Showing 18001 words to 21000 words out of 201092 words
Chapter 7 - AMRAH NAKE SO BOOK COMPLETE DOCUMENT .txt
zai mata.
Amma ki ga fa, har yanzu jini bai tsaya ba."
Ta hau dudduba ta.
"Ina ga kaman dole sai ku kwanta fa, ko da kwana d'aya ne ta yi sannan. Tana da bu'katar kula sosai a nan kafin ku koma gida."
Mik'o min ita ta yi, sannan ta rubuta wata allura ta bani,
"Ki karb'o wannan allurar yanzu a famasi, sai na mata ita kafin komai."
Mik'ewa na yi a hanzarce, na nufi d'akin magani da takardar.
Su kansu sun san ni, sun san cewa a kyauta muke karb'ar duk wani maganinta ko kuma allura.
Bani allurar suka yi da sauri na koma wurinta.
Bayan ta karb'a, ta had'a ta sannan ta sa na kwantar da Amrah a bisa gadon da take duba marasa lafiya.
Allurar ta mata, wanda sai a lokacin na d'an samu kwanciyar hankali, ganin yanda ta d'an zabura a lokacin da allurar ta shiga cikin fatarta.
Bayan ta gama ta jefa allurar a cikin dustbin, sannan ta dawo mazauninta.
"Ki je nurses station ki kira min duk Sister d'in da kika had'u da ita." Ta ce da ni. "Daga nan ki kira min patient na gaba."
Fitar kuwa na yi, bayan na turo mata nurse ne ta umurce ta da a kaimu d'akin irin na mutum d'aya d'in nan (amenity) sannan ta dawo ta kar'bi sauran magungunan da ta rubuta ta karb'o a pharmacy, idan ta farfad'o sai a bata su.
Ina fita na ci karo da Mallam Hafeez, ya tambaye ni halin da ake ciki na shaida masa, sannan na bi bayan nurse d'in.
Bai tsaya ba shi ma d"in binmu ya yi a baya, kwantar da ita ta yi sannan ta tafi ta bar mu a wurin ni da Mallam Hafeez.
"Alfarma guda tal nake nema a wurinka Mallam Hafeez." Na furta ina mai dubansa.
"To Maman Amrah." Ya fad'a had'e da matsowa bakin gadon.
"Dan Allah wurin k'wadagon mahaifinta zan kwatanta maka, ka taimaka ka shaida masa halin da muke ciki."
Na kwatanta masa inda Mallam yake gyaran babur a k'ark"ashin wani bayerabe.
Dubu d'ayar da Head mastet ya bashi ce ya zaro ya bani, sanann ya tafi.
Bayan tafiyar Mallam Hafeez ba da jimawa sosai ba Amrah ta tashi, hawaye duk ya bushe a kumatunta.
Da hanzari na isa gare ta, bin ta nake da kallo har sanda na k'arisa dai-dai gadon da take kwance.
Ganina da ta yi cikin yanayin damuwa da kuma tausayinta ya sa ta sakar min murmushi,
"Ummah..." ta k'o'karta fad'i annuri bai kau daga fuskarta ba.
Duk da na san cewa 'karfin hali ne irin na Amrah, a rayuwarta ko kad'an bata so ta ganmu cikin damuwa, ba wai mu iyayenta kad'ai ba, kowa ma.
A haka ni ma na sakar mata murmushin wanda iyakarsa bisa fuskaka kawai ina kallonta.
"Sannu Amrah." Na fad'a cike da tausayi.
"Yauwa...Ummah, k'ashin bayana ciwo kamar zai tsage." Ta fad'a tana k'ok'arin kai d'ayan hannun da ba a lik'a mata drip ba a bayan.
"Dama dole zai miki ciwo ai. Ki kwantar da hankalinki, zan kira Nurse yanzu zata baki kulawa sosai. Insha Allahu yanzu zai daina yi miki ciwon."
Na kama hanyar nurses station.
"Sister ta farka...ina nufin Amrah Abdallah, mai sickle cell."
Da hanzari ta tashi tsaye, wani kwando ne wanda already ta had'a medications d'in Amrah baki d"aya. Na yi gaba ta biyo ni a baya.
"Ki samo mata ruwa tukuna, wanda zata sha maganin da shi."
"To Sister." Na fad'a ha'de da nufar wajen asibitin.
