayar ta yi, ta ce,


"Umma sake duba shi dai sosai. Na yi mamaki ki ce wai baki ta'ba ganinsa ba.


Wallahi Umma duk ganin da nake masa a tare da ke ne.


Har ma fa akwai ranar da ya gaishe ki, kin dai manta ne kawai."


Kallon mamaki kawai muke binta da shi, saboda yanda muke jin zancen nata kamar a wasa, ga ta ita kuma da gaske take, har tana dagewa rantsuwa.


"Umma ashe dama shi ne Ya Noor d'in. To ni dai gaskiya na yi fushi da shi.


Ashe yana ganina kuma baya min magana ko? Bayan kuma ya san ina cike da kewarsa, ina son ganinshi sosai." Ta b'ata fuskarta cike da damuwa.


Kamo ta na yi na zaunar a kusa da ni,


"Amrah! Ki cire tunanin Annur ne kike gani a asibiti.


Na fad'a miki cewa ba shi ba ne, Annur baya k'asar nan fa.


Kin san ana kamanni a duniya, ta yiu ke kamarsu ce kika gani, bare kuma wannan a hoto ne.


Dan haka ki daina wannan tunanin, ta ya Annur da yake mararin ganinki, kuma zai ganki ya share ki?


Wannan ba abu ne mai yiuwa ba."


Haka na ci gaba da k'ok'arin ganar da ita gaskiya, amma fa sam ta k'ek'ashe ta k'i yarda da maganata. A k'arshe dai ta nunar min da ta yarda, wanda a zahirin gaskiya ba yarda d'in ta yi ba kuma.


Haka dare ya yi na ringa juya maganganun Amrah, ban san dalili ba, haka kawai na saka ma kalaman nata alamar tambaya, ta yanda kallo d'aya ta ce ta san shi, kuma har take rantsuwa cewa wai ya tab'a gaishe ni.


Washe gari da safe ta yi shirin makaranta. Wata makaranta ce a can k'asan layinmu ta gwamnati take, yanzu haka tana primary 6 ke nan.


"Abba baka kira min Yaa Noor d'in ba fa, kuma kai ka ce yau da safe zaka kra min shi kafin na tafi makaranta."


Da murmushi Mallam ya ce,


"Ai kin ga yanzu fa makaranta zaki je Amra, insha Allahu na miki al-k'awari idan kin dawo zan kira miki shi, tun da akwai kati da kuma lambar wayarsa a nan ciki."


"Oya ki yi ki kammala shan kununki ko? K'osan ya ishe ki?" Na tambaye ta.


"Ehh, ya ishe ni Umma. Na gode."


Bayan ta gama ta zo na saka mata al-barka kamar ko yaushe, na ce,


"A yi karatu da kyau 'yata. Ina miki fatan alkhairi. Allah Ya miki al-barka."


"Amin Ummana. Bara in tafi."


Ta sab'i jakar makarantarta.


Bayan ta kusa isa zaure, ta juyo ta d'ago min hannu tana murmushi, wanda wannan d'ago hannun da ta yi, kawai sai na samu kaina da samun rashin kwanciyar hankali.


Take gabana ya hau dukan uku-uku. Na d'aga nawa hannun ni ma ina d'aga mata har ta fice.


Kallon Mallam da ke shan koko na yi, cikin wata murya mai nunar da fargaba ko kuma shakku, na ce,


"Mallam, kawai sai na samu kaina da rashin kwanciyar hankali a kan tafiyar yarinyar nan. Hankalina ya tashi ban san dalili ba."


Murmushi ya yi, ya ce,


"Murja ke nan. Ban san sai yaushe zaki cire ma ranki irin wannan tunane tunanen marassa ma'ana ba.


Ko kin manta addu'ar iyaye ce a kan Amrah?


Fita goma zata yi daga gidan nan sai kin saka mata al-barka, sannan kuma ki mata fatan al-khairi.


Kin ga kuwa, ai bai kamata ma ki saka wani tunani a ranki ba.


Kin san shi shaid'an ta ko wace hanya yana bi dan ganin ya dagula wa mutum lissafi.


Ki yi ta'awizi ki kore shaid'an, a duk lokacin da tunani irin wannan ya fad'o miki."


Kalaman Mallam suka sa na ji wani sanyi a zuciyata, na kuma samu kwanciyar hankali d'ari bisa d'ari.


"Maganarka gaskiya Mallam. Duk wanda al-barkar iyaye ke biye da shi, to tabbas baya tab'ewa.


Ko da a ce wani abu zai same shi, matuk'ar ya rik'e adhkar d'insa, sannan iyayensa na saka masa al-barka, ko ma me zai same shi, zai zo masa da sauk'i.


To bare kuma Amrah, yarinya 'yar shekara goma, wadda a kullum burinta shi ne ta ga ta faranta mana rai.