Da kud'in da Mallam Hafeez ya bani na siyo mata ruwa da lemo, sai kuma biskit.
Bayan na iso, zaune na same ta, Sister kuma tana b'ab'ballo mata magnungunanta, tana d'orawa a wata container wacce suke saka magungunansu a ciki.
"Umma yanzu ya bar wurin nan..." ta fad'a cike da mamaki tana nuna k'ofa.
"Umma baki had'u da shi ba?"
Bayan na k'ariso ciki na tambaye ta,
"Wa ke nan?"
Had'e da d'ora robar ruwan sona a bisa teburin ajiye-ajiye.
"Umma, Ya Noor mana." Ta furta cike da yak'ini.
Gyad'a kai kawai na yi, dan a tunanina ko zafin ciwo ne kawai ya sa ta fad'in hakan.
"Umma wallahi da gaske nake. Sister dan Allah ba yanzu wani gurgu ya bar nan ba?"
Kai sister'n ta gyad'a alamar ehh.
"Na san ke ma kun had'u a dai-dai shigowarki sai dai ko baki ga fuskarsa ba ne.
Amma wallahi Umma shi ne nake gani. Na fad'a maku ke da Abba kun k'i yarda.
In dai wannan wanda kuka nuna min a hoto shi ne Annur, to tabbas shi ne yake kai da kawowa a cikin asibitin nan."
Kai na dafe cike da mamaki, tabbas na ha'du da wani a cikin keken guragu, sai dai kuma ban tsaya na kalli fuskarsa ba bare na tabbatar da gaske ne ko akasin haka.
Zama na yi ba tare da na sake furta komai ba, sai binta da kallo kawai da nake tana dafe da bayanta, amma hakan bai hana ta k'ok'arin tabbatar min da gaskiyarta ba.
"Maman Amrah, sai a kula sosai da magungunan nan. Sannan kuma a kula kar ta yawaita motsawa har sai sanda allurar nan ta sake ta sosai.
Ko fitsari zata yi gwara ki fita waje ki siyo mata fo, dan yawaita motsawar kanshi zai iya lalata mata treatment.
Sannan kuma sai kin yawaita tab'a jikinta, idan kika ji zazza'bin yana yawiata sauko mata sai ki kirani,
Ina jin dole za a mata awon jini dan tabbatar da ya k'one ko bai k'one ba?
Sannan a san madosa."
"To insha Allahu zan kula Sister. Na gode Allah Ya saka da alkhairi."
"Ameen maman Amrah. Allah Ya bata lafiya."
Daga nan ta fita ta bar mu.
Tana fita sai ga Mallam Hafeez a gaba, sai Mallam biye da shi, hankalinshi a tashe.
"Amrah 'yata me ya same ki?" Ya furta cike da damuwa, yana k'ok'arin isowa bakin gadon da take kwance.
"Sannu kin ji? Ashe ciwo ya tashi, Allah Ya kyauta ya tsare gaba."
"Ameen Ya Allahu." Mallam Hafeez ya furta.
Sai a lokacin ma na tuna da ba a mata treatment na raunin da aka mata wurin bulala ba.
Da hanzari na ce,
"Mallam ina zuwa." Na nufi wurin Sister.
Bayan na fad'a mata dalilin zuwana ta ce,
"Ehh ina sane da shi ai, small injury ne ba abun a damu sosai ba.
Gwara a bar mata shi a bud'e ya sha iska,
Dan kar a je a tab'a k'ila k'ashin wurin bashi da wani k'wari sosai. Wurin gyaran gira a rasa ido."
Na gamsu da maganarta sosai, hakan ya sa kawai na mata godiya had'e da tafiya.
_Yawan zazzab'i mai zafi wanda baya sauka, yana d'aya daga cikin alamomin sickler. Lura da kyau, mu zama masu kula da ciwukan da yaranmu ke yi, kar mu zama masu sake, har ciwo ya fara yi masu yawa. Allah Ya bada lafiya._
Pinky durling💗
*RAZ 2👌🏻*
[8/30, 3:33 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥
(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)
Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_
1⃣3⃣
Washe gari da sassafe sai ga Malaman makarantarsu sun zo, su kusan ashirin ko ma fin haka. Har d'akin ma bai iya d'auke yawansu ba.
A lokacin da suka zo Mallam baya nan, ya zo ya kawo mana abinci, ya wuce wurin aikinsa.
Har k'asa na du'ka muka gaisa, sannan na d'an bubbuga Amrah ta tashi.
Head master'nsu ne ya 'kariso dai-dai inda take,
"Sannu Amratu. Ya k'arfin jikin naki?"
Da fara'a k'unshe a fuskarta ta ce,
"Jiki da sau'ki sosai Mallam. Na gode."
Da haka malaman sukaita mata ya jiki, a k'arshe Mallam Mu'ammar cike da kunya ya dafe k'eyarsa, ya ce,
"Insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba. A yi hak'uri." Ya juyo gare ni, "Ban tsammanin abun zai kai har haka ba, da tun farko ban dake ta ba.
Insha Allahu ba zan kuma maimaitawa ba. Zan zama mutum mai tausayi, ba wai gare ta kawai ba, ga baki d'aya d'alibaina."
Ya juya ga sauran Malaman ya ce,
"Dan Allah ina mai neman afuwarku, daga yanzu duk wani d'alibi wanda za a kawo mai sickler, mu ringa kula da shi, mu san ta hanyar da zamu masa hukunci.
Sai mun kula sosai, mun basu kulawa tamkar 'ya'yanmu ko kuma k'annenmu na jini.
Ita rayuwar nan baka san wanda zai maka rana ba, sanann kuma kana naka Allah Na naSa."
Head master ya yi gyaran murya ya ce,
"Haka ne Mallam Mu'ammar. Na ji da'di k'warai da ka gane hakan, har kake bada taka shawarar.
Allah Ya tsayar nan, ita kuma Allah Ya bata lafiya."
"Ameen." Duka Malaman suka fad'a a tare.
Ku'di Head master ya zaro daga aljihunsa ya d'ora bisa gadon Amrah,
"Ga wannan a sai miki lemo. Allah Ya sauwak'a ko?"
Godiya na masa sannan suka fita, suka bar d'akin baki d'ayansu.
Bayan sun tafi na duba kud'in, dubu goma ne cif, hakan ba kad'an d'in dad'i ya min ba, saboda dama babu kud'in, abincin da Mallam ya siyo mana da safe ma da k'yar ya had'a ku'din ya siyo.
Kwananmu biyu aka bata sallama muka koma gida, ranar da muka koma sai ga Hajiya Suhaila ta zo, wai Annur ne ya fad'a mata Amrarsa bata jin da'di, da yake ya kira ta wayar Amrah'n Mallam ya d'auka yake shaida masa bata da lafiya, kuma baya asibiti a lokacin bare su yi waya.
Ta kawo ma Amrah sha tara ta arzik'i, a 'karshe ta mana fatan alkhairi sanann ta tafi.
Da yamma Mallam ya kira ma Amrah Annur. Sun jima suna waya, har take masa ta'din ganinsan da take yawan yi a Turai Hospital, amma ya shaida mata cewa ba shi ba ne, saboda shi tun da ya bar Nigeria bai sake dawowa ba. Wata k'ila dai mai kama da shi ne kawai take gani.
Rayuwa ta ci gaba da tafiya a haka, yau da lafiya gobe babu lafiya, a haka dai take rayuwarta cike da wahala.
Talauci kuma sosai muka rage shi, saboda babu abin da Hajiya Suhaila bata bamu, tun daga kan kayan abinci har sutura yi mana take, Amrah ma kuma ba laifi tana zuwa gidanta, abin dai sai sam barka.
A lokacin da Amrah ta yi JSS ne, take da shekara goma sha uku da watanni.
Ranar da suka gama zana jarabawarsu, Annur yake mata albishir da cewa mahaifinsa ya barshi ya dawo Nigeria ya ci gaba da aikinsa, saboda ya da'de da zama Architecture babba, wanda yake da degree mataki na uku (ph. D) duk a 'bangaren zane-zane.
Sosai Amrah ta yi murna, dan zan iya cewa ko Hajiya Suhaila da ta haife sa, bata kai Amrah jin dad'i ba.
Ranar da suka yi waya cewa zai dawo gobe, kasa bacci Amrah ta yi, sai faman juye-juye take, ta ma rasa me ya kamata ta yi saboda murna.
Washe gari da sassafe ta fito tsakar gida ta hau shara, jin motsinta ya sa na fito a hanzarce na ce,
"Ya da shara tun da duku-dukun safiya, ba zaki yi shirin makaranta ba?"