Ba wai dan Amrah tana tawa ba, amma wallahi zan iya cewa tun da nake a rayuwata, ban tab'a ganin k'aramar yarinya mai kyawawan halaye da d'abi'un kirki kamar ta ba.


Dama dukkan hani ga Allah baiwa ne, na gasgata wannan zancen.


Gata dai yarinya mara wadatacciyar lafiya, Allah Ya rage ta ta fannin lafiya, amma kuma sai ya wadatar da ita da halaye na gari.


Ina mata fatan d'orewa da wannan halaye nata, wanda nake fatan ko bayan babu ita a doron k'asa, zata zama abar koyi da kuma al-fahari ga al-ummah."


Daga nan wani irin kuka ya kufce min, wanda na rasa gane ko na me nene.


Ajiyar zuciya Mallam ya sauke,


"Haka ne Murja. Amrah kam sai dai mu dad'a godiya ga mahalicci.


Ga ta da k'walwa, tun daga b'angaren Islama har b'angaren boko d'in.


Ta zama yarinyar da duk wani abun da za a yi da ya danganci masu k'ok'ari, to ita ce farkon da za a saka a lissafi.


Idan wata gasa ce za a yi da ita a ciki,


Musab'aka har ta k'ananan hukumomi ta je, ta wakilci Katsina Local Government, sahun 'yan izib goma.


Duka wannan halaye nata sun ginu ne ta dalilinki Murja. Ke ce kika d'ora ta a bisa wannan tafarkin na kirki.


Tabbas! Samun uwa ta gari kamar ki sai an tona, ke jajirtacciyar mace ce, abar al-fahari kuma abar kwatance."


Du'kar da kaina na yi ina wasa da warwaron hannuna, ina k'ara jin tausayin Amrah a cikin zuciyata.


Ba dan komai ba sai dan kasa gafartawa kaina da na yi, saboda na san tabbas mu ne sila, ciwon Amrah tamkar mu ne silarsa.


Tun da inda a ce tashin farko mun yi abin da ya dace kafin aure, da duk hakan bata faru ba.


Sai dai kuma k'addara ta rigayi fata, kamar yanda Dr. Xarah ta fad'a mana.


Da wanann tunanin na mik'e, na tattaro kayana da na Amrah masu datti, zan wanke su.


Mallam ya ce,


"Na ji fa ta rok'e ki al-farmar kar ki yi wankin nan har sai ta dawo ku yi tare, shi ne kuma kika fiddo zaki yi?"


Ajje kayan na yi a k'asa sannan na ce,


"Wahalar da yarinyar nan ke yi ce nake ga kaman zata yi yawa Mallam.


Ka ga fa Dr. Xarah ta hane mu a kan saka ta aiki da yawa, musamman ma wanda k'asusuwanta zasu yawaita motsawa.


Shi ya sa ba zan sake barinta ta yi wanki ba. Girki da shara dai da ba wani wahala ne da su ba, sai in ringa taimaka mata wurin yinsu."


"Ehh to, haka ne kuma.


Ni bara in tashi in nufi wurin k'wadago. A yi min addu'a."


Kallonsa na yi da murmushi na ce,


"Allah Ya kare ka da kariyarSa mafificiya.


Allah Ya baka ikon ciyar da mu da halal.


Fatan al-khairi."


"Ameen." Ya fad'a had'e da tafiya.


Misalin k'arfe sha biyu na gama komai, har gyare-gyaren gida duka na yi.


Muroyoyin yara na ji ana hayaniya sosai, kuma abun na k'ara kusantowa a cikin gidanmu.


Saurin mik'ewa na yi jin sun shigo daga zauren gidan, wasu ma har sun iso daga ciki.


Ko da suka k'ariso na tambaye su, lafiya?


Wata yarinya 'yar za'kal d'insu ce ta yi caraf ta ce,


"Amrah Abdallah ce..." muryarta ta sark'e tsabar sauri da take ta fad'a min.


Cikin tashin hankali na ce,


"Fad'a min me ya faru da Amrata? Me ya samu yarinyata?"


"Wani malaminmu ne ya dake ta sume, har yanzu bata farfad'o...."


"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Na furta ban ko jira ta gama maganar ba.


_Duk wasu masu cutar sickler, tun daga manya har izuwa k'ananan yara, ina masu fatan samun sauk'i. Allah Ya sauk'ak'a masu, Ya kawo rahamarSa a gare su._


*Ku yi comment da AMEEN, Please👏🏻😢.*


Pinky durling💗
*RAZ 2👌🏻*
[8/30, 3:32 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥


(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)


Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*


_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_


1⃣2⃣


Tafiya nake gudu-gudu, sauri-sauri. Baki d'aya hankalina a tashe yake, ban ma san inda nake dosa ba, sai dai kawai na san biye nake da yaran da suka zo fad'in sak'on.


A haka muka isa makarantar, kai tsaye muka nufi ofishin head master tare da yaran.


Amrata na gani kwance tamkar bata numfashi, malamai kusan guda biyar zagaye da ita, wani na tofa mata addu'o'i wasu kuma tagumi suka yi cike da tausayinta.


"Amrah!" Na fad'a a firgice.


"Ku fad'a min dan Allah me ya faru da 'Yata? Me aka mata?"


Na jawo ta na rungume tsam a jikina.


"Wallahi idan har yarinyata ta mutu ba zan tab'a yafe wa hukumar makarantar nan ba.


Tun lokacin da za a saka ta sai da muka zo nan tare da mahaifinta, ya maku bayanin lalurinta, gashi a k'arshe kun kasa kare min yarinya.


Wallahi matuk'ar ta mutu sai na yi shari'a da hukumar makarantar, in ya so sai ku fitar da ko ma wane malami ne ya mata wannan dukan."


Kuka sosai nake, ina sake dubar jikinta da aka farfasa da bulala, har a lokacin jini bai daina kwarara ba.


Wannan yarinyar 'yar zak'al ce ta ce,


"Kuma wallahi Mama ba fa ita ce ta yi laifin ba. Amrah babu ruwanta da kowa, bata fitina, ko fad'a ta ga ana yi a cikin ajinmu ma fita take.


Sai da ta rantse ma Mallam Mu'ammar cewa ba ita ce ya aika ba, amma ya ce wai ita ya aika ta d'auko masa red pen d'insa a staff room, gashi kuma bai ga sabon littafinsa ba, wai ita ce ta sace.


Duka 'yan ajin sai da muka bata shaida, amma bai yarda ba, sai da ya mata wannan wawan dukan."


Kai kawai na gya'da, hankalina a tashe na sab'e ta had'e da mik'ewa.


Ban san ma ya zan yi ba, kasantuwar ban fito da ko sisi ba tsabar tashin hankali.


Wani Malami wanda na tarar yana mata addu'a ne ya ce,


"Mu je na kai ku asibiti a mashin."


Ban musa masa ba, dan bani da wani zab'i da ya wuce na bi sa d'in.


Head master'n ne ya zaro dubu d'aya daga aljihunsa,


"Mallam Hafeez ga wannan, ko da za a buk'aci kud'i."


Ya juyo gare ni,


"Dan Allah Hajiya a yi hak'uri, an yi kuskure wanda k'addara ce kuma ta rigayi fata.


Insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba. Fatanmu dai yanzu ta farfad'o, sannan duk maganar da za a yi a yi."


Ko kallonsa ban yi ba kawai na fice, da sauri malamin da aka kira da Mallam Hafeez ya biyo bayana.


Bakin mashin d'insa ya isa, ya fiddo sannan na hau ina rungume da Amrah.


Tambayata ya yi asibitin da muke kaita na fad"a masa, hakan ya sa kai tsaye muka doshi can d'in.


Muna isa risafshan da sauri na k'arisa inda medical recoarder yake, tsabar yawan zuwa asibiti har ma na hardace lambar katinta, babu b'ata lokaci ya fiddo fayil d'inta.


Ganin tana unconcious ya sa ko tsayawa bin layi bamu yi ba, kai tsaye aka shigar da fayil d'in nata muka shiga wurin likita.


Dr. Rabi'atu ce yau muka tarar, ganinmu ya sa ta zare glasses d'inta cike da tausayi ta ce,


"Amrah jikin dai?"


Ta karb'e ta daga hannuna.


"Ehh..." kawai na fad'a ina son ci gaba da magana amma tashin hankali bai bar ni ba, sai faman kuka nake tamkar yau ne ta fara yin ciwon.


Da k'yar na iya jawo magana daga k'asan mak'oshina, na ce,


"Dr. Tun da yarinyar nan take ciwo bata tab'a irin wannan ba. Duk irin sumar da zata yi bata wuce minti biyar ko goma ta farfad'o.


Amma ki ga wannan, tun d'azu take a haka, ga jikinta ya yi zafi rau kamar garwashi."


Kuka ya sake cin k'arfina.


Ajiyar zuciya Dr. Rabiatu ta sauke,


"To yi hak'uri Maman Amrah, daina kukan mana. Insha Allahu zata samu sau'ki.


Amma me aka mata ne har haka?"


"K'awayenta ne suka zo har gida suka shaida min, wai wani malami ne ya dake ta." Na bata amsa ina mai k'ok'arin had'iyar sabon hawayen da ya fito min.


"Subhanallahi! Dama kuwa akwai irin wannan malaman, wanda basu da tausayi ko kad'an.


Banda abinshi, ina abun duka ga wannan 'yar halittar?


Idan ma dukan ne, ai sai ya san kalar wanda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login