Fuska a yamutse ta ce,
"Umma yau fa ba zan je ba. Kin manta Hammana zai dawo?"
Murmushi na yi na ce,
"Ya za a yi na manta da dawowar Annur? Ai ban ga zaman me zaki yi ba idan baki je ba? Ga ki kuma ke ce shugabar aji."
"Umma ai jiya Momy ta kira ni, wai yau da safe na je can mu yi shirye shiryen tarbarsa. Shi ya sa ma na tashi da wuri dan na kammala komai cikin lokaci."
"To ai shi ke nan. Amma ba kya gudun abin da Islam zata miki? Kin san fa ita ma yau tana iya k'in zuwa aiki saboda shi."
Tab'e baki Amrah ta yi ta ce,
"Duk abin da ta min ai sai in bata ha'kuri. Cike nake da murna yau bana jin masifarta da wulak'ancinta zasu yi tasiri a gare ni, har su hana ni tarbar Ya Noor."
Ajiyar zuciya na sauke,
"To ai shi ke nan. Amma sai kin daure, kin kai zuciyarki nesa."
"Insha Allahu kuwa Ummah. Ai kin san ni da wuya mutum ya b'ata min rai. Ina binsa da yanda yake so, sai dai ma a k'arshe shi d'in zai ji kunya."
"Na tabbatar da hakan kuwa 'yata.
Allah Ya miki albarka ya sa ki d'ore da wannan kyawawan halayen naki.
Wai har yanzu ba a saka ranar walimar saukar taku ba?"
"Basu saka ba Umma. Amma dai na san very soon za a yi ta. Shi ya sa ma suka ce kowa ya zama cikin shiri.
Har ma na gama tsara ma d'alibaina diramar (darama) da zasu yi ta larabci."
Murmushi na yi na ce,
"Ke d'in nan ce da d'alibai? Lallai ma."
"Umma kar dai ki ce baki san cewa ina da d'alibai ba? Tun bayan da muka yi sauka da tilawa aka raba mana azuzuwa.
Sauran "yan ajinmu ma aka fitar masu da aji...?"
"To bare kuma ke da kike Amira (Head girl)." Na k'arisa mata had'e da murmusawa.
"Ni dai ban fad'a ba Umma." Ta furta tana murmushi.
"Ai na san can kika dosa."
Ci gaba da sharar ta yi har sanda ta gama.
Zata yi wanke wanke na dakatar da ita,
"Je ki shirya kawai ki bar min wannna zan yi. Dan na ga a matse kike sosai."
"A'a Umma. Wallahi ki bari zan yi kawai. Wanke-wanken duka nawa yake?"
Ta ci gaba da ha'da ruwan kumfa.
"Sanin bashi da yawan ne ai ya sa na ce miki ki bari na yi. Kullum fa ke ke yi, yau rana d"aya dan baki yi ba ai ba damuwa."
Da 'kyar na samu ta bar wanke wanken na ci gaba. Ita kuwa ta nufi wanka.
K'arfe goma saura wayarta ta hau ruri, ganin Momy rubuce ya sa ta hanzarta d'auka,
"Assalamu alaikum." Ta furta had"e da matse wayar da wuyanta, tana shafa kwalli.
"Ehh Momy saura k'iris na gama. Gani nan zuwa yanzu insha Allahu."
Ta d'an yi shiru daga nan,
"Da azahar? Ahh lallai to bara na hanzarta. Ashe ma isowar wuri zasu yi."
Ta tsinke wayar had'e da mik'ewa.
"Umma bara na tafi. Da azahar wai jirginsu zai sauka.
So nake Ya Noor ya fara cin girkina idan ya iso. Ni da kaina zan masa abin da yake so. Dama ya min text na favorite d'insa (abincin da ya fi so)"
"To shi ke nan Amrah. Allah Ya miki albarka ya sa a fita lafiya a dawo lafiya."
"Amin, Ummana." Ta furta had'e da fita tana murmushi.
Ko da ta isa ta samu Hajiya Suhaila sai ujila take, bata can bata can ana ta aikin tarbar bak'i.
Ashe wai har da Nadrah babbar yayarsu da yake gidanta zasu zo. Saddiqa ma tana kan hanya ita da yaranta, Islam kuma tana da theatre k'arfe sha biyu, hakan ya sa ta shirya ta bar gidan da wuri.
Haka sukaita aiki har sha biyu da rabi sannan Hajiya Suhaila ta ce ta bar sauran aikin ga mai aikinta Safina, zasu tafi Airpot ne dan ta san suna daf da isowa.
Wani wankan ta sake yi, sannan ta saka wata doguwar rigarta kalar baby pink, wadda aka k'awata da adon duwatsu hot pink.
Gyalen rigar ta yafe wanda shi ma kalarsa hot pink ce. Asalin rigar ma Hajiya Suhaila ce ta siyo mata ita daga Umra da ta je.
'Karfe d'aya da rabi ta masu a Airpot d'in Umaru musa Yaradua. Suna isa suka tarar da Saddiqa da yaranta uku sun isa, saboda dama a can suka yanke sahawarar had'uwa kawai.
A yanda Amrah ke bani labari; sun yi zama kamar na kusan mintina arba'in kafin k'arar jirgi ta dake dodon kunnuwansu.
Har da hawayen murna ta yi, a dai-dai lokacin da jirgin ya sauko k'asa.
Babban farin cikinta, shi ne yau zata ga farin cikin rayuwarta. Zata ga mutum ma fi soyuwa a zuciyarta, wanda ta ta'allak'a rayuwarta da shi. Bata san shi ba, bata tab'a ganinshi ba, tun bayan sanda ta yi wayo, amma a zuciyarta tamkar sun saba ne, wata irin shak'uwa take jin sun yi, a tsawon lokutan da suka d'auka suna waya.
"Mommy sun fara fitowa."
Muryar Saddiqa ce ta dawo da Amrah daga birnin tunanin da ta lula.
Murmushin yak'e ta yi, ganin ta kalli Saddiqa amma ta wurga mata wani matsiyacin kallo.
Bin bayansu ta yi, zuciyarta cike da tunane tunane, na yanda zata ga Hammanta Noor.
Amrah ba yarinya ba ce mai hanzari, komai nata cikin sanyi take yinsa, hakan ya sa suka mata nisa.
Da sauri Salmah ta dawo ta kama mata hannu,
"Aunty ki yi sauri mana. Kin ga har an miki nisa."
Murmushi ta k'irk'iro ha'de da 'kara saurin tafiyarta.
A lokacin da suka isa iyaka, wato daga inda ba za a barsu wucewa ba, har sai sanda matafiyan suka fito da kansu. Dakatawa suka yi, Salmah na k'ok'arin jan Amrah da hira, amma Mamanta Saddiqa ta daka mata tsawa, wanda dolenta ta yi shiru.
Tun daga nesa ta hangoshi, bayanshi goye da bak'ar jika, sai kuma wani babban trolly da ya jawo da hannunsa.
Biye da shi Nadrah ce, sai yaranta twins 'yan mata, wanda a girme sun girmi Amrah.
Kallonsa take tun daga nesa, bata gama gasgata tunaninta ba har sai sanda ya k'ariso inda suke. Fuskarsa yalwace take da annuri, idonshi k'yam a kanta.
"Shi ne..." ta furta a razane, tana nuna shi da yatsa.
"Ko shekaranjiya ba na ganka ba a asibiti? Yaushe ka warke? Yaushe ka daina hawan keken guragu?"
Har a lokacin bata ajje hannunta daga nuna san da take ba.
_Daga lokacin da yaro mai sickler ya haura ma shekara uku, za a iya ganin idanuwansa suna canzawa, suna rikid'ewa daga ainahin yanda suke. Wasu kuma hak'oransu jajaye ne. Duk iya k'ok'arin na brushing d'in da ake masu, ba zasu tab'a zama farare ba. Wannan duk cikin alamomin sickler ne. Da zarar kuka ga haka, hanzarta kai yaronku asibiti domin a masa awon genotype. Allah Ya kare mu da ahalinmu baki d'aya._
Pinky durling💗
*RAZ 2👌🏻*
[8/30, 3:34 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥
(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.)
Na Amrah A Msh
_(Princess Amrah)_
*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
_Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_
1⃣4⃣
_Sakon gaisuwa bad'e da jinjina ga *ANEESA ABUBAKAR RIMI (ANEELURV)* You are indeed a nice person to me, and to everyone. May Allah continue to bless you. Allah Ya barki da Oga._
***
Ba wai Annur kad'ai ba, ita kanta Hajia Suhaila sai da ta yi